Sashe 89
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta turo baki ta ce " Ai son rai ne yasa shi fa'din hakan, ya san komai yake so ina taya shi son abin ina kuma girmama shi. Amma kai Baffa ne yake sonka ya daukaka lamarinka ya girmamaka. Yayin da kai baka sonsa kana amfani da shi ne dan cikar burinka da zarar ka samu, zaka iya ture komai ka kunyata shi, ka cusa masa takaicin da yake fakar idon mutane yana goge hawayen ba'kin cikin ka".
Idonta ya ciko da hawaye, ta shanye ta zarce da fadin " wannan karon wallahi har Baffan na shirya shayar da shi mamaki tunda baya kishina. Matu'kar Sharia ta damka mini zabin mijin aure a hannuna to ina tabbatar maka zan yi iyakacin yi na na dora hukuncin Sharia akan hukuncin Baffah. Ka rabu da ni, ka daina zuwa wurin ubana, kai ba 'dan-uwanmu bane, bamu da alakar komai da kai, akan me zaka zo ka dinga yi mini katsalandan a tsakanina da ubana, alhalin lokacin da ya kamata na shiga rigar uban nawa nuna mini ka yi bai isa ba, amma yanzu kana mini karfa karfar dole ka shiga rigarsa".
Jikin Mk ya yi sanyi kwarai da gaske ya ce "Allah dai ya so ba daga sama na fado ba Sa'adatu, kina yawan yi mini gorin bamu hada komai ba, na yarda bamu hada komai ba, amma Jawad ya hadamu, Baffa ai kakansa ne wannan hadin ai ya wuce ace na zama bare".
Ta kufulo ta ce "oh saboda Jawad kake mini wannan bibiyar, kake neman hada ni ya'ki da tsohona, to albishirinka, duk duniya uwace kawai ta san ainihin uban danta".
Wannan karon bai kai hannu jikinta da niyyar duka ba, amma ya yi matu'kar kidima, wani irin tashin hankali ya bayyana a fuskarsa da jikinsa, sai ta ganshi tamkar ranar da ya saketa.
Ya jingina da bango yana fa'din"Ya Hayyu ya QAYYUM bi Rahamatika astagisu".
Abin mamaki tausayinsa ya shigeta soasai, amma ta daure ta hadiye shi.
Ido jawur ya kalleta ya ce "Ki yiwa Allah da Ma'aiki ki fa'da mini mai zan yi ki daina jifana da irin wadannan kazaman kalaman da suke nufin tarwatsewata".
Yana rufe baki ta ce "ka daina shiga tsakanina da ubana saboda kai Baffa ya mini abin da har na mutu ba zan daina takaici ba, ba zan daina zubar da hawaye ba, ba dan darajar sa ta zarta komai a gurina ba, wallahi da ba zan yafe ba domin iyakacin cin fuska anyi mini, ba kuma dan komai ba sai dan ya faranta maka".
Ya tausasa murya ya ce " Fada mini abin da ya miki saboda ni, na miki al'kawarin idan na ji kina da hujja ba zan sake zuwa wajensa akan maganar ki ba, ke kawai zan tunkara, ke kuma ai sai kin amince".
Murya na rawa ta ce "kasan dai ai kusan sadakata Baffah ya baka, Nima nasan haka aka kai ni ba wata hidima, amma dai naje da gadona da kayayyakin amafanin da suka fi zama Dole. Na so a mini kayan daki da lefe kamar yadda ake yi a al'ada amma na yi hakuri na bi ra'ayinsa, dan samun albarka.
Bayan mun rabu na tattara komai da nake ganin kamaar lefe na ne, har da gold dina sai da ya nutse na sayi filaye da zummar idan hidimar iyayena ko aure ya zo mini a siyar ayi hidima, kawai Baffa ya je ya siyar mini ya baka kudin ka yi aure kana jin dadinka ni kuma ko na mutu ko na yi rai ko oho".
Wani irin kuka ya kwace mata, fiye da wadda ta yi a ranar rabuwarsu a mota, sosai take yinsa saboda yadda abin yake dafata.
Kukan da take yi ya wanke bacin ran da ta jefa shi a farko.
Tausayinta ya maye gurbin takaicin maganar da ta caba masa ya ce "Tabbas ba a miki adalci ba Sa'adatu, amma ki yi hakuri, na yarda kuma Baffah ya na sona, amma ko daya cikin goman son da yake miki ban samu ba. Da ciwo sosai, da gaske kuma na taya ki jin takaici, amma bari na tuna miki wasu abubuwa, Ni dai na da'de ban ga mai sa'a irinki ba, tabbas kin ci sunan ki na Sa'a".
