Sashe 27
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Farincikinsa ya karu ya hau fadin, "In Sha Allah ba za ki yi nadamar zabe na a matsayin mijin aurenki ba."
Shauki ya debe su ba su ankara ba har aka fara kiran sallah sannan ya tafi yana cewa, "Duk yadda muka yi da Baffa za ki ji."
Alkalamin
*SURAYYA DAHIRU*
✍️✍️.
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*
*A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
*TALLAH*!
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._
41-42
A Daren ranar Baffa ya sake zaunar da Sa'adah tare da mahaifiyarta, ya ce "Ina sane na bar ki kina sauraran wasu bayan Mutari.
Saboda na ba ki damar da shari'a ta ba ki, na kar na aurar da ke bisa dole, duk da shari'ar tace ni na fi cancanta na zaba miki mijin aure kasancewar ki budurwa.
Amma tunda muna wani irin zamani da 'ya'ya suke ganin sun fi iyayensu sanin abin da ya dace da su, ya sa na ba ki damarki, na sha fada miki aure zan miki, ba kuma zan miki auran dole ba, sai dai na dora ki akan shawara mai kyau. Alhamdulillah lokaci ya yi, don haka ki fada mini a cikin masu zuwa wajenki wa kika zaba? Ina son ya turo mini magabatansa a tsayar da magana guda daya."
Ta yi shiru kanta na kasa, Inna ce ta tanka , "Ai na ga alamar sun daidaita da Muutar din."
Hannu Baffa ya daga mata alamun ta yi shiru, ya bude murya ya ce, "Iyah tsakanin Alhaji Mamman da Mutari wa kike so?"
Ta sake yin shiru, ya nisa ya ce, "Dole fa ki yi mini magana saboda duk hukuncin da zan yanke, ya kasance da yardar ki, ba na so daga baya ki ba ni matsala, kwanakin baya da Alhaji Mamman ya same ni ban ba shi amanna ba, amma na ce ya nemi yardar ki, saboda shi ma mutumin kirki ne, ya samu yabo a wurin mutanen da suke kewaye da shi. Yanzu kuma lokaci ya yi da zan sallami daya a cikinsu."
Inna da ta ke sauraran su ta ji tamkar ta ce Alh Mamman zai sallama amma ta yi shiru saboda bai ba ta damar yin magana ba.
Ya sake kiran ta a karo na biyu, "Iyah!"
Ta amsa murya a dakushe. "Wa zan sallama a tsakaninsu? Ko kuma dukkansu ba ku shirya ba?"
Ta jima kafin ta bude baki ta ce, "Dazu Inna ta fada ai."
Da'di ya kama dukkansu, ya ce, "Kina nufi da Mutari ku ka shirya?"
Kai ta sake yin kasa da shi ba tare da ta amsa ba, Inna ce ta yi fit ta ce "Ka san ba za ta iya amsawa ba, amma na lura da Muutar ne za'binta."
"ALHAMDULILLAH!" Baffa ya furta a fili. Ya zarce da fadin, "Shike nan da kaina zan ba wa Alhaji Mamman hakuri, Allah Ya sanya alkhairi a tsakaninku, ki yi ko yi da uwarki wurin biyayya, Allah Ya tabbatar da alherin da muke zaton sa tsakaninki da yaron nan."
Da haka ya sallame ta wanda da kyar ta iya tashi.
Washegari kuwa bayan La'asar MK ya samu Baffa, zatonsa ya tabbata domin kuwa maganar turo magabatansa ya yi bayan ya tabbatar masa ya yi magana da Sa'adah ta ce shi ne zabinta. Godiya sosai MK ya yi tare da cewa, "Za su zo ba da jimawa ba."
Baffa ya nisa ya ce, "Ka yi shirinka a hankali sannan zan fada maka ni ba a kawo mini lefe sannan ni ma bana yin kayan daki, don haka ka shirya dakin da za ka ajiye ta da iya abin da za ka iya, ni ma zan hado ta da yan tarkacen da zan iya.
Daurin aure kawai za a yi sai kuma uwarta za ta dan yi taron mata a gida, zuwa yammaci da kaina zan kai ta dakinta, Ban yarda da wani taron maza da mata da sunan fati ko wani abu na daban ba! Idan kun tare kuna da ra'ayi, da damar yin walima wannan sunna ce sai ku yi. idan har wannan tsarin ya yi, akan hakan za ka turo mini magabatanka, Saboda idan sun zo, zan sanar da su."
Godiya sosai Mk ya sake yi tare da fadin, "In Sha Allah yadda duk ka ce haka zan yi Baffa, na gode sosai da karamci Allah ya saka da alheri."
Da haka suka rabu MK na jinjina halin wannan dattijon, ko irin su nawa ne suka yi saura a cikin al'ummar mu?
