Sashe 17
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da 'kyar ta bude baki ta gaishe shi, ya amsa yana nazarin yadda ta zabge lokaci guda.
Kai tsaye ya ce, "Mai ya hana ki zuwa makaranta tsawon sati guda?"
Shiru ta yi amma a zuciyarta fadi take na bar muku makarantar sai ku tabbata kai da Farida da sauran staff masu shaidar zur, har Mahdi ya bayyana.
Sau biyu yana tambayar ta, ba ta 'dago kanta ba, bare ta amsa mishi. A karo na uku ya yi magana a kausashe tare da cewa "I will not repeat myself!"
Cikin turo baki ta ce "Ni ban son makarantar ne na gaji"
Mamaki ya kama shi wacce irin yarinya ce wannan? Ka zo shekarar 'karshe a karatunka kuma rana daya ka ce wai ka gaji?
Ya zuba mata ido yana nazarinta matsakaicin tsayi gare ta, ba'ka ce amma ba sosai ba, irin su ake cewa wankan tarwa'da, zagayayyiyar fuska ce da ita, mai dauke da manyan idanuwa dara-dara, gashin girar ta a cike, sannan hancinta ya dace da fuskar sai dan 'karamin baki irin na Baby Girl🤩, mai dauke da wushiryar da take 'kawata murmushinta, ga ta kuma da dimples a dukkan kumatunta ko motsa bakin ta yi sai sun lotsa, ba siririya ce ba amma kuma bata da jiki na sosai, sai dai a cike take, 'kasanta ne mai fadi, amma ta sama a tsuke take musamman da ta yi sa'a ba ta da tumbi sai hakan ya taimaka wurin fito da cikakkiyar sura mai birgewa. Shi yasa uniform ke mata kyau tunda sai sun mishi shape sannan kuma hijabin su 'dan mitsil ne.
Ya nisa yana kokawa da zuciyarshi, ya ce, "Ban gane kin gaji ba"?
Shiru ta yi ba ta ce 'kala ba.
Ganin yadda ta rame ya san dole akwai wani abu daya sata wannan borin sai ya tausasa murya ya ce,
"Sa'adah what's your problem, mai yasa haka? Ba za ki ji tausayin iyayenki ba, duk wahalar da suka yi sai da abu ya zo gaf, kice ke ba za ki yi ba, ko auran kike so wata nawa ya rage ki kammala sai a miki"
Wani malolon ba'kin ciki ya tokare mata wuya, tasan Baffa ne ya ce mishi haka, ta kasa magana amma ranta in ya kai dubu to ya baci.
Sai shi ne ya gaji da shirun ya ce, "Tunda gajiya ce kawai dalilinki ai yanzu kin huta tunda kin fi sati kina hutawa, kuma gobe Monday lallai ki shirya ki zo makaranta.
Kai tsaye ta ce, "Idan har FGC ne sai dai a kai gawata!"
Ta fada kuka na kwace mata, ta sunkuyar da kai tana danne kukan.
Shiru ya yi tare da tunanin dalilin 'kin makarantar haka farat 'daya, murya ba amo ya ce "Listen, idan aka canja miki wata makarantar za ki je"?
Kai ta 'daga mishi.
Ya ce "it's ok but let's talk the reality. Fada mini dalilinki na son barin makarantar ni kuma idan na ji kina da hujja da kaina zan nemo miki wata makarantar na kawo wa Baffa"
Ta yi shiru sai shesshe'kar kuka take yi, jikinsa ya yi sanyi zuciyarsa sai kisima mishi abubuwa take yi.
Ya dade yana lallashinta da kalmomi masu dad'i har ya samu ta bude baki ta ce, "Akan me zata dinga tsokana ta sannan duk a hadu a ba ni rashin gaskiya? Saboda ita Babanta mai kudi ne, ni kuma nawa talaka? Saboda ita mai haza'ka ce, ni kuma ba ita ba ce? Duk staff kowa ita ya gasgata! amma ni da nake yar class 'dinka, ka kasa kare mini hakkina, saboda ita Bebinka ce, ni kuma ka tsane ni? To na bar mata makarantar ta tabbata a ciki kar ta fita"
Mamaki ya yi matu'kar kama shi amma ganin ta hau dokin fushi mai yawa, sai ya tattaro dukkan alhini ya ya'ba a fuska da gangar jikinsa.
Ya kira ta, ta amsa ba tare da ta 'dago kanta ba, cikin muryar lallashi ya ce, " Have I ever said I hated you?"
