← Book details Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 113

Sashe 21

Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A ranar Baffa ya zaunar da Sa'adah tare da mahaifiyarta ya ce, "Bakin da suka bakunce ni a yammacin yau, zuwan Iyah ne. Yaron nan Mutari ne ya turo a ba shi iznin neman amincewarki, ni kuma na ba shi dama ya nemi yardarki ba don Ina jin tsoron kada ki yi mini *HALIN YAU* ba, da kai tsaye zan ce na ba shi su zo ayi maganar aure. Saboda yaron nutsatstse ne , ya san mutuncin manya mai kokarin neman na kansa ne, kullum ya zo shagon askinsa sai ya zo ya gaishe ni, ban kuma taba jin hayaniyarsa da wani ba, kiga dai yadda shagon yake cika dam da matasa amma ban taba jin an ce ana fada da shi ba.
Da shi muke sallar Magariba da Isha kullum yana sahun gaba, ba zan miki dole ba amma da a ce zan miki zabi ki karba, to da ba zan tsallake shi ba. Idan kuma kin kafe shi ma bai miki to lallai ki tsayar da wanda ya miki da zarar kin kammala makaranta zan aurar da ke, ki ri'ke wannan!"

Alkalamin
SURAYYA GWARAM
✍️✍️.

🌺 *HALIN YAU*! 🌺

•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•

*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*

*TALLAH* *TALLAH*!
*KAR KU BARI A BARKU A BAYA WURIN KARANTA DADDAN LABARIN NAN*

*⚜️BUƊAƊƊIYAR SOYAYYA⚜️*
_NA_
*Jameey yar'mutan kankia*.

*Promo* *Promo* *Promo*

_Daga yau 21/5/2022 promo dinmu zai fara,har zuwa 30/5/2022 inshaa Allah,ga yanda promo din yake_.

*#300-sau biyu a rana*
*#500 -sau ukku a rana*
*#700 -sau hudu a rana*

_Kiyi ma wanann number magana danjin yanda zaki biya 08160508316_.

*MASU SON A TALLATAH MUSU HAJARSU KOFA A BUDE TAKE*
_TUNTUBI_
08032773332.

*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.

34-35.

Baffa na rufe baki, Inna ta yi caraf ta ce "Gara ka jaddada mata don ni a halin da nake ciki da ita, ban ki ka kawar mini da ita a cikin wannan watan ba."

'Dan murmushi ya yi mai sauti tare da cewa, "Anya Salamatu ba gaskiyar Iyah ba ne da take cewa kin fi nan nan da Sumayya?"

Da sauri ta ce "Hmm Ni yaushe ma na ga yayar tata bare har na nuna son kan da take korafi? Mafi yawa ai karamin 'da ya fi shiga rai, sai idan halinsa ne marar kyau ko ba ya jin magana".

Ya sake fadada fara'arsa ya ce "Ato ni ma dai na ce ban taba ganin wacce ba ta ririta autarta ba sai ke".

Da sauri Sa'adah ta ce, "Ai ni Baffa Inna ba ta dauke ni a auta ba, ALLAH ne ya mayar mata da ni auta akan dole."

"To ki dinga jin maganar da ake fada miki, ki rage dogon buri, sannan ina sake jan hankalinki akan yaron nan kar ki bari ya kubuce miki."

Ta yi kasa da kanta, nuna alamun kunya, a ranta fadi take "Son sa nake sosai Baffa daina jan hankalina" 😀
Sa'ade ke nan.

Daga haka ya sallame ta ta mike tana fadin "Sai da safe."

Tana zuwa, ta zube kan katifa tana jin wani irin nisha'di na tsirga mata, idonta a rufe wani irin shauki yana mamayar ta.

Can kuma ta fara tunanin maganar Baffa in da ya ce, "Shagon aski! Kar dai The Boss barbing shop?" Duk titin ba katon shago irinsa, shago ne da ya samu karbuwa wurin samari yan kwalisa da kullum suke dafifin zuwa gyaran suma ko yin aski. Ashe shi yasa kwanaki ta gan shi agun? A fili ta ce, "Hadadden guy dan boko da yin aski?"

A take wani sashi na zuciyarta ya ce mata ai ya huce takaicin bani-bani a wurin iyaye da dangi, ya kuma kere sa'a a tsakanin abokai masu jiran gwamnati ta ba su abin yi.

Maimakon ta ji abin alfahari ya yi, ta yabawa kokarinsa na dogaro da kafafunsa, sai ta ji tana jin kunyar ace saurayinta wanzami ne 😁.

Washegari da wurwuri ta shirya ta biya wa Zainab Ma'aji, a hanya ta ba ta labarin yadda ta kaya tsakaninta da MK, murna sosai Zainab ta yi tare da cewa "To ki kiyaye abin da ya ce baya so, sannan ki kama bakinki."

Duk sa idon su Halima ba su iya gano soyayyar da ke tsakaninta da Malamin nasu ba, saboda yadda suka rufe kofar da za a gane akwai wata alaka a tsakaninsu da ta wuce Malami da dalibarsa.
Khalil ne kawai ya kasa gamsuwa musamman yadda ya lura Sa'adah ta yi matu'kar sauya masa, sannan ta toshe duk kofar da suke samu su yi hira, zai mata letter sau goma bai fi ta ba shi amsa daya ba a dukunle. Wannan sauyin da yake gani a tare da ita yasa ya sake kullatar MK yana ganin tun zuwansa makarantar ya canja masa Sa'arsa. Saboda haka ya sake daukar samfurin nuna rashin da'a a gaban Uncle MK, duk lokacin da ya zo ajin sai Khalil ya yi abin da zai harzuka zuciyarsa, wanda hakan ya janyo kiyayya mai tsananin gaske a tsakaninsu, wata rana an fita break ya samu ya yi magana da ita a dalilin ya sa Halima ta tsayar masa da ita, duk tambayar da ya mata idan laifi ya mata ta yafe masa.

