Sashe 61
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta fa'da hawaye yana zubo mata. take ya ji sonta ya dawo daga suman da ya yi, Ashe son ba raguwa ya yi ba, comma ya shiga.
Ya bude mata dukkan hannuwansa biyu, a yau bata tsaya jan aji ba, da sauri ta fada masa, yasa dukkan hannuwansa ya rungumeta tsantsan ita kuma tana kuka kasa kasa.
Baice komai ba, illah shafar bayanta yana jin sau'kin 'daurin da kirjinsa ya yi akanta.
Tun daga ranar ya canja, ya daina 'daure fuska, sannan ya bu'de mata kofar nisha'di a tsakanin su, sab'anin satikan da suka shude da ya rufe ta rif.
Saukowar Mk ya sa ta fara murmurewa, tashin hankalin da ta shiga yasa ta manta da wayar ta Bb, sai yanzu da ta sami nutsuwa take fitowa da ita, idan ya fita.
* Tsautsayi*
Ranar da ta zama 'bakar Rana ga rayuwar ma'auratan guda biyu, wadda tarihin rayuwar su ba zai cika ba, sai an sako ranar.
Asabar ce cikin watan Augusta da safe bayan sun kammala karyawa cikin walwala, ya shirya ya mata sallama, zai je ta'aziya Baban Abokinsu ya rasu daga nan zai zarce gidan su ba zai dawo ba sai yamma, ta masa addu'ar dawowa lafiya,ya tafi tare da Jawad. Kafin ya fita ta nemi iznin za ta je kitso, bai hana ba, ya amince mata.
Sai da ta gama komai na gyaran gida, ta yi wanka, ta tsaya jikin wardrobe tana nazarin rigar da zata sanya.
Wata daguwar riga ta janyo data jima bata sa ta ba, garin janyowar ta hado da ledar kayan da su Halima suka kawo mata na tsarabar khalil, wadda ta manta da su, ta leka ta ga rigunan Jawad ne da agogon ta, sai kwalin wayar Blackberry, ta jefa kan gado akan sai ta dawo zata san yadda zata yi ta nunawa Mk rigunan, dan ta fara sakawa Jawad tunda tsadaddu ne.
Ta dauko wayar daga inda take boyewa, ta jona a caji, ta shirya ta rufe gidan ta fita, zuwa bayan layinsu inda take kitson.
Mk da ya fito daga gidan rasuwar gidan Mahmoud suka zarce adalilin motar Mahmoud din ta lalace, dan haka ya kai shi, ai kuwa Jawad ya ce anan zai zauna wurin Dady.
Anan ya 'bata lokaci, ganin hadari ya hadu sai ya yanke hukuncin komawa gida ya huta bayan la'asar sai ya je wurin Hajiya.
Ya isa gidan, da mukallin hannun sa ya bude gidan, ya shiga, dakinsa ya kwanta sai ya tuna yana son dauko Agogon sa dake dakin Sa'adah da bai dauko ba, kullum sai ya fita yake tunawa.
Ya mike ya doshi dakinta, ya duba ya dauko Agogon, har ya kai bakin kofa sai ledar kan gadon ta ja hankalinsa, mussaman da ta kasance ta waje ce, dan haka sai ya koma ya dauko ya bude, ganin kaya ne, ya zazzage su akan gadon, kayan Jawad basu dauki hankalinsa kamar tsadadden agogo da kuma kwalin wayar ba.
Zuciyarsa ta dinga bugawa, wani irin tsoro, da razani suka shige shi, shaidan ya kawowa zuciyar sa caffa! kawai sai ya dinga tuno sadda take cewa matan bariki na mallakar duk abin da suke so cikin gaggawa.
Innalillahi wa ilaihir raji'un kawai ya ke ambata, ya kalli socket ya hango wayar da bai san da ita ba, ya karasa gurin ya dauko, yana dubawa, ganin Blackberry ce kuma babbar sai hankalinsa ya sake tashi, ya kasa budewa saboda ta sa mata password.
