← Book details Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 113

Sashe 8

Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Jin ta yi shiru yasa shi fadin, "Ban aure ki akan wani dalili ba sai don ina son ki, ina zaune da ke saboda ina son ki, ina kuma jin dadin zama dake, don haka ba wani abin dazai raba ni da ke matu'kar ba ke ce kika bijire mini ba. Ina son ki Farida irin son da zan iya sadaukar miki da komai, ba abu mai da'di a soyayya irin a so ka da kai da dukkan matsalarka, a mutuntunta ka, a kuma yarda ka isa koda kuwa a zahiri baka isan ba.

Ba abin da baki mini na kyautatawa ba, ba kuma zan manta ba, kar ki yarda ki sa a ranki wai zan juya miki baya akan Sa'adah, kar ki ji a ranki na fi son ta akan ki, ni ban san wacce na fi so ba, wacce duk ta kiyaye mini 'bacin Raina, ta zauna da ni lafiya cikin aminci, ta yarda bazan musguna mata da gangan ba, ba shakka itace zata jagoranci zuciya ta. Idan kuma kina da matsala akan dawowarta fada mini zan iya fasawa, idan har hakan zai fi zama masalaha."

Rungume shi ta yi sosai ta na jin wata irin nutsuwa ta na shigar ta.

Ashe har haka matsayinta yake, ashe darajarta ta kai haka? kai ta hau girgizawa, ta ce, "A a ban da matsalar komai wallahi, kawai dai fargaba nake kar ka canja mini kar ka juya mini baya".

Murmushi ya yi yasan tana da hujjarta tunda an yi hakan a baya, don haka sai ya ce, "Aure ya wuce wasa ba na fatan kuma na rabu da matar aure na akan wata matar, ki cire wannan tunanin don yanzu ke ce matata, zan iya ha'kura da ita, matu'kar ta ce ba za ta zauna da ke ba, ke ko ba zan iya rabuwa da ke akan ta ba"

Sai kawai ta saki kukan da take ta haniniya da shi akan kar ya zubo, ya 'dago ta ya shiga lashe hawayen nata, wanda na tsananin murnar maganganunsa ne ko da ba haka ba ne a zuciyarsa ya nuna mata girmamawa tare da karramawa, ta kuma gamsu yana son ta sosai.

"Ubangiji Ya sanya alheri ya zaunar da mu lafiya, Allah ya 'kara maka lafiya, da bu'din arziki ya kuma hore maka ikon yin adalci"

Amin ya ke ta fa'di tare da jin ba abu mai dadi a duniya irin mace ta gari, mai fahimta, mai kuma ilimi da aiki da shi, don sau tari shedanun matan masu ilimin ne, kawai aiki da shi ne ba sa yi. A fili ya ce, "Ubangiji Ya miki albarka My Feri-Feri, Allah Ya ba ki rabo mai amfani."

Zuciyarta ta yi fes ta na jin dadin wannan addu'ar da yake yawaita yi mata na albarka da samun zuri'a mai albarka.

Suna haka har aka kira La'asar sannan suka mike shi ya yi Alwala ya yi masallaci ita kuma ta yi a 'dakinta.

Bayan ya dawo Masallaci bai shiga gidan ba a 'kofar gidan ya samu gefe ya zauna ya ciro wayarshi ya fara lalubo lambarta, karon farko bayan shudewar lokaci mai yawa, daf da za ta tsinke ya ji ta dauka, Sallama ta yi, ya amsa, sai kuma ta ja bakinta ta tsuke, shi kansa sai al'amarin ya zo mishi a bai bai, cikin 'karfin halin da aka san namiji da shi ya ce, "Ke ba ki iya gaisuwa ba ne?"

Cike da son ta nuna mishi ba shi da sauran matsayi a zuciyarta ta ce, "Waye?"
Bai yi mamaki ba, dan haka sai ya nufin 'kunsa mata takaici shima.

"Wadda ki ke ta sallar dare ne akansa".

Yana rufe baki ta ce, "Babu wannan halittar"
tare da kashe wayarta.

Zuciyarta na bugawa wai yau mafarki take ne ko kuwa da gaske Malam ne ya kira ta taka nas? Wacce iriin sa'a yau ta tashi da ita? tana tuna kalaminshi na 'karshen maganar su a wani lokaci da ya shu'de, sai ta ji murnarta ta koma ciki, ba za ta saurare shi ba har sai ya janye kalamunshi, da kallon da yake mata, idan ko ba haka ba, to tabbas ba za ta sake mu'amala da shi ba, bare babbar mu'amala irin ta aure, ko da hakan na nufin mutuwarta ne.

Al'kalamin
SURAYYA DAHIRU
✍🏼✍🏼✍🏼
[5/16, 13:26] +234 806 791 2288: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺

*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•

*SADAUKARWA GA*
*SADIQ ABUBAKAR*

*Fatan Alheri ga*
_DANDALIN MUM KHADY_.
🤝🏽

15-16

Mamakin ta ne ya yi matu'kar kama shi wai yau shi ta kashe ma waya? Anya Sa'adah za ta canja hali kuwa?

Sake 'kiran ta ya yi a karo na biyu, amma ga mamakin sa har 'kiran ya katse ba ta 'daga ba.

Ya ri'ke wayar ya yi jim cikin sanyin jiki da tunani iri iri.
Ya san kirkinta ya fi sharrinta yawa, har yau kuma, shi dai a idanuwanshi bai ga wacce ta iya tsara kwalliya da gayu irin Sa'adah ba, ma'abociyar son 'kyale-'kyale ce, kusan wannan dabi'ar tata na son kayan 'kawa masu tsadar gaske ya taimaka wurin sake jefa aurensu cikin garari.

