← Book details Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 2 OF 113

Sashe 2

Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da gudu ya cim mata ta baya ya rungeme ta yana fadin,

"Am sorry Mami, very sorry!"

"Ai ni kuma ba ruwana da kai Jawad, tun da dai kai ba ka jin magana, na hana ka wannan manyancen naka, na hana ka shiga abin da bai shafe ka ba, amma ka 'ki, to ka je ka yi ta yi."

Ya marairaice yana ba ta ha'kuri har dai ya samu ta ha'kura ya ga murmushinta.

Malam yana zaune yana kallon su har suka ba ce ma ganinsa, a ransa yana mugun tausaya wa Jawad, tun da shi burinsa a ce Mamansa na tare da su, wadda faruwar hakan sai ikon Allah.

Yana zaune, ya dawo ya tarar da shi yana ta tunani, "Ni ma ai zuwa zan yi na tafi. Mu je mota ka kwaso kayanka."

Daidai lokacin wayarsa ta dauki ruri, yana dubawa yaga matarsa ce Farida ya amsa, tambayar Jawad ta yi, wayar ya mi'ka ma yaron tare da cewa, "Karbi!"

Ba wani karsashi ya karbi wayar har ita ma ta ji babu dadi tana tambayar shi ko lafiya ya ce mata, "Lafiya lau!" Bana son Malam ya tafi ya tafi nee, sannan baku zo ba ke da Hajiyan Bichi".
ta shiga bashi hakuri cike da murna ganin ya fara dawo mata tamkar farkon zamansu.

Suna tafe yana masa nasiha tare da nuna masa ba ayina uwa ba a yin musu da ita, dole a bi ta yadda take so, sannan ya daina shiga matsalar da ba tashi ba, hawaye yake gogewa tare da cewa,

"Ni dai Malam ka dawo da ita gidanmu ni ma in dinga ganin Mamana a gidanmu, kamar yadda nake ganin na friends dina, kowa Mamansa da Babansa tare suke zuwa masa amma banda ni!"

Ya 'karasa cikin kuka sosai, janyo shi jikinsa ya yi yana dan bubbuga bayansa alamun rarrashi yana cewa
"Ina ce ni ma tare da Antinka nake zuwa maka?"

"Amma ai ba da Mamana kuke zuwa ba!"

"To ka kwantar da hankalinka, ka dinga mana adddu'a sai ka ga very soon ta dawo har ma ka zama Yaya Jawad kana so?"

Ya daga kansa tare da sa hannu yana goge hawayen da ya'ki tsayawa.

"To in dai kana son haka, ka daina damuwa ka kuma daina yiwa Mami maganar bare ta dake ka, kawai addu'a za ka na yi, ni kuma ka dinga tuna mini, wataran sai dai ka dawo hutu ka ganta a gidanmu."

"Malam da gaske?" ya tambaya cike da zumudi.

"E Mana indai ka daina kuka, ka daina damuwa, ka daina damunta, kana addu'a to ina tabbatar maka ba abin da ya fi addu'a juya lamura!"

Murmushi ya shiga yi yana goge hawaye da handkerchief din hannunsa yana 'fadin,
"Ai ko Malam ban san murnar da zan yi ba,, kuma har da kai zan 'dauka a jirgin nawa".

Dariya Mk ya yi tare da cewa "Ai kuwa dai nima naji dadi tunda albakacin Mami zan shiga jirgin Jawad"
Kunya ta kama yaron yace "Ai dan ita bata taba shiga bane"

Ya sake cewa, "Malam ka gai da Hajiya, kuma ina zuba idon zuwanta, tunda ba ta zo yau ba, ina bin ta bashi!"

Alkalamin
Surayya Dahiru ✍️
[5/11, 17:15] ~fatieshak🌹: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/

*Tukuici ga*
*FADILA LAMIDO*
*BINTA UMAR ABBALE*
*ZAINAB MAZAWAJE*

*Nagode da Shawarwarinku da 'karfafa guiwa, Allah Ya saka muku da alheri, Ya 'kara daukaka.*

*GODIYA GA MAKARANTA*
*Na gode da yadda kuka 'karbin wannan labarin, ha'kika jiya na ga ruwan masoya, ban yi zaton a 'kankanin lokaci littafin zai 'karade duniyar karatu haka ba, na gode muku sosai, in sha Allah ba za ku yi NADAMAR bibiyar wannan labarin ba!Heart U all*

3-4

A sanyaye ya fito wa da Jawad kayayyakin provisions din da ya kawo mishi, tamkar wanda zai yi rabin shekara bai je gida ba, yana sake jaddada mishi ya daina damuwa ya kuma ci gaba da karatunshi.

Ya shiga mota Jawad na 'daga mishi hannu har ya fice, bai yi nisa sosai ba don kuwa bai gama barin garin Kiyawa ba, ya hango su Sa'adah da wasu matan a waje, gefe kuma an bude motar bakanike sai tabe-tabe yake, ga dukkan alamu motar ce ta lalace musu, kamar ya wuce sai kuma ya kasa.

Don haka sai ya tsaya a gabansu, bai fito ba, sai ya lalubo lambar da Jawad ya kira shi da ita dazu, ya san tabbas layinta ne duk kuwa da ba ainihin layin ta ba ne daya santa da shi.