Da yake data a kunnen ta ke
Ya dinga ganin sakonni na shigowa ba jinkiri.
Ya dinga jin jiri na katantanwa da shi, bai taba jin tashin hankali irin na yau ba,me Sa'adah take yi haka? A ranar ya gane duk yadda yake daukarta ta wuce nan.
Kusan mintina talatin yana zaune a dakin nata, cikin tashin hankali iri iri.
Daidai lokacin ta shigo gidan a sukwane, tunda ta ga motarsa a waje ta shigo a hanzarce, zuciya na 'bari, ba ta yi zaton zai dawo ba, wacce irin 'kaddara tasa ta bar kayan nan da waya a fili?
Kai tsaye 'dakinsa ta shiga dan ganin wanne kallo zai mata?
Har 'bandaki baya nan, bugun zuciyar ta ya karu, cikin shahada ta nufi ta nufi falon , bata ganshi ba, fargabar ta ta 'karu ta tabbatar ya ga wayar nan.
'Karfin hali ta lalubo ta dora a fuskarta duk kuwa da zuciya da gangar jikinta sun 'ki karban wannan 'karfin halin.
Da sallama a bakinta ta shiga dakin, yanayin da ta iske shi, sai da ya ka'da mata 'ya'yan hanji.
Bai 'dago ya kalleta ba, amma ya amsa sallamarta da murya marar amo.
Ta aro jarumtar 'boye kaduwar da take ciki, ta matsa kusa da shi tana cewa "Ba ka jin dadi ne, da kace sai yamma za ka dawo, a Ina ka baro Jawad?"
Ya dago yana kallon ta, yana jin wata irin tsanar ta na neman Samun muhalli a zuciyar sa.
Bai amsa mata ba, ya zuba mata ido yana jin tamkar ya tashi ya yi ta dukanta. marar gaskiya akace ko a ruwa gumi ya ke yi, ta dinga jin 'barin jiki irin na fargaba, ta yi sukuri tamkar ace 'kyat ta fece da gudu.
Ya mi'ke ya isa inda take tsaye yace " A Ina kika samo wadannan kayayyaki masu daraja?"
Cikin rawar murya tace "Anty Sumayya ta aiko mana, dama na fito da su idan ka dawo, ka gani"
Ya zuba mata ido yana kallon yadda ta ke shirya zancen da babu azanci a cikinsa, ledar kayan ta nuna daga Egypt kayan suke, sannan a cikin kwalin wayar akwai risit din siyan wayar a ciki mai dauke da sunanta a takaice( S.B). Kwanan watan ya nuna ta kai wattanni biyu a hannun ta.
Ya ce "Sumayya yaushe ta je Egypt ban sani ba? Ta hannun wa sa'kon ya same ki?"
Ta muzanta kwarai da gaske, ta kasa bude baki ta yi magana.
Ya dauko wayar yana cewa "Wannan wayar da ta lashe manyan ku'da'de Sumayya ta aiko miki? Ko kuma saurayin ki, ki ka fa'dawa mijinki ya gaza?"
Ya mi'ka mata ya ce "Bu'de mini! tashin hankalin ta ya ninku, Baki na rawa ta ce "kar ka yi aiki da zato, wayar Halima ce ba tawa ba".
Idonsa ya canja zuwa jah, jijiyoyin kansa suka bayyana ru'du ru'du, makoshinsa ya bushe, zuciyarsa ta cushe da tsananin bacin rai, hankalin sa ya kai 'kololuwa wurin tashi.
"A zafafe sosai ya ce " wacce maganar zan kama, wayar Halimace ko Sumayya ce ta kawo miki?
ki bude min wayar nan tun kafin na tozarta ki, domin sai na dauke ki munje gaban Halima, Ina rantse miki da ubangiji agaban Baffa za'a yi komai".