Ya nisa ya ce da" kin san irin soyayyar da Baffah yake Miki da kin ji kunyar takaicin ya siyar da abinki ya bani na yi aure."
"Da kin san yadda Jawad yake son ki, yake fatana ya girma ya yi ku'di dan ya jiyar da ke da'di, da ba abin da sai sake damun ki na dai wani abu da ku'di zai iya siyansa."
"Da kin san yadda nake son ki, nake kwana nake tashi da ke, nake jin kin fi duniya da abin da yake cikinta da baki yi kishin auren Farida ba".
"Bari yau na fa'da miki gaskiyar magana ba dan ki yarda ki karbi soyayyata ba, sai dan ki gamsu iyakacin gaskiyar kenan, ina da yakinin ban ta'ba yi miki karyar da ban cancanci ki 'ki gasgata ni ba".
"Farida na cikin jerin matan da ubangiji ya kaddara mini zan aura. Rabuwarmu ta zama tilas Sa'adah domin itama kaddarata ce. Kin sani idan ina tare da ke wallahi duk yadda nake zage 'kwanjina akan ki, zai yi wahalar gaske na iya aure, bani da wannan 'kwarin guiwar saboda tsananin son da nake miki. To fa'da mini ta yaya zan auri Farida alhalin hakan ya zama dole, na farko mutuwa na iya kauda ke, na biyu kaddara ta rabamu, kinga da ki mutu ki barmu, ai gwara kadarar rabuwar tunda idan da rai ai da rabo".
Sannan Dan Allah bai isheki daraja ba ace ke ce kika biya sadakin kishiyarki, ke kuwa ni zan biya na ki, na tabbatar abin da Jawad yake yi miki a shekarunsa ya isa ki gane ubangiji yana tare da ke".
Jikinta ya yi sanyi ta san kalamansa duka ba karya, illah wadda ya ce ta fi duniya, da hakane ai da sai ya bari kaddarar ta kasheta in yaso shima ya zauna jiran wa'adinsa babu aure har ya mutu, su hadu a aljannah su sake rayuwar da babu bacin rai, amma yanzu ya gama curarta ya bari wannan makirar da take boye ainihin kalarta, ta san komai nasa, ta mallake shi, shine zai zo ya mata da'din bakin wai ta zarce duniya? kai namiji Hankaka ne tabbas.
Ganin ta yi lakwas sai ya ce "kin gamsu kin yarda?"
Ai kuwa tamkar wadda ya mareta har huci take yi ta ce "Wallahi ko shiga kunnuwana wai kana sona fiye da duniya bata yi ba, na dai yarda Baffah da Jawad na zarce komai a gunsu".
Ya fesar da zazzafar ajiyar zuciya ya ce "shikenan ba sai kin yarda ba. Ko ba kya sona mu komawa aurenmu, son da nake Miki, da wadda Jawad yake miki ya isa yasa ki rayu cikin farin-ciki".
Ta goge kwalla ta ce "har abada ba zan yi farin ciki a hannun ka ba, ka rufe idonka ka ce mini ina ha'intarka, ka rufe ido ka ce mini ana maka sharing dina"
Muryarta ta fara rawa tabbacin tsumin bacin rai ya taso, ta nisa ta ce "ka rufe idonka ka barni ka dauki wadda kasan na tsaneta saboda munafuncinta, ta faki idon mutane ta tsokane ni, amma sai ta layance a kuma bata gaskiya. Allah ne ya rufawa al'umma asiri ba karatun lauyanci ta yi ba, dan anga kwarewa wurin bada kariya ga karya".
Da 'kyar ya ce na janye kalamina, wallahi tashin hankali ne da kishinki, Amma nasan ha'inta dai babbar ha'inta ba zaki yi ba, na san ni ka'dai ne na muaamalance ki, na tabbatar da hakan har zuciyata".
Wani abu mai nauyi da ya danne kirjin Sa'adah shekaru uku ya fa'da mata sai dan saura.
Ta ce "to shikenan na yafe maka. Amma ka sani gaskiya ban da buri ko sha'awar auren mai mata kishi kashe ni zai yi, kawai ka barni na auri wadda zan sami nutsuwa, ka bar ni nima na dandana wani namijin kamar yadda ka ke dandana Balarabiyar Yemen".
