Sashe 15
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Take ta ji tamkar ta mutu, zuciyarta ta daure,'kirjin ta yayi nauyi ainun, tafiya kawai take amma bata sanin inda take jefa 'kafarta.
Suna tsaye a bakin gate din makarantar suna jiran abin hawa ta ga yazo ya wuce su akan mashin 'dinsa da a wancan lokacin ake mishi la'kabi da tsuntsun soyayya.
Hannu ya daga musu amma sai ta juyar da fuskar ta, tayi kamar bata ganshi ba, Zainab ce kawai tayi waving 'din shi.
Tana isa gida 'dakin ta, ta wuce ta fa'da kan katifarta wani kuka ya kwace mata, tayi abinta ta 'koshi kasan cewar Innar ta na wanka, daga kukan barci yayi gaba da ita, sanin da mahaifiyar ta yi na fashin salla take yasa bata tashe ta ba.
Haka ta yi hutun nan su ku ku, ciwon so na wahalar da ita, a tunaninta tasan so akan khalil, Ashe ba son sa take ba, kawai shakuwa ne da kuma yadda yake mata hidima, a yanzu ne take dandana azabar soyayya, yanzu ne take jin so tun daga zuciyarta, idanuwanta, da gangar jikinta gaba'daya.
Idan ta tuna Farida yake so, sai taji tamkar za ta sume.
A yadda ta ji ciwon ganinsa da Farida a tsaye yana mata magana cikin walwala komi yana iya faruwa da ita idan ya kasance kullum zata na ganinsa tare da ita.
Zaune ta ke tana fargaban komawar ta makaranta wani satin, a da ta dauka zullimin zuwa makaranta ya 'kare tunda yanzu ta tsira daga tozarcin Uncle Mk! ashe tsugunne bata 'kare mata ba?.
Agogon bango ta kalla taga 2:30pm da sauri ta 'mike ta shiga wanka ta fito ta shirya cikin lallausar atamfar quali-wax mai kalar samaniya(Skye blue)da ratsin ja, Riga da skirt ne, dinkin yayi matuqar zama a jikinta,'katon jan 'dan kunne mai round tasa, a lokacin yayin kwalliya irin ta wannan zamanin ba tazo ba, amma duk da hakan ta she'kawa fuskar ta kwallliyar da ta dace da ita.
Mayafi jah ta ya fa, sumfurin(internet). ta sanya takalmi half-cover amma hills. da yar mitsitsiyar jakarsa wadda zuwanta jos ta siyo su masu Jan duhu. ta fesa turare ta fita zuwa 'dakin Inna.
Inna na shirya, mi'ke wa tayi daga kishingidar da ta yi, hannun ta ri'ke da carbi tunda ta idar da sallar azahar bata tashi ba.
"Yanzu Iyah ba za ki daina zabga turaren nan idan zaki fita ba?
Ba kyau fa, ki kiyayi taba shari'a wallahi"
A hankali tace
"Allah Inna 'dan ka'dan ne, kawai 'kamshi ne dashi".
"To tunda kin san yadda yake dole ne, idan zaki fita sai kin saka?
Ki fa dinga jin tsoron ubangijin ki, kina kiyaaye ka'idojin shari'a".
Kafin tayi magana, ta sake cewa
"A gabana kika ce da Baffan ku, bayan la'asar za ku dawo, ki sani idan kika wuce wannan lokacin ba zan 'ki fada mishi ba"
"In sha Allah bazan kai maghrib ba Innah"
"Sannan kuma kiji tsoron Allah idan mu bama kallon ki, shi yana kallon ki.
inda kika tambaya nan kawai aka lamince miki zuwa.
Sai kin martaba kanki, kafin wani ya martaba ki, sannan kuma
duk saurayin da ya tsayar da ke kice mishi yazo gidan ku, ya nemi izinin magana dake a wurin mahaifin ki."
A sanyaya ta amsa da
"Zan kiyaye Inna"
Sannan ta juya ta tafi, tana rayawa ko sai yaushe Inna za ta dena mata bitar wannan nasihar a duk sadda zata fita?
Jikin ta yayi sanyi, nasihar ta matu'kar ratsata.
take ta ji ta fasa zuwa inda ta yi niyya, tunda gidan su Halima zata je su hadu da Khalil dake duk kusan unguwar su daya.
Tunda akayi hutu basu hadu ba, a dalilin fushin da yake yi da ita, yana zargin soyayya suke ita da Uncle Mukhtar.
Baisan gidan su ba, kullum cewa take ba a barinta yin zance, sannan indai aka ganshi yaje gun ta za ta Sami matsala babba, nan kuwa gani ta ke da kunya yazo ya ga gidansu.