Ta fara kuka tana cewa "Ajiya ta kawo mini itama ba tata bace, dan Allah ka yi hakuri, gaskiya na fada maka".
Karon farko da hakurinsa ya kwace ya dauke ta wani irin mari mai katse ji da gani na wucin gadi! ya ce "Da aurena Sa'adatu, da aurena akan ki? Idan wayar Halima ce to wannan Agogon da kayan na uwar waye?"
Tsananin zafin marin yasa habo ya goce mata, duk da hakan bata damu ba, asalima kukan tsayawa ya yi cak duk da hakan furucinsa ya fi firgita ta sama da marin
A gigice ta ce " gaskiya na fada maka, ka yarda da Ni"
Ta riga ta kudiri aniyar komai zai mata ba zata bude ba, domin a jiya ma sun yi chart da Khalil, duk da ba wani dirty abubuwa suka tattauna ba, amma akwai maganganun da ba zata so Mk ya gani ba, mussaman hotunan sa da ya turo mata, ita kuma ta tura masa na Jawad.
Hankalin Mk ya kai ma'kura wurin tashi ya matsa kusa da ita sosai yace "ki bude min wayar nan idan ba so kike ki wulakanta kanki ba".
ta karba, amma ilahirin jikinta rawa yake yi na tsananin tsoro da firgici.
Fiye da mintina goma tana ri'ke da waya amma ta 'ki budeta, lamarin da ya sanya Mk ya ce ta fita suje gidan su Halima, ya tasa ta a gaba har tsakar gida, anan ta coge akan ita ba zata je gidansu wata Halima ba.
Ya nuna ta da yatsa ya ce "Billahillazi sai kin je, daukota zamu yi, muje gaban Baffa shine al'kalin wannan jahilcin na ki".
Ta rasa inda zata tsoma ranta, ta tabbatar Halima kai tsaye za ta ce ba wayarta bace tunda ba ta 'ki ta kashe auren Mk ba dama.
Ya koma 'daki dauko mukallin mota, tashin hankali yasa ya kasa ganin inda ya ajiye, yana cikin dube dube kawai sai jin 'karar fashewar abu ya ji da karfin gaske.
Ya fito da sauri, ya ga wayar ta rotsa, ta fashe sosai, ta wargaje yadda ba zata tashi ko ta moru ba.
Bai san sadda ya isa gareta ba, ya sha'keta sosai, sai da ya lura tana dab da sumewa ya wancakalar da ita, ya hau dukanta da hannuwansa.
Ganin yana dukan amma ba abin da yake ji na sauki sai ma 'karin tafasar zuciya, ya kyaleta ya zauna a kasa dabas ya dinga ambaton innalillahi wa ilaihir raji'un, hawaye bakin ciki na tsere akan fuskar sa.
Ta dago da 'kyar ta ga yadda ya ke zubar d hawayea! a fili bai damu da aga yana kukan ba, duk wata dauriyarsa sa ta kwace a YAU.
Hankalin ta ya sake ri'banya tashi, ta dinga kuka tana fadin " Ka yafe mini, wallahi ba wayata bace".
A tunzure ya antayo ashar irin wadda bata taba jinta ba, ya maka mata, tare da cewa "Idan ki ka kuma bude baki da nufin yi min, magana ko bani ha'kuri Billahillazi sai na miki abin da baza ki manta ba".
Wayarsa ya ciro aljihu, da kyar ya iya lalubo sunan Fahad Auwal!
Dalibinsa ne tun a FGC yana cikin samarin Sa'a duk da dai bata ta'ba kulashi ba, sannan yanzu ma dalibinsa ne a B.U.K.
Da girmamawa ya gaida Mk.
Cikin rashin sukuni Mk yace "Fahad cikin class mate din ku na FGC akwai mai karatu a Egypt kuwa?"
Dan Jim Fahad ya yi sannan yace"Khalil Ibrahim ne kawai a Egypt".