A sanyaye ya ce "Sa'a ina jiye miki tsoron kar ki zama ajalina, domin kuwa banda lafiya, duk sadda na ganki sai kin yi mini fami a akan jinyar da nake yi".
Kai tsaye ta ce" Tunda bakin cikin ka bai mayar da ni gawa ba, na tabbatar kaima ba zaka zama ba".
Cikin gajiyawa ya ce "Next week Jawad zasu yi hutu, gaba'daya zai yi hutunsa a gurinki".
Maimakon ta ji dadi saboda ta san dan ya faranta mata ne yasa ya yanke wannan hukuncin, sai ta yi nufin gwasale shi.
Ta ce "bana bu'katar ganinsa ma bare ya mini hutu, inace saboda kar ya zo na zuga shi yasa ka kai shi makarantar kwana? Saboda kana son sai ya so Farida sama da ni yasa ka hana ya kwana a gidan nan sai dai ya zo ya yini? To shima na barka maka shi ban bu'katarsa, Ni kuwa a duniya me zaka mini na huce, ka zalunce ni iyaka".
Kafin ya yi magana sai ganin Innah suka yi, a ladabce Mk ya sunkuya ya gaishe ta, ta amsa babu yabo babu fallasa, daga gaisuwar bata ko tambayi Hajiyarsa ba bare matarsa, ta juya tana cewa "kin dora girki kin barshi zai kone, daga cewa zaki karbo sako?".
Wannan shagulatin bangaro da Inna ta yi masa ya matu'kar dukan zuciyar sa, yana ganin rashin nasarar sa a fili, Bai ga laifinta ba ko kadan, domin ya fahimci tana kan fahimtar su Baba Isa da Hajiyar Bichi ne. Wato Baffah ne kawai hoope dinsa.
Akwai gumurzu kenan dan kuwa sai inda karfinsa ya kare, yanzu ne zai yi dambar jefa alkalamin sa cikin Tawada. Domin ya ga maneman nata dukkansu basu da makusa, shine ma mai tarin kalubalen rashin samun goyan baya a wurin iyaye da Sa'adatu sa'ar Mata.
Surayya Dee
✍️✍️.
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
NA
*SURAYYA DAHIRU*.
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
*_Doka mai lamba ta 68 ta nuna cewa satar fasaha babban laifi ne da yake dai da satar Dukiya._*
Idonta ya ciko da hawaye, ta shanye ta zarce da fadin " wannan karon wallahi har Baffan na shirya shayar da shi mamaki tunda baya kishina. Matu'kar Sharia ta damka mini zabin mijin aure a hannuna to ina tabbatar maka zan yi iyakacin yi na na dora hukuncin Sharia akan hukuncin Baffah. Ka rabu da ni, ka daina zuwa wurin ubana, kai ba 'dan-uwanmu bane, bamu da alakar komai da kai, akan me zaka zo ka dinga yi mini katsalandan a tsakanina da ubana, alhalin lokacin da ya kamata na shiga rigar uban nawa nuna mini ka yi bai isa ba, amma yanzu kana mini karfa karfar dole ka shiga rigarsa".
Jikin Mk ya yi sanyi kwarai da gaske ya ce "Allah dai ya so ba daga sama na fado ba Sa'adatu, kina yawan yi mini gorin bamu hada komai ba, na yarda bamu hada komai ba, amma Jawad ya hadamu, Baffa ai kakansa ne wannan hadin ai ya wuce ace na zama bare".
Ta kufulo ta ce "oh saboda Jawad kake mini wannan bibiyar, kake neman hada ni ya'ki da tsohona, to albishirinka, duk duniya uwace kawai ta san ainihin uban danta".
Wannan karon bai kai hannu jikinta da niyyar duka ba, amma ya yi matu'kar kidima, wani irin tashin hankali ya bayyana a fuskarsa da jikinsa, sai ta ganshi tamkar ranar da ya saketa.
Ya jingina da bango yana fa'din"Ya Hayyu ya QAYYUM bi Rahamatika astagisu".
Abin mamaki tausayinsa ya shigeta soasai, amma ta daure ta hadiye shi.
Ido jawur ya kalleta ya ce "Ki yiwa Allah da Ma'aiki ki fa'da mini mai zan yi ki daina jifana da irin wadannan kazaman kalaman da suke nufin tarwatsewata".