Nasihar Inna tasa ta canja shawara gara kawai yau ta kaiwa Zainab Ma'aji ziyara ta huta da gorin da ta ke mata na ba ta zuwa gidansu, tunda dama nan ta cewa iyayen ta za ta.
Tana fita yar tafiya tayi 'kadan, tana jiran ta tsallaka, kamar ance 'daga kanki kawai sai idanuwan ta ya fada cikin na shi yana fitowa daga wani shagon aski da ke gaban gidansu kadan.
Mamaki ne ya kamashi ya tsallako ya same ta, tuna nasihar da ya musu na nuna ladabi yasa ta risina tare da fadin
"Barka da rana"
Maimakon ya amsa da hausa sai ya juya harshe, yace
"Sa'adah how are you"? how ur parents and everything?"
A hankali tace"very fine"
Ya sake fadin "are you living here?"
Kai kawai ta 'daga tare da nuna mishi gidansu "this is our house"
bata san mai yasa shi bata ji, kunyar nuna masa gidan nasu ba, kamar yadda ta ke jin kunyar su Halima da Khalil su ga gidan. duk kuwa da bashi da makusa tunda ginin bulon siminti ne, a shafe yake da filasta, 'kyauren 'kofar shiga lafiyeyye ne mai aminci, sabanin gidajen su 'kawayen nata manyan gates ne dasu, masu zubin mahadi ka ture mussaman gidan su Safina da Humaira Suraj, nasu Halima ne dai ba wani shararren gida bane amma darajar unguwar ma kadai ta kerewa tasu unguwar.
Yayi murmushi tare da fadin "wonderful I know ur father since"
Da mamaki ta kalle shi tace 'Realy"?
"Sosai kuwa for over 5 years, is he around?"
"No yaje Gogel 'dazu"
"Said it in English"
Ta tura baki alamun ya fara son 'kureta wadda shikuma hakan da tayi drives him crazy.
Tace, "He went to our Home town" ta tsuke bakinta ta yi shiru in ma bata yi dai dai ba 'karshen dagewar ta kenan.
Murmushi yayi ya sake cewa "oh rude Sa'adah!"
Har cikin ranta take jin dadin yadda ya yanke sunan yake fadin Sa'adah!
Bashine farkon fa'da mata hakan ba, amma shine farkon wadda ya iya fadin sunan, shinea farkon wadda yasa mata son sunan.
Ba zato ta ji yace "where's is ur loverboy"?
Kunyar duniya ta kamata ta yi 'kasa da kai tana jin kamar 'kasa ta tsage ta shige,
Ganin yadda ya kunyata ta, yasa shi tambayar inda zata,
Kai tsaye tace
"Gidan su Zainab Ma'aji".
Sai ya mata sallama, ya tsallaka ya hau mashin dinsa.
ganin haka yasa ta wuce ta nufi gidan su Zainab.
Cike da shauki ta isa gidan su Zainab din, a dakin dake mallakin tane da yayarta Asiya suka zauna, suna hira, tare da Anty Asiya gaba'daya, cike da farinciki take basu labarin haduwarsu da Uncle Mk yanzun nan.
Asiya ta ri'ke baki tana kallon yadda Sa'adatu ke bada labarin shi cike da 'doki da farin ciki, kasa 'boye mamakinta ta tayi, tace
"Sa'adatu da wuri haka?"
Cike da rashin fahimta tace
Kamar "Yaya da wuri haka, ban fahimce ki ba?"
Cike da iya shege Asiya tace "Ato na ga a duniya kin washi ayi maganar bawan Allah nan, abin mamakin kuma sai gashi yau da kanki kina hirar shi cike da shauki da jin dadi, shine nace da wuri haka har 'kiyayyar ta 'kare?"
Kunya ta kamata sai cewa tayi "Ni fa ba gun ki nazo ba, kuma bada ke nake zance na ba".
Dariya suka sa mata daga Zainab har yayar tata, take kuwa takaicin su ya kamata sai kawai ta fashe musu da kuka.
Nan da nan kuma jikin su yayi sanyi, suka gintse dariyar, suka hau bata ha'kuri, barin ma Asiya da ta ke ta fadin "daga wasa, nifa tsokanar ki nake, to yi ha'kuri ba zan sake ba"
da ga haka ta mi'ke ta bar musu dakin cike da mamakin shagwaba irin ta Sa'adah.
Da 'kyar Zainab ta shawo kanta ta huce, ta shiga bata labarin tunda akayi hutu basu hadu da Khalil ba, saboda yana fushi da ita akan Mk.