Ko godiya Mk bai tsaya yi ba, ya katse wayar.
Ya bude mata dukkan hannuwansa biyu, a yau bata tsaya jan aji ba, da sauri ta fada masa, yasa dukkan hannuwansa ya rungumeta tsantsan ita kuma tana kuka kasa kasa.
Baice komai ba, illah shafar bayanta yana jin sau'kin 'daurin da kirjinsa ya yi akanta.
Tun daga ranar ya canja, ya daina 'daure fuska, sannan ya bu'de mata kofar nisha'di a tsakanin su, sab'anin satikan da suka shude da ya rufe ta rif.
Saukowar Mk ya sa ta fara murmurewa, tashin hankalin da ta shiga yasa ta manta da wayar ta Bb, sai yanzu da ta sami nutsuwa take fitowa da ita, idan ya fita.
* Tsautsayi*
Ranar da ta zama 'bakar Rana ga rayuwar ma'auratan guda biyu, wadda tarihin rayuwar su ba zai cika ba, sai an sako ranar.
Asabar ce cikin watan Augusta da safe bayan sun kammala karyawa cikin walwala, ya shirya ya mata sallama, zai je ta'aziya Baban Abokinsu ya rasu daga nan zai zarce gidan su ba zai dawo ba sai yamma, ta masa addu'ar dawowa lafiya,ya tafi tare da Jawad. Kafin ya fita ta nemi iznin za ta je kitso, bai hana ba, ya amince mata.
Sai da ta gama komai na gyaran gida, ta yi wanka, ta tsaya jikin wardrobe tana nazarin rigar da zata sanya.
Wata daguwar riga ta janyo data jima bata sa ta ba, garin janyowar ta hado da ledar kayan da su Halima suka kawo mata na tsarabar khalil, wadda ta manta da su, ta leka ta ga rigunan Jawad ne da agogon ta, sai kwalin wayar Blackberry, ta jefa kan gado akan sai ta dawo zata san yadda zata yi ta nunawa Mk rigunan, dan ta fara sakawa Jawad tunda tsadaddu ne.
Ta dauko wayar daga inda take boyewa, ta jona a caji, ta shirya ta rufe gidan ta fita, zuwa bayan layinsu inda take kitson.
Mk da ya fito daga gidan rasuwar gidan Mahmoud suka zarce adalilin motar Mahmoud din ta lalace, dan haka ya kai shi, ai kuwa Jawad ya ce anan zai zauna wurin Dady.
Anan ya 'bata lokaci, ganin hadari ya hadu sai ya yanke hukuncin komawa gida ya huta bayan la'asar sai ya je wurin Hajiya.
Ya isa gidan, da mukallin hannun sa ya bude gidan, ya shiga, dakinsa ya kwanta sai ya tuna yana son dauko Agogon sa dake dakin Sa'adah da bai dauko ba, kullum sai ya fita yake tunawa.
Ya mike ya doshi dakinta, ya duba ya dauko Agogon, har ya kai bakin kofa sai ledar kan gadon ta ja hankalinsa, mussaman da ta kasance ta waje ce, dan haka sai ya koma ya dauko ya bude, ganin kaya ne, ya zazzage su akan gadon, kayan Jawad basu dauki hankalinsa kamar tsadadden agogo da kuma kwalin wayar ba.
Zuciyarsa ta dinga bugawa, wani irin tsoro, da razani suka shige shi, shaidan ya kawowa zuciyar sa caffa! kawai sai ya dinga tuno sadda take cewa matan bariki na mallakar duk abin da suke so cikin gaggawa.
Innalillahi wa ilaihir raji'un kawai ya ke ambata, ya kalli socket ya hango wayar da bai san da ita ba, ya karasa gurin ya dauko, yana dubawa, ganin Blackberry ce kuma babbar sai hankalinsa ya sake tashi, ya kasa budewa saboda ta sa mata password.