Ta ba shi amsa da cewa, "Khalil ba ka mini komai ba, kawai ganin jarrabawarmu ta gabato akwai bukatar mu fuskanci karatunmu ne."

Kai tsaye ya ce, "Zan so wannan dalilin ya zama shi ne gaskiyar magana, amma na san idan na rantse ba zan yi kaffara ba, cewar akwai wani dalilin ba wannan ba. Ni koma mene ne zan yi ha'kurinsa amma idan wannan mugun Malamin is behind your changes, to ba zan yafe masa ba!" Ya fada cike da 'bacin rai.

A tunanin Sa'adah tunda ya turo a ba shi iznin neman amincewarta, an kuma bashi ai zai dinga zuwa zance, sai ta ga an kwashe kwanaki kusan goma bai zo ba, bai kuma sake waiwayar ta ba ko a makaranta, wannan abu na ci mata tuwo a kwarya musamman da a safiyar yau 'yan ajin nasu suka yi laifin da gaba'daya ya zane su, amma da ya zo kanta sai ta ga ya dage iya karfinsa ya zabga mata bulala har hudu maimakon bibiyu da ya yi wa kowa.

Abin ya tsaya mata a rai sosai, sai kawai ta tsiri fishi da shi, ya lura da fishin da take yi amma sai ya share, tun ranar da ya gan ta tana hira da Khalil ya ji gabadaya ya rasa inda zai sa ransa shi yasa da ya samu damar dukan yan class din ya ninka nata dukan!

Ranar wata Juma'a da yamma Sa'adah na zaune a tsakar gida tana yanke farce ta yi kwalliya da daguwar riga ta shadda purple (Mai ruwan Shanshanbale) a lokacin surfani aikin sama ake ya yi, dinkin ya yi kyau sosai!
Innarta sai mita take yi, akan har yau Muutar bai zo ba, ganin Sa'adah ta yi shiru ba tare da ta ce komai ba, sai ya harzuka ta, ta zuba mata ido ta ce, "Iyah ba magana nake yi ba ne kika mini kunnen uwar shegu?"

Tura baki ta yi da ya zame mata jiki cikin yanayin tabara ta ce, "Ayya Inna ni ma ban sani ba fa!"

A tunzure ta ce, "Kin sani Iyah kawai dai kin nuna masa halin naki ne"

"To ni a ina zan nuna masa halin nawa tunda ko a makaranta ma ba kula ni yake yi ba, ni wallahi na fara tantamar shi ya aiko yana so na? Shekaranjiya ba ki ga dukan da ya mini ba."

Jikin Inna ya yi sanyi ta fara wasiwasi tana fatan Allah ya sa lafiya, amma sai ta ce, "Allah ya sa dai ba wani abin ba ne."

Tana rufe baki yaro ya yi sallama ya ce, "Wai ana sallama da Sa'adatu" Da sauri Innar ta ce, "Je ka ce Wai waye?"

Ba a jima ba ya dawo ya ce, "Wai Mukhtar ne." Dadi ya kamata da sauri ta ce, "Je ka ce ta na zuwa."

Ta juya ta ga hakimar ko motsawa ba ta yi ba tana ci gaba da yankan farcenta, kamar za ta yi magana sai kuma ta shanye, tana mai son ganin iya gudun ruwanta.

Fiye da shudewar mintina goma tana zaune ta gama yankewar. Amma sai ta tsiri kankarewa, zuciyar Inna ta hau ba tare da Iyah ta ankaraba, kawai ta ji saukar duka da mafici a zabure ta mike tana dire-diren shagwaba tana cewa, "Me na yi kuma na duka Inna?"

Dakuwa ta mata da hannunta na dama tare da cewa, "Za ki wuce ki dauko mayafinki ko kuwa?"

Ta shige dakinta tana cewa "Daga zuwansa zan debi jiki na fita, ba jan aji ba komai, salon ya ga arhata."

Mahaifiyarta bin ta yi da kallo, jiki a sanyaye ta rasa bakin magana, ta shiga dakinta ta fito da lemon kwalba guda biyu, da Swan roba biyu, da tuni Baffa ya tanada saboda zuwansa, ta zuba mata a kan faranti mai kyau ta ajiye.

Kan dole ta bi ta dakin a zaune ta same ta ta sake gyara fuskar ta yi kyau sosai ga mayafin da ya dace da zaren surfanin dake jikin rigar, kamshin tsadadden turaren Escada sai tashi yake a dukkan dakin! Sassautawa ta yi ta ce, "Yanzu zama ki ka sake yi Iyah? ko ba komai ai malaminki ne, malami kuwa ai kamar uba ne, ki duba fa tsawon lokacin da kika shanya shi yana faman jiran ki?"

Bata ce komai ba ta mi'ke ta fice ta dauki tabarma, ganin ruwa da lemo a kusa da tabarmar yasa ta ganewar iyayenta sun fi ta kambama lamarin MK.
Chapter 21 · 0% Book details