Tabe baki Zainab ta yi tana fadin jimin yaro da 'karfin hali, to shi da nufin sa baza ki kula wani ba? bama shi da hankali.
Sanin da Sa'a ta yi Zainab ba ta yin Khalil, ya sata tsuke bakin ta, har sai da ta gama caccakar shi ta 'kosa dan kanta, ta bar maganar.
Wai a Ina kika ga Uncle Mk din? Zainab ta tambaya cike da son jin 'karshen maganar da Asiya ta so watsawa.
Bata rai ta yi tace inace dariya ku ke min?"
"Ni ba ke na yiwa dariya ba, Yaya Asiya ce ta bani dariya da ta shiga zancen da ba na ta ba".
Numfasawa ta yi tace
"A 'kofar gidan mu ya fito a wannan shagon na The Boss barbing shop".
Amma dai kin gaishe shi, Zainab ta tambaya da sauri.
"Ah sosai ma har hira mun yi"
Murmushi Zainab tayi tare da fadin
"In sha Allah wannan ne mafarin hirar taku, ba 'karshe ba"
Da sauri Sa'adah ta dube ta, tace
"saboda me kika ce haka?"
Kai tsaye ta bata amsa da cewa "saboda kuna son junan ku"
Sunkuyar da kai Sa'adah ta yi tana mamakin yadda ta hasko tana son Mk, sanin Zainab akwai ta da sa ido sai ba tayi mamakin gano ta da ta yi ba.
Kamar zata yi shiru sai ta kasa tace
"Zainab shi ba ya sona, Farida ya ke so", ta fada cikin muryar kuka.
Hannunta Zainab ta ru'ko cikin lallashi tace
"Wallahi yana son ki, ke duk wannan takurar daya miki a banza ce? kin ta'ba tunanin mai yasa ke kadai ya damu ki maida hankali a kan karatun ki?
Ni na dade da gane yana sonki amma irin mutanan ne masu kiyaye doka da oda. kinga ai bai dace ya nuna miki soyayya alhalin aikata hakan laifi ne babba da hukumar makaranta ba za ta amince da shi ba,
Sannan Farida 'daliba ce mai haza'ka irin su farin jini ne da su a gun dukkan malami ba wai Uncle Mk ba kawai. gaskiya ba sonta ya ke, so irin na soyayyar saurayi da budurwa ba, illa 'kaunar da malami yake yiwa dalibarsa mai ladabi da haza'ka".
Suna tsaye a bakin gate din makarantar suna jiran abin hawa ta ga yazo ya wuce su akan mashin 'dinsa da a wancan lokacin ake mishi la'kabi da tsuntsun soyayya.
Hannu ya daga musu amma sai ta juyar da fuskar ta, tayi kamar bata ganshi ba, Zainab ce kawai tayi waving 'din shi.
Tana isa gida 'dakin ta, ta wuce ta fa'da kan katifarta wani kuka ya kwace mata, tayi abinta ta 'koshi kasan cewar Innar ta na wanka, daga kukan barci yayi gaba da ita, sanin da mahaifiyar ta yi na fashin salla take yasa bata tashe ta ba.
Haka ta yi hutun nan su ku ku, ciwon so na wahalar da ita, a tunaninta tasan so akan khalil, Ashe ba son sa take ba, kawai shakuwa ne da kuma yadda yake mata hidima, a yanzu ne take dandana azabar soyayya, yanzu ne take jin so tun daga zuciyarta, idanuwanta, da gangar jikinta gaba'daya.
Idan ta tuna Farida yake so, sai taji tamkar za ta sume.
A yadda ta ji ciwon ganinsa da Farida a tsaye yana mata magana cikin walwala komi yana iya faruwa da ita idan ya kasance kullum zata na ganinsa tare da ita.
Zaune ta ke tana fargaban komawar ta makaranta wani satin, a da ta dauka zullimin zuwa makaranta ya 'kare tunda yanzu ta tsira daga tozarcin Uncle Mk! ashe tsugunne bata 'kare mata ba?.
Agogon bango ta kalla taga 2:30pm da sauri ta 'mike ta shiga wanka ta fito ta shirya cikin lallausar atamfar quali-wax mai kalar samaniya(Skye blue)da ratsin ja, Riga da skirt ne, dinkin yayi matuqar zama a jikinta,'katon jan 'dan kunne mai round tasa, a lokacin yayin kwalliya irin ta wannan zamanin ba tazo ba, amma duk da hakan ta she'kawa fuskar ta kwallliyar da ta dace da ita.