Da yake data a kunnen ta ke
Ya dinga ganin sakonni na shigowa ba jinkiri.
Ya dinga jin jiri na katantanwa da shi, bai taba jin tashin hankali irin na yau ba,me Sa'adah take yi haka? A ranar ya gane duk yadda yake daukarta ta wuce nan.
Kusan mintina talatin yana zaune a dakin nata, cikin tashin hankali iri iri.
Daidai lokacin ta shigo gidan a sukwane, tunda ta ga motarsa a waje ta shigo a hanzarce, zuciya na 'bari, ba ta yi zaton zai dawo ba, wacce irin 'kaddara tasa ta bar kayan nan da waya a fili?
Kai tsaye 'dakinsa ta shiga dan ganin wanne kallo zai mata?
Har 'bandaki baya nan, bugun zuciyar ta ya karu, cikin shahada ta nufi ta nufi falon , bata ganshi ba, fargabar ta ta 'karu ta tabbatar ya ga wayar nan.
'Karfin hali ta lalubo ta dora a fuskarta duk kuwa da zuciya da gangar jikinta sun 'ki karban wannan 'karfin halin.
Da sallama a bakinta ta shiga dakin, yanayin da ta iske shi, sai da ya ka'da mata 'ya'yan hanji.
Bai 'dago ya kalleta ba, amma ya amsa sallamarta da murya marar amo.
Ta aro jarumtar 'boye kaduwar da take ciki, ta matsa kusa da shi tana cewa "Ba ka jin dadi ne, da kace sai yamma za ka dawo, a Ina ka baro Jawad?"
Ya dago yana kallon ta, yana jin wata irin tsanar ta na neman Samun muhalli a zuciyar sa.
Bai amsa mata ba, ya zuba mata ido yana jin tamkar ya tashi ya yi ta dukanta. marar gaskiya akace ko a ruwa gumi ya ke yi, ta dinga jin 'barin jiki irin na fargaba, ta yi sukuri tamkar ace 'kyat ta fece da gudu.
Ya mi'ke ya isa inda take tsaye yace " A Ina kika samo wadannan kayayyaki masu daraja?"
Cikin rawar murya tace "Anty Sumayya ta aiko mana, dama na fito da su idan ka dawo, ka gani"
Ya zuba mata ido yana kallon yadda ta ke shirya zancen da babu azanci a cikinsa, ledar kayan ta nuna daga Egypt kayan suke, sannan a cikin kwalin wayar akwai risit din siyan wayar a ciki mai dauke da sunanta a takaice( S.B). Kwanan watan ya nuna ta kai wattanni biyu a hannun ta.
Ya ce "Sumayya yaushe ta je Egypt ban sani ba? Ta hannun wa sa'kon ya same ki?"
Ta muzanta kwarai da gaske, ta kasa bude baki ta yi magana.
Ya dauko wayar yana cewa "Wannan wayar da ta lashe manyan ku'da'de Sumayya ta aiko miki? Ko kuma saurayin ki, ki ka fa'dawa mijinki ya gaza?"
Ya mi'ka mata ya ce "Bu'de mini! tashin hankalin ta ya ninku, Baki na rawa ta ce "kar ka yi aiki da zato, wayar Halima ce ba tawa ba".
Idonsa ya canja zuwa jah, jijiyoyin kansa suka bayyana ru'du ru'du, makoshinsa ya bushe, zuciyarsa ta cushe da tsananin bacin rai, hankalin sa ya kai 'kololuwa wurin tashi.
"A zafafe sosai ya ce " wacce maganar zan kama, wayar Halimace ko Sumayya ce ta kawo miki?
ki bude min wayar nan tun kafin na tozarta ki, domin sai na dauke ki munje gaban Halima, Ina rantse miki da ubangiji agaban Baffa za'a yi komai".
Ta fara kuka tana cewa "Ajiya ta kawo mini itama ba tata bace, dan Allah ka yi hakuri, gaskiya na fada maka".