Ta girgiza kai alamun a'a sai kuma ta ce. "No, but actions speak louder than words!"
A thick silence sweeps the atmosphere! Ya zama speechless, bai yi tunanin irin kallon da take masa ba kenan. Cike da ta'ajibi ya ce,
"Kar fa ki zama cikin jerin mutanen da idan an musu gyara yake zama gaba, tunda haka ne na miki al'kawarin ba zan sake shiga cikin case 'dinki ba, wannan bai kai dalilin da za ki bar karatu ba, sai dai idan da gaske auran kike so, ko kuma ba gaskiyar maganar kika fada mini ba."
Ta yi shiru ya ce, "Yanzu kin ha'kura za ki koma?"
"Amma ai cewa ka yi idan na fada maka dalilina za ka samo mini wata makarantar."
"E na fadi hakan! €amma nima sai da nace idan na ji kina da dalili, to ban gamsu da wannan dalilin ba."
Ta yi 'kasa da kanta,"Ai dama na san ba zaka mini adalci ba, tunda abin ya shafe ta."
Ido ya zuba matat kamar kishi take da Farida, amma kuma ai shi ba wacce ya ce yana so a cikinsu, daga Ubangiji sai shi sai zuciyarshi su kasan me yake ciki.
"Wai ta ina ta zama Bebina?"
Da sauri ta ce, "Saboda kullum bakinka baya gajiya da ambaton ta, duk fadin makarantar nan da ita kake misali, alhalin ba ita ce kawai daliba mai 'kwazo ba, sannan za ta tsokane ni, amma har da kai a masu gaskata ta, ni kuma a 'karyata ni" Ta fada cike da takaici kwarai da gaske.
Ya nisa, "To ai nace ba zan sake shiga case din ki ba"
Ya sake sassauta murya ya ce "Sa'adah!" Har cikin jikinta sai da 'kiran ya ratsa, jikinta ya yi sanyi, ya sake kiran a karo na biyu. "Sa'adah!"
Ba ta amsa ba amma ta dago ta zuba mishi manyan idanuwanta da sukayi ja saboda kuka.
"Idan na ce ke ce Bebin nawa fa?"
Da sauri ta yi 'kasa da kanta saboda yadda maganar ta dirar mata a ba zata! kuma yanayin sa ya matu'kar sa kunya ta kama ta.
"Ki dago ki amsa mini." Ya fada murya ba amo.
Ganin ta kasa magana, ya fara gaskata zarginsa na ita ma tana son sa, ya nisa tare da cewa. "Ban so na fada miki sirrin zuciyata yanzu ba, na so sai kin kammala karatunki, sai na zo na nemi aurenki a gidanku, amma ke na lura gaba'daya kallon wani 'dan ta'adda kike mini, idan za ki yarda da ni, ni ba son Farida nake yi ba, amma na san ina tausayin ta, sannan idan ke ba ki amince mini ba, to tabbas zan iya maye gurbinki da ita"
Wani takaicin ya sake kama ta akwai alamun tausayin nan zai iya rikidewa zuwa soyayya kamar yadda Zainab Ma'aji ta hasaso, abin da take ayyanawa a ranta ke nan.
Ya gaji da jiran amsarta ya ce, "Kin yi shiru?"
'Kasa ta sake yi da kanta cikin fushi ta amsa, "Tunda har za ka iya maye gurbina da ita, kawai ka ri'ke ta tun yanzu ai dama ita ce a ranka."
Ta fada murya na rawa.
"Wai ke kam wacce irin yarinya ce mai 'karyata na gaba da ita? Kin sa na fada miki sirrin zuciya ta, amma kina 'karyata ni. zan maimata miki a karon 'karshe, ke ce Bebina ba Farida ba, da gaske auren ki nake son yi, don nan ba gidan da zan yi wasa ba ne".
Ya mi'ke yana sa takalmi, yana ci gaba da fadin,
"Idan kin amince kin kuma gaskata ni, to lallai gobe na gan ki a makaranta, zan kuma fada miki wata magana. Rashin zuwan ki amsa ne na baki amince da soyayya ta ba, ba kuma ki gaskata ni ba, kin ga ba zancen ki ji ma maganar da zamu yi, zan tafi sai yadda hali ya yi ki gaida Inna!"
Ya juya ya fice.
Alkalamin
SURAYYA DAHIRU.