Yana rufe baki ta ce "ka daina shiga tsakanina da ubana saboda kai Baffa ya mini abin da har na mutu ba zan daina takaici ba, ba zan daina zubar da hawaye ba, ba dan darajar sa ta zarta komai a gurina ba, wallahi da ba zan yafe ba domin iyakacin cin fuska anyi mini, ba kuma dan komai ba sai dan ya faranta maka".
Ya tausasa murya ya ce " Fada mini abin da ya miki saboda ni, na miki al'kawarin idan na ji kina da hujja ba zan sake zuwa wajensa akan maganar ki ba, ke kawai zan tunkara, ke kuma ai sai kin amince".
Murya na rawa ta ce "kasan dai ai kusan sadakata Baffah ya baka, Nima nasan haka aka kai ni ba wata hidima, amma dai naje da gadona da kayayyakin amafanin da suka fi zama Dole. Na so a mini kayan daki da lefe kamar yadda ake yi a al'ada amma na yi hakuri na bi ra'ayinsa, dan samun albarka.
Bayan mun rabu na tattara komai da nake ganin kamaar lefe na ne, har da gold dina sai da ya nutse na sayi filaye da zummar idan hidimar iyayena ko aure ya zo mini a siyar ayi hidima, kawai Baffa ya je ya siyar mini ya baka kudin ka yi aure kana jin dadinka ni kuma ko na mutu ko na yi rai ko oho".
Wani irin kuka ya kwace mata, fiye da wadda ta yi a ranar rabuwarsu a mota, sosai take yinsa saboda yadda abin yake dafata.
Kukan da take yi ya wanke bacin ran da ta jefa shi a farko.
Tausayinta ya maye gurbin takaicin maganar da ta caba masa ya ce "Tabbas ba a miki adalci ba Sa'adatu, amma ki yi hakuri, na yarda kuma Baffah ya na sona, amma ko daya cikin goman son da yake miki ban samu ba. Da ciwo sosai, da gaske kuma na taya ki jin takaici, amma bari na tuna miki wasu abubuwa, Ni dai na da'de ban ga mai sa'a irinki ba, tabbas kin ci sunan ki na Sa'a".
Ya nisa ya ce da" kin san irin soyayyar da Baffah yake Miki da kin ji kunyar takaicin ya siyar da abinki ya bani na yi aure."
"Da kin san yadda Jawad yake son ki, yake fatana ya girma ya yi ku'di dan ya jiyar da ke da'di, da ba abin da sai sake damun ki na dai wani abu da ku'di zai iya siyansa."
"Da kin san yadda nake son ki, nake kwana nake tashi da ke, nake jin kin fi duniya da abin da yake cikinta da baki yi kishin auren Farida ba".
"Bari yau na fa'da miki gaskiyar magana ba dan ki yarda ki karbi soyayyata ba, sai dan ki gamsu iyakacin gaskiyar kenan, ina da yakinin ban ta'ba yi miki karyar da ban cancanci ki 'ki gasgata ni ba".
"Farida na cikin jerin matan da ubangiji ya kaddara mini zan aura. Rabuwarmu ta zama tilas Sa'adah domin itama kaddarata ce. Kin sani idan ina tare da ke wallahi duk yadda nake zage 'kwanjina akan ki, zai yi wahalar gaske na iya aure, bani da wannan 'kwarin guiwar saboda tsananin son da nake miki. To fa'da mini ta yaya zan auri Farida alhalin hakan ya zama dole, na farko mutuwa na iya kauda ke, na biyu kaddara ta rabamu, kinga da ki mutu ki barmu, ai gwara kadarar rabuwar tunda idan da rai ai da rabo".
Sannan Dan Allah bai isheki daraja ba ace ke ce kika biya sadakin kishiyarki, ke kuwa ni zan biya na ki, na tabbatar abin da Jawad yake yi miki a shekarunsa ya isa ki gane ubangiji yana tare da ke".
Jikinta ya yi sanyi ta san kalamansa duka ba karya, illah wadda ya ce ta fi duniya, da hakane ai da sai ya bari kaddarar ta kasheta in yaso shima ya zauna jiran wa'adinsa babu aure har ya mutu, su hadu a aljannah su sake rayuwar da babu bacin rai, amma yanzu ya gama curarta ya bari wannan makirar da take boye ainihin kalarta, ta san komai nasa, ta mallake shi, shine zai zo ya mata da'din bakin wai ta zarce duniya? kai namiji Hankaka ne tabbas.