Karon farko da hakurinsa ya kwace ya dauke ta wani irin mari mai katse ji da gani na wucin gadi! ya ce "Da aurena Sa'adatu, da aurena akan ki? Idan wayar Halima ce to wannan Agogon da kayan na uwar waye?"
Tsananin zafin marin yasa habo ya goce mata, duk da hakan bata damu ba, asalima kukan tsayawa ya yi cak duk da hakan furucinsa ya fi firgita ta sama da marin
A gigice ta ce " gaskiya na fada maka, ka yarda da Ni"
Ta riga ta kudiri aniyar komai zai mata ba zata bude ba, domin a jiya ma sun yi chart da Khalil, duk da ba wani dirty abubuwa suka tattauna ba, amma akwai maganganun da ba zata so Mk ya gani ba, mussaman hotunan sa da ya turo mata, ita kuma ta tura masa na Jawad.
Hankalin Mk ya kai ma'kura wurin tashi ya matsa kusa da ita sosai yace "ki bude min wayar nan idan ba so kike ki wulakanta kanki ba".
ta karba, amma ilahirin jikinta rawa yake yi na tsananin tsoro da firgici.
Fiye da mintina goma tana ri'ke da waya amma ta 'ki budeta, lamarin da ya sanya Mk ya ce ta fita suje gidan su Halima, ya tasa ta a gaba har tsakar gida, anan ta coge akan ita ba zata je gidansu wata Halima ba.
Ya nuna ta da yatsa ya ce "Billahillazi sai kin je, daukota zamu yi, muje gaban Baffa shine al'kalin wannan jahilcin na ki".
Ta rasa inda zata tsoma ranta, ta tabbatar Halima kai tsaye za ta ce ba wayarta bace tunda ba ta 'ki ta kashe auren Mk ba dama.
Ya koma 'daki dauko mukallin mota, tashin hankali yasa ya kasa ganin inda ya ajiye, yana cikin dube dube kawai sai jin 'karar fashewar abu ya ji da karfin gaske.
Ya fito da sauri, ya ga wayar ta rotsa, ta fashe sosai, ta wargaje yadda ba zata tashi ko ta moru ba.
Bai san sadda ya isa gareta ba, ya sha'keta sosai, sai da ya lura tana dab da sumewa ya wancakalar da ita, ya hau dukanta da hannuwansa.
Ganin yana dukan amma ba abin da yake ji na sauki sai ma 'karin tafasar zuciya, ya kyaleta ya zauna a kasa dabas ya dinga ambaton innalillahi wa ilaihir raji'un, hawaye bakin ciki na tsere akan fuskar sa.
Ta dago da 'kyar ta ga yadda ya ke zubar d hawayea! a fili bai damu da aga yana kukan ba, duk wata dauriyarsa sa ta kwace a YAU.
Hankalin ta ya sake ri'banya tashi, ta dinga kuka tana fadin " Ka yafe mini, wallahi ba wayata bace".
A tunzure ya antayo ashar irin wadda bata taba jinta ba, ya maka mata, tare da cewa "Idan ki ka kuma bude baki da nufin yi min, magana ko bani ha'kuri Billahillazi sai na miki abin da baza ki manta ba".
Wayarsa ya ciro aljihu, da kyar ya iya lalubo sunan Fahad Auwal!
Dalibinsa ne tun a FGC yana cikin samarin Sa'a duk da dai bata ta'ba kulashi ba, sannan yanzu ma dalibinsa ne a B.U.K.
Da girmamawa ya gaida Mk.
Cikin rashin sukuni Mk yace "Fahad cikin class mate din ku na FGC akwai mai karatu a Egypt kuwa?"
Dan Jim Fahad ya yi sannan yace"Khalil Ibrahim ne kawai a Egypt".
Ko godiya Mk bai tsaya yi ba, ya katse wayar.