Ya danna alamar kira, yana hango ta tana ta kici-kici da jakarta wurin lalubo wayar, amma abin mamaki ya ga ta fito da wayar amma ba ta dauka ba har ta katse, mamaki ya kama shi wai yaushe Sa'adah ta ko yi jarumta akan lamarinsa ne?
Ya yi jim yana tunanin rabon da Sa'adah ta shiga harkarsa, ba shakka ba lokaci ne Mai tsayi, ba ta sake neman shi ba, ba ta sake duba dukkan lamarin sa ba, ta yi fatali da shi da dukkan soyayyarshi, abin da ya dade yana mamakinsa. bai daddaraba, ya sake 'kira tana gab da tsinkewa ta daga ba ta yi magana ba, amma dai ta kara a kunnen ta, sanin halinta da ya yi na ba za ta fara magana ba, yasa shi cewa,

"Ke na gani a titi a na muku gyaran mota?".

Cikin rashin nuna damuwa ta ce "A a ba ni ba ce."

Bai yi mamakin amsarta ba ya ce. "Amma ba ke ce nake hangowa a tsaye kina amsa wayar nan daidai jikin Alheri bread🍞 ba?"

Shiru ta masa sai ji ya yi ta ma ka'tse wayar gaba'daya.

Shiru ya yi ranshi na suya ya na sake jaddada halayyarta a jininta ne ba za ta sauya ba.

Har ya ta da motar da niyyar barin wajen ta je ta 'karata, sai kuma ya tuna uwar Jawad ce tilon 'dansa, ya tabbatar da tare yake da Jawad din, ba zai yarda su tafi su bar Maminshi a bayan gari jejin Allah ba, ga yamma ta yi likis sosai, sanyin da ake 'dan busawa ya sake taimaka wa garin ya yi dan duhu, don haka sai ya fito bayan ya kulle motar ya nufe su.

Yana zuwa ya ga har da Zainab Ma'aji da wasu mata biyu da bai gane su ba.

Ita ko Zainab tana ganin shi ta saki fuska."Lah! Uncle kai ne ashe."

Ta gaishe shi irin gaisuwar da dalibi ke yi idan ya ga malamin da ya koyar da shi a baya. Shi ma ya amsa da jin dadin girmama shi da Zainab ke yi tun fil azal.

Hannu ya mi'ka ya dauki yaronta Walid ya masa wasa sannan ya ce, "Motar taku lalacewa ta yi ne?".

"E wallahi ga mu nan dai ana ta faman gyara".

"To ku zo mana mu wuce tun da ba tabbacin za ta gyaru yanzu".

Kallo ta kai ga Sa'adah da ta koma baya ta yi kamar ba ta gan shi ba, ta kuma cika ta yi fam kamar kububuwa.

Zainab ta ce "To uncle bari na yi wa abokan tafiyar tamu magana."

"Okay"
Kawai ya ce, yana ci gaba da wasa da Walid dake ta bingila mishi dariya tamkar ya san shi.

Bayani Zainab ta musu kamar yadda ya bu'kata, dukkan su sun amince, su bi shi, amma ban da Sa'ada. Don haka Zainab da 'yan uwanta su ma suka janye tun da dai ai sun san saboda ita ya tsaya har ya nemi ya taimake su, to kuwa ta ya ya za su ce za su bi shi alhalin ita ta yi rantsuwar gara ta kwana a nan da ta shiga motarsa!

A matu'kar kunyace Zainab take ba shi ha'kuri tare da ba shi uzirin direban ba zai ji dadi ba, ya san sarai Sa'ada ce ta'ki amincewa, amma sai ya ce ai zan sallame shi ku zo mu tafi kawai.

Nan ma sai ta sake dora wa 'yan uwanta laifi akan yayarsu tace ba zasu sab'awa direban al'kawari ba. Ya jinjina hankali da Zainab ke da shi, duk da ya san 'kawar ta ce ta'ki amincewa, amma ba ta fadi hakan ba, sai kariya take ta bayarwa, ina ma tun farko Sa'ada ita ta ri'ka a matsayin 'kawa, ba bara gurbi irin su Halima da Safina ba?

Wanda 'kawacenta da su bai amfane ta da komi ba sai muguwar asara da nadama, tunda sun mata ingiza mai kantu ta yarda har ta tsinke igiyar aurenta, a yanzu kuma sun bar ta sun koma suna zunden ta.

Don haka sai yace "To shi kenan ba damuwa ya matsa ga bakaniken dake ta iyakar kokarin shi don ya ga motar ta tashi.

magana suke yi da direba, cikin ikon Allah ba a wani dauki lokaci sosai ba motar ta gyaru, amma har an yi sallar Maghriba, dan haka malam da direban suka yi jam'i suka yi sallarsu, yayin da matan suka shiga wani kewaye su ka yi ta su.

Bai yarda ya tafi ba sai da ya ga tashin su sannan ya taka ya isa inda motarsa take shi ma ya bi su a baya.

A cikin motar kuwa yayyen Zainab sai caccakar Sa'ada suke da rashin kirkinta, "A haka kike son komawa gidan nasa? Ba kya girmama shi, a gaban kowa za ki iya keta shi?"

Cikin turo baki ta ce "Ni fa Anty da ne na yi haukan banza na son sai ya mayar da ni, yanzu kuwa ko ni da shi muka rage ba na sonsa ba zan koma ba"

Cikin fushi ita ma Anty Asiya wadda ita Zainab ke bi, kuma da ita duk a ka yi gwagwarmayar su Sa'adah, ta ce, "Ai shima ba son naki yake ba, shashasha da ba ta san me ya kamata ba."

Dattijon dake jan motar ya ce, "Um'um fa! Ba'a shiga lamarin mace da namiji, ai koni da yau na fara ganin su na hango soyayyarta mai yawa a idonsa da gangar jikinsa, ita ma kuma duk wannan kumburin da take yi da fiffi'ka duk soyayyar ce, da alama dai kishi ne ke dawainiya da ita a kansa, dan na ga fishi take mai tsanani da shi!"

Dukkan motar a kasa dariya a na cewa Baba ashe duk ka gano su?
Chapter 2 · 0% Book details