Ganin ta yi lakwas sai ya ce "kin gamsu kin yarda?"
Ai kuwa tamkar wadda ya mareta har huci take yi ta ce "Wallahi ko shiga kunnuwana wai kana sona fiye da duniya bata yi ba, na dai yarda Baffah da Jawad na zarce komai a gunsu".
Ya fesar da zazzafar ajiyar zuciya ya ce "shikenan ba sai kin yarda ba. Ko ba kya sona mu komawa aurenmu, son da nake Miki, da wadda Jawad yake miki ya isa yasa ki rayu cikin farin-ciki".
Ta goge kwalla ta ce "har abada ba zan yi farin ciki a hannun ka ba, ka rufe idonka ka ce mini ina ha'intarka, ka rufe ido ka ce mini ana maka sharing dina"
Muryarta ta fara rawa tabbacin tsumin bacin rai ya taso, ta nisa ta ce "ka rufe idonka ka barni ka dauki wadda kasan na tsaneta saboda munafuncinta, ta faki idon mutane ta tsokane ni, amma sai ta layance a kuma bata gaskiya. Allah ne ya rufawa al'umma asiri ba karatun lauyanci ta yi ba, dan anga kwarewa wurin bada kariya ga karya".
Da 'kyar ya ce na janye kalamina, wallahi tashin hankali ne da kishinki, Amma nasan ha'inta dai babbar ha'inta ba zaki yi ba, na san ni ka'dai ne na muaamalance ki, na tabbatar da hakan har zuciyata".
Wani abu mai nauyi da ya danne kirjin Sa'adah shekaru uku ya fa'da mata sai dan saura.
Ta ce "to shikenan na yafe maka. Amma ka sani gaskiya ban da buri ko sha'awar auren mai mata kishi kashe ni zai yi, kawai ka barni na auri wadda zan sami nutsuwa, ka bar ni nima na dandana wani namijin kamar yadda ka ke dandana Balarabiyar Yemen".
A sanyaye ya ce "Sa'a ina jiye miki tsoron kar ki zama ajalina, domin kuwa banda lafiya, duk sadda na ganki sai kin yi mini fami a akan jinyar da nake yi".
Kai tsaye ta ce" Tunda bakin cikin ka bai mayar da ni gawa ba, na tabbatar kaima ba zaka zama ba".
Cikin gajiyawa ya ce "Next week Jawad zasu yi hutu, gaba'daya zai yi hutunsa a gurinki".
Maimakon ta ji dadi saboda ta san dan ya faranta mata ne yasa ya yanke wannan hukuncin, sai ta yi nufin gwasale shi.
Ta ce "bana bu'katar ganinsa ma bare ya mini hutu, inace saboda kar ya zo na zuga shi yasa ka kai shi makarantar kwana? Saboda kana son sai ya so Farida sama da ni yasa ka hana ya kwana a gidan nan sai dai ya zo ya yini? To shima na barka maka shi ban bu'katarsa, Ni kuwa a duniya me zaka mini na huce, ka zalunce ni iyaka".
Kafin ya yi magana sai ganin Innah suka yi, a ladabce Mk ya sunkuya ya gaishe ta, ta amsa babu yabo babu fallasa, daga gaisuwar bata ko tambayi Hajiyarsa ba bare matarsa, ta juya tana cewa "kin dora girki kin barshi zai kone, daga cewa zaki karbo sako?".
Wannan shagulatin bangaro da Inna ta yi masa ya matu'kar dukan zuciyar sa, yana ganin rashin nasarar sa a fili, Bai ga laifinta ba ko kadan, domin ya fahimci tana kan fahimtar su Baba Isa da Hajiyar Bichi ne. Wato Baffah ne kawai hoope dinsa.
Akwai gumurzu kenan dan kuwa sai inda karfinsa ya kare, yanzu ne zai yi dambar jefa alkalamin sa cikin Tawada. Domin ya ga maneman nata dukkansu basu da makusa, shine ma mai tarin kalubalen rashin samun goyan baya a wurin iyaye da Sa'adatu sa'ar Mata.
Surayya Dee
✍️✍️.
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
NA
*SURAYYA DAHIRU*.
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
*_Doka mai lamba ta 68 ta nuna cewa satar fasaha babban laifi ne da yake dai da satar Dukiya._*