✍🏼✍🏼
[5/26, 20:33] Aminan Ibrahim: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺
•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*Dan Allah masu son Halin Yau! Daga farko, ku dinga tambaya a group, a kullum nakan turawa mutane daban daban sama da sau goma, nasan soyayyar labarin ne ta kawo hakan, amma abin yana mini yawa mussaman da kullum'kara yin nisa muke yi! Idan anturo ku dinga tarawa, idan antambaya ku yi sharing, yanzu aka fara, labari na gaba, JAZAKUMULLAHI KHAIR.*
*Comments din ku na sani nisha'di na gode sosai fans Allah ya fini yabawa*
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
29.
Ta jima zaune a gun, tana jin wani irin nisha'di tare da shauki yana ratsa zuciyarta da gangar jikinta gaba'daya, tana tuno yadda ya lankwashe murya yana fadin,
"Ke ce Bebina ba Farida ba"
Cike da farin-ciki ta na'de tabarma ta shiga gida, dakin Inna ta fara shiga ta shaida mata ta dawo sannan ta jigine mata tabarma inda ta dauka.
'Dakinta ta shiga, ta fara tattara uniform din da ba ta wanke su ba, ta fita tsakar gida ta hau wanki, hatta sandal sai da ta wanke ta shanya, tana gamawa ana kiran Maghrib. Koda Inna ta fito ta ga shanyar uniform uffan ba ta ce mata ba.
Sai da Baffa ya shigo bayan sallar Isha ta je ta durkusa gabansu, ta shaida musu gobe za ta je makaranta, Inna dai ba ta tanka ba, Baffa ne ya ce,
"Allah ya kai mu"
Ta dade a tsugunne tana jinta wani iri, ta san fushi suke da ita dukkansu musamman Inna. don haka sai ta sanyaya murya ta ce,
"Don Allah ku yi ha'kuri na san ban kyautata muku ba, na yi musu da ku, ku yi mini afuwa"
Ta fada cikin muryar kuka, kasancewar Baffa ya fi mata sassauci, shi ne ya fara tankawa da cewa,
"Ni ban san inda kika samo dabi'ar yin musu da iyaye ba Iyah? Ni da kaina na rarrashe ki akan wannan maganar kika kafe, kika nuna mini ni ne zan bi ki ba ke za ki bi ni ba".
Kai tsaye ya ce, "Mai ya hana ki zuwa makaranta tsawon sati guda?"
Shiru ta yi amma a zuciyarta fadi take na bar muku makarantar sai ku tabbata kai da Farida da sauran staff masu shaidar zur, har Mahdi ya bayyana.
Sau biyu yana tambayar ta, ba ta 'dago kanta ba, bare ta amsa mishi. A karo na uku ya yi magana a kausashe tare da cewa "I will not repeat myself!"
Cikin turo baki ta ce "Ni ban son makarantar ne na gaji"
Mamaki ya kama shi wacce irin yarinya ce wannan? Ka zo shekarar 'karshe a karatunka kuma rana daya ka ce wai ka gaji?
Ya zuba mata ido yana nazarinta matsakaicin tsayi gare ta, ba'ka ce amma ba sosai ba, irin su ake cewa wankan tarwa'da, zagayayyiyar fuska ce da ita, mai dauke da manyan idanuwa dara-dara, gashin girar ta a cike, sannan hancinta ya dace da fuskar sai dan 'karamin baki irin na Baby Girl🤩, mai dauke da wushiryar da take 'kawata murmushinta, ga ta kuma da dimples a dukkan kumatunta ko motsa bakin ta yi sai sun lotsa, ba siririya ce ba amma kuma bata da jiki na sosai, sai dai a cike take, 'kasanta ne mai fadi, amma ta sama a tsuke take musamman da ta yi sa'a ba ta da tumbi sai hakan ya taimaka wurin fito da cikakkiyar sura mai birgewa. Shi yasa uniform ke mata kyau tunda sai sun mishi shape sannan kuma hijabin su 'dan mitsil ne.
Ya nisa yana kokawa da zuciyarshi, ya ce, "Ban gane kin gaji ba"?
Shiru ta yi ba ta ce 'kala ba.
Ganin yadda ta rame ya san dole akwai wani abu daya sata wannan borin sai ya tausasa murya ya ce,
"Sa'adah what's your problem, mai yasa haka? Ba za ki ji tausayin iyayenki ba, duk wahalar da suka yi sai da abu ya zo gaf, kice ke ba za ki yi ba, ko auran kike so wata nawa ya rage ki kammala sai a miki"
Wani malolon ba'kin ciki ya tokare mata wuya, tasan Baffa ne ya ce mishi haka, ta kasa magana amma ranta in ya kai dubu to ya baci.