Gefe guda kuma tunanin yadda Sa'adah za ta karbi lamarin yake yi, ko ya ya za ta ji idan aka ce ba za a yi mata lefe ba? Sannan ya za ta yi idan ta gane cewa ita ma haka za a kai ta ba kayan daki, ba biki irin na zamani?😁
Da kansa ya ji dariya ta kufce masa haka ya samu gefe ya yi dariyarsa mai yawa, sai da ya gama a fili ya ce, "Sa'adah big girl ba lefe!" 😁
MK shiru ya yi bai fada wa Sa'adah tsarin Baffa ba, bai san mai yasa yake jin tsoron fada mata ba, ya ja bakinsa ya tsuke, ta ji maganar a bakin wanda ya tsara lamarin.
Takanas 'yan uwan mahaifin MK, Baba Umaru, da Baba Idi, suka taho Kano suka hadu da Alhaji Isa, suka rankaya gidan su Sa'adatu nema wa MK auranta. Kai tsaye ya ce ya ba su sannan sadaki kawai za su kawo masa. Bai boye musu tsarinsa na rashin yin hidima ba.
Dukkansu, sun yi farinciki, sun kuma yi amanna da tsarinsa, suna fadin ai mu ma da ga yau za mu yi koyi da kai don mu sami sauki a cikin zamantakewarmu, sannan darajar aure za ta karu za a daina fargaban yin sa, saboda an kewaye shi da hidimomi masu wahalarwa.
Baffa ya sake cewa "Na baku wuka da nama duk lokacin yaron ya kammala shirinsa kusa ranar aure da kan ku, sai ku sanar da ni, ina kuma rokon ku fada masa iya abin da zai iya shi zai yi, fatana dai Ubangiji ya albarkaci auren."
Godiya sosai suka yi
suna yaba halin kwarai irin na mahaifin Sa'adah, suka jaddada masa ba da jimawa ba kuwa zai ji ranar da suke ganin ta dace da shirin MK, suka sake yi masa godiyar wannan girman da ya ba su. suka rabu cike da farinciki, a hanyar su ma tattauna karamcin da suka gani suke ta yi.
Alh Isa ya ce, "Ai ni tun zuwan da na yi a farko na gane Mukhtar ya nemo aure a gidan mutunci, sai dai mu yi fatan Allah ya zaunar da su lafiya."
Dukkan su, suka hada baki wurin fadin, "Ameen."
Baba Umaru ya nisa ya ce, "Saboda karamcin wannan Mutumin, bayan sadakin da zan biya wa Mutari har kudin da zai shirya wa yarinyar daki zan ba shi ya kara saboda iyayenta su san muma mun iya karamci."
Su Alh Isa su ma suka hau fadin, "Ai kuwa mu ma za mu sake sabon shiri."
Sai da suka je gidan su MK suka yi wa Hajiya Babba bayanin halin da ake ciki, sannan suka tafi.
Dukkan dangin MK sun karbi tsarin mahaifin Sa'adah, na ba zai yi kayan daki ba, musamman da bai nemi a ba shi wani kudi ba, illa ma lefen da ya ce su ma kar su yi.
Da daddare suna falon gidan gaba'dayansu har Hajiyar Bichi, kasancewar duk sun zo gidan saboda haihuwa da Sameera ta yi, yau kuma aka yi suna, shi ne suka zarto gidan su. Hafsatu ce kawai ba ta nan, saboda a Lagos take aure, Hajiya Babba ta sanar musu.
Ta kare maganar da cewa "Kayan da na fara tarawa na lefe kuwa tabbas zan ba ta, don da sunanta na ke sayan su."
Hayaniya ta cika falon na yadda suka ji dadin tsarin suka hau fadin, "Ai kuwa dai za mu dage mu yi kayan daki masu kyau."
Abbas ya dubi MK ya ce, "Amaryar taka tana da 'kanwa ne?"
Falo ya sake daukar hayaniya Akil ya ce, "Saboda ka ji ba lefe ba bidi'oi?"
Shi dai MK bai sa musu baki ba, suka yi shewarsu, suka gama. Haka ma Hajiyar Bichi uffan ba ta ce ba! Haj Babba ce da ragowan yaran suke ta dabdalarsu.
Kwanaki uku tsakanin zuwan iyayen MK, Alhaji Isa ya sake yin tattaki da kansa ya sanar da Baffa suna son a yi auren bayan karamar sallah watanni biyar masu zuwa. Bai musa ba ya ce, "Allah ya sa ranmu zai kai"
Baffa bai yi kasa a guiwa ba ya hakurkurtar da Alhaji Mamman, da ke ba yaro ba ne rabuwa aka yi irin ta salin alin, duk da bai so hakan ba, amma ya hakura, ya kuma roki Baffa ya ba shi damar ganinta, a karo na karshe. Baffah bai ki ba ya ce zai iya ganin ta. Maimakon ya jira a turo masa ita sai ya ce bari ya je ya dawo.