Mayafi jah ta ya fa, sumfurin(internet). ta sanya takalmi half-cover amma hills. da yar mitsitsiyar jakarsa wadda zuwanta jos ta siyo su masu Jan duhu. ta fesa turare ta fita zuwa 'dakin Inna.
Inna na shirya, mi'ke wa tayi daga kishingidar da ta yi, hannun ta ri'ke da carbi tunda ta idar da sallar azahar bata tashi ba.
"Yanzu Iyah ba za ki daina zabga turaren nan idan zaki fita ba?
Ba kyau fa, ki kiyayi taba shari'a wallahi"
A hankali tace
"Allah Inna 'dan ka'dan ne, kawai 'kamshi ne dashi".
"To tunda kin san yadda yake dole ne, idan zaki fita sai kin saka?
Ki fa dinga jin tsoron ubangijin ki, kina kiyaaye ka'idojin shari'a".
Kafin tayi magana, ta sake cewa
"A gabana kika ce da Baffan ku, bayan la'asar za ku dawo, ki sani idan kika wuce wannan lokacin ba zan 'ki fada mishi ba"
"In sha Allah bazan kai maghrib ba Innah"
"Sannan kuma kiji tsoron Allah idan mu bama kallon ki, shi yana kallon ki.
inda kika tambaya nan kawai aka lamince miki zuwa.
Sai kin martaba kanki, kafin wani ya martaba ki, sannan kuma
duk saurayin da ya tsayar da ke kice mishi yazo gidan ku, ya nemi izinin magana dake a wurin mahaifin ki."
A sanyaya ta amsa da
"Zan kiyaye Inna"
Sannan ta juya ta tafi, tana rayawa ko sai yaushe Inna za ta dena mata bitar wannan nasihar a duk sadda zata fita?
Jikin ta yayi sanyi, nasihar ta matu'kar ratsata.
take ta ji ta fasa zuwa inda ta yi niyya, tunda gidan su Halima zata je su hadu da Khalil dake duk kusan unguwar su daya.
Tunda akayi hutu basu hadu ba, a dalilin fushin da yake yi da ita, yana zargin soyayya suke ita da Uncle Mukhtar.
Baisan gidan su ba, kullum cewa take ba a barinta yin zance, sannan indai aka ganshi yaje gun ta za ta Sami matsala babba, nan kuwa gani ta ke da kunya yazo ya ga gidansu.
Nasihar Inna tasa ta canja shawara gara kawai yau ta kaiwa Zainab Ma'aji ziyara ta huta da gorin da ta ke mata na ba ta zuwa gidansu, tunda dama nan ta cewa iyayen ta za ta.
Tana fita yar tafiya tayi 'kadan, tana jiran ta tsallaka, kamar ance 'daga kanki kawai sai idanuwan ta ya fada cikin na shi yana fitowa daga wani shagon aski da ke gaban gidansu kadan.
Mamaki ne ya kamashi ya tsallako ya same ta, tuna nasihar da ya musu na nuna ladabi yasa ta risina tare da fadin
"Barka da rana"
Maimakon ya amsa da hausa sai ya juya harshe, yace
"Sa'adah how are you"? how ur parents and everything?"
A hankali tace"very fine"
Ya sake fadin "are you living here?"
Kai kawai ta 'daga tare da nuna mishi gidansu "this is our house"
bata san mai yasa shi bata ji, kunyar nuna masa gidan nasu ba, kamar yadda ta ke jin kunyar su Halima da Khalil su ga gidan. duk kuwa da bashi da makusa tunda ginin bulon siminti ne, a shafe yake da filasta, 'kyauren 'kofar shiga lafiyeyye ne mai aminci, sabanin gidajen su 'kawayen nata manyan gates ne dasu, masu zubin mahadi ka ture mussaman gidan su Safina da Humaira Suraj, nasu Halima ne dai ba wani shararren gida bane amma darajar unguwar ma kadai ta kerewa tasu unguwar.
Yayi murmushi tare da fadin "wonderful I know ur father since"
Da mamaki ta kalle shi tace 'Realy"?
"Sosai kuwa for over 5 years, is he around?"
"No yaje Gogel 'dazu"
"Said it in English"
Ta tura baki alamun ya fara son 'kureta wadda shikuma hakan da tayi drives him crazy.
Tace, "He went to our Home town" ta tsuke bakinta ta yi shiru in ma bata yi dai dai ba 'karshen dagewar ta kenan.
Murmushi yayi ya sake cewa "oh rude Sa'adah!"
Har cikin ranta take jin dadin yadda ya yanke sunan yake fadin Sa'adah!
Bashine farkon fa'da mata hakan ba, amma shine farkon wadda ya iya fadin sunan, shinea farkon wadda yasa mata son sunan.