Sai shi ne ya gaji da shirun ya ce, "Tunda gajiya ce kawai dalilinki ai yanzu kin huta tunda kin fi sati kina hutawa, kuma gobe Monday lallai ki shirya ki zo makaranta.
Kai tsaye ta ce, "Idan har FGC ne sai dai a kai gawata!"
Ta fada kuka na kwace mata, ta sunkuyar da kai tana danne kukan.
Shiru ya yi tare da tunanin dalilin 'kin makarantar haka farat 'daya, murya ba amo ya ce "Listen, idan aka canja miki wata makarantar za ki je"?
Kai ta 'daga mishi.
Ya ce "it's ok but let's talk the reality. Fada mini dalilinki na son barin makarantar ni kuma idan na ji kina da hujja da kaina zan nemo miki wata makarantar na kawo wa Baffa"
Ta yi shiru sai shesshe'kar kuka take yi, jikinsa ya yi sanyi zuciyarsa sai kisima mishi abubuwa take yi.
Ya dade yana lallashinta da kalmomi masu dad'i har ya samu ta bude baki ta ce, "Akan me zata dinga tsokana ta sannan duk a hadu a ba ni rashin gaskiya? Saboda ita Babanta mai kudi ne, ni kuma nawa talaka? Saboda ita mai haza'ka ce, ni kuma ba ita ba ce? Duk staff kowa ita ya gasgata! amma ni da nake yar class 'dinka, ka kasa kare mini hakkina, saboda ita Bebinka ce, ni kuma ka tsane ni? To na bar mata makarantar ta tabbata a ciki kar ta fita"
Mamaki ya yi matu'kar kama shi amma ganin ta hau dokin fushi mai yawa, sai ya tattaro dukkan alhini ya ya'ba a fuska da gangar jikinsa.
Ya kira ta, ta amsa ba tare da ta 'dago kanta ba, cikin muryar lallashi ya ce, " Have I ever said I hated you?"
Ta girgiza kai alamun a'a sai kuma ta ce. "No, but actions speak louder than words!"
A thick silence sweeps the atmosphere! Ya zama speechless, bai yi tunanin irin kallon da take masa ba kenan. Cike da ta'ajibi ya ce,
"Kar fa ki zama cikin jerin mutanen da idan an musu gyara yake zama gaba, tunda haka ne na miki al'kawarin ba zan sake shiga cikin case 'dinki ba, wannan bai kai dalilin da za ki bar karatu ba, sai dai idan da gaske auran kike so, ko kuma ba gaskiyar maganar kika fada mini ba."
Ta yi shiru ya ce, "Yanzu kin ha'kura za ki koma?"
"Amma ai cewa ka yi idan na fada maka dalilina za ka samo mini wata makarantar."
"E na fadi hakan! €amma nima sai da nace idan na ji kina da dalili, to ban gamsu da wannan dalilin ba."
Ta yi 'kasa da kanta,"Ai dama na san ba zaka mini adalci ba, tunda abin ya shafe ta."
Ido ya zuba matat kamar kishi take da Farida, amma kuma ai shi ba wacce ya ce yana so a cikinsu, daga Ubangiji sai shi sai zuciyarshi su kasan me yake ciki.
"Wai ta ina ta zama Bebina?"
Da sauri ta ce, "Saboda kullum bakinka baya gajiya da ambaton ta, duk fadin makarantar nan da ita kake misali, alhalin ba ita ce kawai daliba mai 'kwazo ba, sannan za ta tsokane ni, amma har da kai a masu gaskata ta, ni kuma a 'karyata ni" Ta fada cike da takaici kwarai da gaske.
Ya nisa, "To ai nace ba zan sake shiga case din ki ba"
Ya sake sassauta murya ya ce "Sa'adah!" Har cikin jikinta sai da 'kiran ya ratsa, jikinta ya yi sanyi, ya sake kiran a karo na biyu. "Sa'adah!"
Ba ta amsa ba amma ta dago ta zuba mishi manyan idanuwanta da sukayi ja saboda kuka.
"Idan na ce ke ce Bebin nawa fa?"