Shauki ya debe su ba su ankara ba har aka fara kiran sallah sannan ya tafi yana cewa, "Duk yadda muka yi da Baffa za ki ji."
Alkalamin
*SURAYYA DAHIRU*
✍️✍️.
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*
*A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
*TALLAH*!
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._
41-42
A Daren ranar Baffa ya sake zaunar da Sa'adah tare da mahaifiyarta, ya ce "Ina sane na bar ki kina sauraran wasu bayan Mutari.
Saboda na ba ki damar da shari'a ta ba ki, na kar na aurar da ke bisa dole, duk da shari'ar tace ni na fi cancanta na zaba miki mijin aure kasancewar ki budurwa.
Amma tunda muna wani irin zamani da 'ya'ya suke ganin sun fi iyayensu sanin abin da ya dace da su, ya sa na ba ki damarki, na sha fada miki aure zan miki, ba kuma zan miki auran dole ba, sai dai na dora ki akan shawara mai kyau. Alhamdulillah lokaci ya yi, don haka ki fada mini a cikin masu zuwa wajenki wa kika zaba? Ina son ya turo mini magabatansa a tsayar da magana guda daya."
Ta yi shiru kanta na kasa, Inna ce ta tanka , "Ai na ga alamar sun daidaita da Muutar din."
Hannu Baffa ya daga mata alamun ta yi shiru, ya bude murya ya ce, "Iyah tsakanin Alhaji Mamman da Mutari wa kike so?"
Ta sake yin shiru, ya nisa ya ce, "Dole fa ki yi mini magana saboda duk hukuncin da zan yanke, ya kasance da yardar ki, ba na so daga baya ki ba ni matsala, kwanakin baya da Alhaji Mamman ya same ni ban ba shi amanna ba, amma na ce ya nemi yardar ki, saboda shi ma mutumin kirki ne, ya samu yabo a wurin mutanen da suke kewaye da shi. Yanzu kuma lokaci ya yi da zan sallami daya a cikinsu."
Inna da ta ke sauraran su ta ji tamkar ta ce Alh Mamman zai sallama amma ta yi shiru saboda bai ba ta damar yin magana ba.
Ya sake kiran ta a karo na biyu, "Iyah!"
Ta amsa murya a dakushe. "Wa zan sallama a tsakaninsu? Ko kuma dukkansu ba ku shirya ba?"
Ta jima kafin ta bude baki ta ce, "Dazu Inna ta fada ai."
Da'di ya kama dukkansu, ya ce, "Kina nufi da Mutari ku ka shirya?"
Kai ta sake yin kasa da shi ba tare da ta amsa ba, Inna ce ta yi fit ta ce "Ka san ba za ta iya amsawa ba, amma na lura da Muutar ne za'binta."
"ALHAMDULILLAH!" Baffa ya furta a fili. Ya zarce da fadin, "Shike nan da kaina zan ba wa Alhaji Mamman hakuri, Allah Ya sanya alkhairi a tsakaninku, ki yi ko yi da uwarki wurin biyayya, Allah Ya tabbatar da alherin da muke zaton sa tsakaninki da yaron nan."
Da haka ya sallame ta wanda da kyar ta iya tashi.
Washegari kuwa bayan La'asar MK ya samu Baffa, zatonsa ya tabbata domin kuwa maganar turo magabatansa ya yi bayan ya tabbatar masa ya yi magana da Sa'adah ta ce shi ne zabinta. Godiya sosai MK ya yi tare da cewa, "Za su zo ba da jimawa ba."
Baffa ya nisa ya ce, "Ka yi shirinka a hankali sannan zan fada maka ni ba a kawo mini lefe sannan ni ma bana yin kayan daki, don haka ka shirya dakin da za ka ajiye ta da iya abin da za ka iya, ni ma zan hado ta da yan tarkacen da zan iya.
Daurin aure kawai za a yi sai kuma uwarta za ta dan yi taron mata a gida, zuwa yammaci da kaina zan kai ta dakinta, Ban yarda da wani taron maza da mata da sunan fati ko wani abu na daban ba! Idan kun tare kuna da ra'ayi, da damar yin walima wannan sunna ce sai ku yi. idan har wannan tsarin ya yi, akan hakan za ka turo mini magabatanka, Saboda idan sun zo, zan sanar da su."
Godiya sosai Mk ya sake yi tare da fadin, "In Sha Allah yadda duk ka ce haka zan yi Baffa, na gode sosai da karamci Allah ya saka da alheri."
Da haka suka rabu MK na jinjina halin wannan dattijon, ko irin su nawa ne suka yi saura a cikin al'ummar mu?