Ba zato ta ji yace "where's is ur loverboy"?
Kunyar duniya ta kamata ta yi 'kasa da kai tana jin kamar 'kasa ta tsage ta shige,
Ganin yadda ya kunyata ta, yasa shi tambayar inda zata,
Kai tsaye tace
"Gidan su Zainab Ma'aji".
Sai ya mata sallama, ya tsallaka ya hau mashin dinsa.
ganin haka yasa ta wuce ta nufi gidan su Zainab.
Cike da shauki ta isa gidan su Zainab din, a dakin dake mallakin tane da yayarta Asiya suka zauna, suna hira, tare da Anty Asiya gaba'daya, cike da farinciki take basu labarin haduwarsu da Uncle Mk yanzun nan.
Asiya ta ri'ke baki tana kallon yadda Sa'adatu ke bada labarin shi cike da 'doki da farin ciki, kasa 'boye mamakinta ta tayi, tace
"Sa'adatu da wuri haka?"
Cike da rashin fahimta tace
Kamar "Yaya da wuri haka, ban fahimce ki ba?"
Cike da iya shege Asiya tace "Ato na ga a duniya kin washi ayi maganar bawan Allah nan, abin mamakin kuma sai gashi yau da kanki kina hirar shi cike da shauki da jin dadi, shine nace da wuri haka har 'kiyayyar ta 'kare?"
Kunya ta kamata sai cewa tayi "Ni fa ba gun ki nazo ba, kuma bada ke nake zance na ba".
Dariya suka sa mata daga Zainab har yayar tata, take kuwa takaicin su ya kamata sai kawai ta fashe musu da kuka.
Nan da nan kuma jikin su yayi sanyi, suka gintse dariyar, suka hau bata ha'kuri, barin ma Asiya da ta ke ta fadin "daga wasa, nifa tsokanar ki nake, to yi ha'kuri ba zan sake ba"
da ga haka ta mi'ke ta bar musu dakin cike da mamakin shagwaba irin ta Sa'adah.
Da 'kyar Zainab ta shawo kanta ta huce, ta shiga bata labarin tunda akayi hutu basu hadu da Khalil ba, saboda yana fushi da ita akan Mk.
Tabe baki Zainab ta yi tana fadin jimin yaro da 'karfin hali, to shi da nufin sa baza ki kula wani ba? bama shi da hankali.
Sanin da Sa'a ta yi Zainab ba ta yin Khalil, ya sata tsuke bakin ta, har sai da ta gama caccakar shi ta 'kosa dan kanta, ta bar maganar.
Wai a Ina kika ga Uncle Mk din? Zainab ta tambaya cike da son jin 'karshen maganar da Asiya ta so watsawa.
Bata rai ta yi tace inace dariya ku ke min?"
"Ni ba ke na yiwa dariya ba, Yaya Asiya ce ta bani dariya da ta shiga zancen da ba na ta ba".
Numfasawa ta yi tace
"A 'kofar gidan mu ya fito a wannan shagon na The Boss barbing shop".
Amma dai kin gaishe shi, Zainab ta tambaya da sauri.
"Ah sosai ma har hira mun yi"
Murmushi Zainab tayi tare da fadin
"In sha Allah wannan ne mafarin hirar taku, ba 'karshe ba"
Da sauri Sa'adah ta dube ta, tace
"saboda me kika ce haka?"
Kai tsaye ta bata amsa da cewa "saboda kuna son junan ku"
Sunkuyar da kai Sa'adah ta yi tana mamakin yadda ta hasko tana son Mk, sanin Zainab akwai ta da sa ido sai ba tayi mamakin gano ta da ta yi ba.
Kamar zata yi shiru sai ta kasa tace
"Zainab shi ba ya sona, Farida ya ke so", ta fada cikin muryar kuka.
Hannunta Zainab ta ru'ko cikin lallashi tace
"Wallahi yana son ki, ke duk wannan takurar daya miki a banza ce? kin ta'ba tunanin mai yasa ke kadai ya damu ki maida hankali a kan karatun ki?
Ni na dade da gane yana sonki amma irin mutanan ne masu kiyaye doka da oda. kinga ai bai dace ya nuna miki soyayya alhalin aikata hakan laifi ne babba da hukumar makaranta ba za ta amince da shi ba,
Sannan Farida 'daliba ce mai haza'ka irin su farin jini ne da su a gun dukkan malami ba wai Uncle Mk ba kawai. gaskiya ba sonta ya ke, so irin na soyayyar saurayi da budurwa ba, illa 'kaunar da malami yake yiwa dalibarsa mai ladabi da haza'ka".