Da sauri ta yi 'kasa da kanta saboda yadda maganar ta dirar mata a ba zata! kuma yanayin sa ya matu'kar sa kunya ta kama ta.
"Ki dago ki amsa mini." Ya fada murya ba amo.
Ganin ta kasa magana, ya fara gaskata zarginsa na ita ma tana son sa, ya nisa tare da cewa. "Ban so na fada miki sirrin zuciyata yanzu ba, na so sai kin kammala karatunki, sai na zo na nemi aurenki a gidanku, amma ke na lura gaba'daya kallon wani 'dan ta'adda kike mini, idan za ki yarda da ni, ni ba son Farida nake yi ba, amma na san ina tausayin ta, sannan idan ke ba ki amince mini ba, to tabbas zan iya maye gurbinki da ita"
Wani takaicin ya sake kama ta akwai alamun tausayin nan zai iya rikidewa zuwa soyayya kamar yadda Zainab Ma'aji ta hasaso, abin da take ayyanawa a ranta ke nan.
Ya gaji da jiran amsarta ya ce, "Kin yi shiru?"
'Kasa ta sake yi da kanta cikin fushi ta amsa, "Tunda har za ka iya maye gurbina da ita, kawai ka ri'ke ta tun yanzu ai dama ita ce a ranka."
Ta fada murya na rawa.
"Wai ke kam wacce irin yarinya ce mai 'karyata na gaba da ita? Kin sa na fada miki sirrin zuciya ta, amma kina 'karyata ni. zan maimata miki a karon 'karshe, ke ce Bebina ba Farida ba, da gaske auren ki nake son yi, don nan ba gidan da zan yi wasa ba ne".
Ya mi'ke yana sa takalmi, yana ci gaba da fadin,
"Idan kin amince kin kuma gaskata ni, to lallai gobe na gan ki a makaranta, zan kuma fada miki wata magana. Rashin zuwan ki amsa ne na baki amince da soyayya ta ba, ba kuma ki gaskata ni ba, kin ga ba zancen ki ji ma maganar da zamu yi, zan tafi sai yadda hali ya yi ki gaida Inna!"
Ya juya ya fice.
Alkalamin
SURAYYA DAHIRU.
✍🏼✍🏼
[5/26, 20:33] Aminan Ibrahim: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺
•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*Dan Allah masu son Halin Yau! Daga farko, ku dinga tambaya a group, a kullum nakan turawa mutane daban daban sama da sau goma, nasan soyayyar labarin ne ta kawo hakan, amma abin yana mini yawa mussaman da kullum'kara yin nisa muke yi! Idan anturo ku dinga tarawa, idan antambaya ku yi sharing, yanzu aka fara, labari na gaba, JAZAKUMULLAHI KHAIR.*
*Comments din ku na sani nisha'di na gode sosai fans Allah ya fini yabawa*
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
29.
Ta jima zaune a gun, tana jin wani irin nisha'di tare da shauki yana ratsa zuciyarta da gangar jikinta gaba'daya, tana tuno yadda ya lankwashe murya yana fadin,
"Ke ce Bebina ba Farida ba"
Cike da farin-ciki ta na'de tabarma ta shiga gida, dakin Inna ta fara shiga ta shaida mata ta dawo sannan ta jigine mata tabarma inda ta dauka.
'Dakinta ta shiga, ta fara tattara uniform din da ba ta wanke su ba, ta fita tsakar gida ta hau wanki, hatta sandal sai da ta wanke ta shanya, tana gamawa ana kiran Maghrib. Koda Inna ta fito ta ga shanyar uniform uffan ba ta ce mata ba.
Sai da Baffa ya shigo bayan sallar Isha ta je ta durkusa gabansu, ta shaida musu gobe za ta je makaranta, Inna dai ba ta tanka ba, Baffa ne ya ce,
"Allah ya kai mu"
Ta dade a tsugunne tana jinta wani iri, ta san fushi suke da ita dukkansu musamman Inna. don haka sai ta sanyaya murya ta ce,
"Don Allah ku yi ha'kuri na san ban kyautata muku ba, na yi musu da ku, ku yi mini afuwa"
Ta fada cikin muryar kuka, kasancewar Baffa ya fi mata sassauci, shi ne ya fara tankawa da cewa,
"Ni ban san inda kika samo dabi'ar yin musu da iyaye ba Iyah? Ni da kaina na rarrashe ki akan wannan maganar kika kafe, kika nuna mini ni ne zan bi ki ba ke za ki bi ni ba".