Gefe guda kuma tunanin yadda Sa'adah za ta karbi lamarin yake yi, ko ya ya za ta ji idan aka ce ba za a yi mata lefe ba? Sannan ya za ta yi idan ta gane cewa ita ma haka za a kai ta ba kayan daki, ba biki irin na zamani?😁
Da kansa ya ji dariya ta kufce masa haka ya samu gefe ya yi dariyarsa mai yawa, sai da ya gama a fili ya ce, "Sa'adah big girl ba lefe!" 😁
MK shiru ya yi bai fada wa Sa'adah tsarin Baffa ba, bai san mai yasa yake jin tsoron fada mata ba, ya ja bakinsa ya tsuke, ta ji maganar a bakin wanda ya tsara lamarin.
Takanas 'yan uwan mahaifin MK, Baba Umaru, da Baba Idi, suka taho Kano suka hadu da Alhaji Isa, suka rankaya gidan su Sa'adatu nema wa MK auranta. Kai tsaye ya ce ya ba su sannan sadaki kawai za su kawo masa. Bai boye musu tsarinsa na rashin yin hidima ba.
Dukkansu, sun yi farinciki, sun kuma yi amanna da tsarinsa, suna fadin ai mu ma da ga yau za mu yi koyi da kai don mu sami sauki a cikin zamantakewarmu, sannan darajar aure za ta karu za a daina fargaban yin sa, saboda an kewaye shi da hidimomi masu wahalarwa.
Baffa ya sake cewa "Na baku wuka da nama duk lokacin yaron ya kammala shirinsa kusa ranar aure da kan ku, sai ku sanar da ni, ina kuma rokon ku fada masa iya abin da zai iya shi zai yi, fatana dai Ubangiji ya albarkaci auren."
Godiya sosai suka yi
suna yaba halin kwarai irin na mahaifin Sa'adah, suka jaddada masa ba da jimawa ba kuwa zai ji ranar da suke ganin ta dace da shirin MK, suka sake yi masa godiyar wannan girman da ya ba su. suka rabu cike da farinciki, a hanyar su ma tattauna karamcin da suka gani suke ta yi.
Alh Isa ya ce, "Ai ni tun zuwan da na yi a farko na gane Mukhtar ya nemo aure a gidan mutunci, sai dai mu yi fatan Allah ya zaunar da su lafiya."
Dukkan su, suka hada baki wurin fadin, "Ameen."
Baba Umaru ya nisa ya ce, "Saboda karamcin wannan Mutumin, bayan sadakin da zan biya wa Mutari har kudin da zai shirya wa yarinyar daki zan ba shi ya kara saboda iyayenta su san muma mun iya karamci."
Su Alh Isa su ma suka hau fadin, "Ai kuwa mu ma za mu sake sabon shiri."
Sai da suka je gidan su MK suka yi wa Hajiya Babba bayanin halin da ake ciki, sannan suka tafi.
Dukkan dangin MK sun karbi tsarin mahaifin Sa'adah, na ba zai yi kayan daki ba, musamman da bai nemi a ba shi wani kudi ba, illa ma lefen da ya ce su ma kar su yi.
Da daddare suna falon gidan gaba'dayansu har Hajiyar Bichi, kasancewar duk sun zo gidan saboda haihuwa da Sameera ta yi, yau kuma aka yi suna, shi ne suka zarto gidan su. Hafsatu ce kawai ba ta nan, saboda a Lagos take aure, Hajiya Babba ta sanar musu.
Ta kare maganar da cewa "Kayan da na fara tarawa na lefe kuwa tabbas zan ba ta, don da sunanta na ke sayan su."
Hayaniya ta cika falon na yadda suka ji dadin tsarin suka hau fadin, "Ai kuwa dai za mu dage mu yi kayan daki masu kyau."
Abbas ya dubi MK ya ce, "Amaryar taka tana da 'kanwa ne?"
Falo ya sake daukar hayaniya Akil ya ce, "Saboda ka ji ba lefe ba bidi'oi?"
Shi dai MK bai sa musu baki ba, suka yi shewarsu, suka gama. Haka ma Hajiyar Bichi uffan ba ta ce ba! Haj Babba ce da ragowan yaran suke ta dabdalarsu.
Kwanaki uku tsakanin zuwan iyayen MK, Alhaji Isa ya sake yin tattaki da kansa ya sanar da Baffa suna son a yi auren bayan karamar sallah watanni biyar masu zuwa. Bai musa ba ya ce, "Allah ya sa ranmu zai kai"
Baffa bai yi kasa a guiwa ba ya hakurkurtar da Alhaji Mamman, da ke ba yaro ba ne rabuwa aka yi irin ta salin alin, duk da bai so hakan ba, amma ya hakura, ya kuma roki Baffa ya ba shi damar ganinta, a karo na karshe. Baffah bai ki ba ya ce zai iya ganin ta. Maimakon ya jira a turo masa ita sai ya ce bari ya je ya dawo.