Lambar amininshi ya lalubo Dr. Mahmoud Karfi, ba ta dade tana dokawa ba, ya ji an 'dauka, tare da sallama, kai tsaye MK ya ce, "Kana Ina?" Daga can bangaren ya amsa da cewa, "Ina makaranta, lafiya?"

"Lafiya Lau jira ni gani nan zuwa"

Ya katse wayar ya mi'ke ya shiga gida, ya dauki mukullin motarshi, tare da yi wa matarshi sallamar ya fita, ta bi shi da addu'ar dawowa lafiya.

"Kai tsaye sabuwar Jami'ar Bayaro ya nufa, bai bi takan ofishin saba, ya zarce ofis din Dr. Mahmoud Karfi.
Da sallama ya shiga shi ka'dai ya tarar yana dakon isowarsa, musabaha suka yi, Dr. Karfi ya dube shi, "Ka sa ni tunani iri iri fa"

Jim MK ya yi tare da cewa, "Wallahi ru'dani na shiga, ka san Hajiya ta matsa akan maganar na dawo da yarinyar nan, to dai yanzu na amsa mata akan na amince bayan na yi addua na kuma ji na aminta da lamarin. Wai yau na 'kira ta a waya da farko ce mini ta yi waye?"

Dariya ta so subuce wa Dr. 'Karfi, amma ya kirne, shi kuma ya zarce da cewa,
"Karshe kuma sai ta kashe mini waya"

"Alhamdulillah!"

'Karfi ya furta a fili tare da cewa "Ni na da'de ina ji a jikina idan dai ba mutuwa ce ta sure dayanku ba, to kuwa za ku sake ha'dewa. Shi yasa na kyale ka ka sami nutsuwa, ka san dai Sa'adah ta bi ka iyakar bi akan ka yafe mata, amma ba ka yi ba, ka zo ka yi aure dole ta gaji ta yi fishi, amma na san fishin ba mai yawa ba ne, tunda tana son ka."

A sanyaye ya ce, "Anya kuwa? ba ku san ta ba ne, a makarantar su Jawad fa baka ga iya shegen da ta mini a bainar nasi ba"

Dariyar da Dr. 'Karfi ya ke ri'kewa ta subuce, ya hau yi sosai, har ta sha'kar da MK, don haka sai ya mike ya ce, "Na gode"

Da sauri 'Karfi ya ruko shi ya na fadin, "Yi hakuri ka zauna ai ba mu gama ba"

Cikin fushi ya ce, "Ya zan zo maka da matsalar da ta dame ni, ka sani gaba kana mini dariya ka mayar da ni mahauka ci!"

"Wane ni Allah ya huci zuciyarka zauna mu gama"
'Karfi ya fada bayan ya shanye dariyarshi. Komawa ya yi ya zauna amma fuskar nan a ha'de.
"Yanzu ka san me? Zan je na same ta mu yi magana, idan ya so sai mu koma tare, daga nan kuma shike nan sanda za ka je ma ba zan sani ba"

Cikin cin magani ya ce "Ni wallahi bazan ta zarya a wajenta ta na mini iya shege ba, yanzun ma Hajiya ce ta matsa amma banda haka ta je can ta 'karaci tsiyarta"

Mahmoud ya ce, "Yanzu ma damuwar da na gani a fuskarka, akan ta kashe maka waya, Hajiya ce ta matsa ka fada mini?"

Tsaki ya ja, ya san sha'kiyanci zai masa, tunda idan akwai wanda ya san yadda yake son Sa'adah to kuwa Mahmoud ne.

Sai kawai ya mi'ke ya fice yana fadin, "Sai ka yi kai ka'dai."

Shi kuwa ya ci gaba da dariyar shi a sake yadda yake so.

Ta idar da sallar Maghrib ke nan tana zaune tana tasbihi, zuciyarta cike da farin cikin fara gyaruwar al'amuranta, wayarta ta hau kuwwa, ganin sunan Baban dady yasa ta jin wani farin ciki ya 'kara kama ta, ba ta yi azarbabin 'dagawa ba har ta katse.

Kafin ta yi wani yun'kurin, ya sake 'kira, haka ta gama yau'kinta, ta dauka hadi da yin sallama,"Ranki ya dade ai na zaci ba za ki dauka ba ne"

'Yar dariya ta yi, "Akan me? Sallah na idar."

"Ya mutanen gidan to?" Ya tambaya, ta amsa mishi da, "Duka lafiya Lau"

"Ina son ganin ki wanne lokaci zan same ki?"

sanin mutuncinsa da karamcinsa ya sa ta fadin ko yaushe "Ina gida!"

"To ki saurare ni anjima kadan zan iso."

"Sai ka zo." Ta fada tana jin wani irin nisha'di na tsirga mata.

Wanka ta shiga ta fito ta shirya cikin lallausan yadi ruwan hoda, mai shegen tsada ba shi da adon komai haka yake plane sai yauki yake da 'daukar ido. Doguwar riga ne aka 'kawata da shudin stones masu sheki matu'ka, don haka ta yane jikinta da matsakaicin mayafi blue,
mai da roll on kawai ta shafa, kasancewar turarukanta sun kama kayanta sosai kuma ma'abociyar yin turaren kaya ne irin na barebari (garam). Duk da dare ne, sai da ta shafa powder ta kuma zagaye le'banta da jan baki ruwan hoda.
Chapter 8 · 0% Book details