Sashe 78
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Amma ba ina nufin kita zama a hakan bane, ki bawa masu sonki kofar da za su tunkare ki, domin a hakan kika samu Mutari, yanzu kuma da kika barwa Allah ya miki zabi, ina da yakinin ba zai barki haka ba".
Jikinsu ya sake yin sanyi, suna gasgata maganganunsa, mussaman Sa'adah da take jin karfin zuciya na dirar mata, tana hango ya kamata ta budewa kanta kofofin farin-ciki, zata dawo da kwalliyar da ta da'de da daina yi, sannan zata sake dagewa a makaranta domin a yanzu da Mukhtar ya auri Farida sai take ganin tamkar ya raina arzikinsu ne.
*SURAYYA DAHIRU*
✍️✍️.
16/06.
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*
*A guji ta'ba wannan LABARIN ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.
*Gaisuwa da fatan alheri ga*
*HADIZA TINAU*.
*Ki yi yadda kike so da wannan shafin, farar mai farar zuciya, ubangiji ya yi mana abin da bamu yi zati ba na alheri*
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
89- 90.
Maganganun Baffah sun sake 'karawa Sa'a kwarin guiwar gina sabuwar rayuwar da babu Mk a cikinta.
Tana kwance har tsakiyar dare tana nazarin yadda zata koma sabuwar Sa'adah da bata san Mk ba, ta nisa tana hakaito abubawan da zata nema, bata da bu'katar sutura domin tana da su ba adadi tsadaddun gaske, da yawansu ma bata sake waiwaryasu ba.
Kayan kwalliya da waya tafi bukata a yanzu, sai hanyar da zata dinga samun ku'di tunda yanzu bata bu'katar na Mukhtar, tasan shima ba zai yi gigin bata ba.
Ta sani iyayenta da Sumayya suna iyakar kokarinta amma dai ba zai yiwu ace dukkan lalurarta sai an yi mata ba.
Saura kwana uku tafiyar su Jawad, Ahamad ya kawo shi gurin Sa'adah inji Hajiya ya kwana mata biyu, tare da sallama, tunda Mk ya yi aure Hajiya ta shiga cikin wani hali na kunyar Sa'a da iyayen ta, mussaman da Mk ya fada mata Baffan Sa'a ne ya biya masa sadaki, sai ta ji inama ace Hajiya Babbace a raye ita kuma a mace, tasan Hajiyar ta fita juriya da shanye 'bacin rai.
Sosai Sa'adah ta samu sau'kin zuciya cikin sati biyu nan, domin ko da ta ji tafiyar da Farida da Jawad za su yi bata wani damu ba, illah ta ji ba da'di, Jawad ne ma ya nemi karya mata zuciya da yawan tambayoyinsa akan me yasa ba zata bisu ba?
Da daddare suna kwance kansa na kirjinta yana bata labarin abubuwan da zai siyo mata idan zai dawo.
Can ya ce "to kawai Mami mu tafi tare mana, kema ai baki taba hawa jirgi ba".
A hankali ta ce "Malam bai ce na je ba, Aunty Amarya ya ce ta je".
"Mami idan kin je ai ba zai yi fa'da ba".
Cike da soyayyar 'danta ta ce "Ai bai biya mini kudin jirgi ba".
Ya yi shiru sai ya ce "Na ji kafin ya tafi ya fa'dawa Hajiya, Baban Antin ya ce shi zai biya kudin tafiyar mu".
Zuciyarta'daya ta ce " To ka ga ba ni a tafiya kenan tunda Ni Baffahna bashi da ku'di".
Ya yi shiru, can kuma ya kalleta tamkar wadda aka kitsa masa ya nisa! ya ce "Ni zan tara ku'di da yawa na kai ki, har jirgin ma zan siya miki".
Hawaye ya cika mata idanuwa, ta yi kokarin gogewa ba tare da ya gani ba.
Sai da ta shanye kukan da ya zo mata ta shafa kansa ta ce "Allah ya nufa Jawad, ubangiji ya maka albarka, idan ka je ka dinga sallah da wuri, komai Anti ta ce ka yi, kada ka yi mata musu kawai ka yi, ka dage da karatu sosai banda wasa, domin wadda zai siyi jirgi sai ya zama mai jin maganar iyayensa ya kuma yi karatu tukuru.
U.K.
A airport suka tarar da Mk yana fama jiran isowar su, da Jawad ya hango shi, da gudu ya nufe shi, da azama Mk ya daga shi sama domin abin da Jawad ya ke so kenan ya ga Babansa ya daga shi sama ya'ki yarda ya girma.
Taxi suka hau, zuwa gidan da zasu zauna, a hawa na takwas gidan yake dan haka Suka shiga lifta abin da ya burge Jawad, domin dai shine bai santa ba, tunda Farida ta saba fita kasashen waje.
Gajiyar hanyar da suka kwaso bai hana Mk sake dorawa Farida wata gajiyar ba, domin a matu'kar takure yake sai da ya samu ya zubar da abin da ya takura shi sannan ya ji shi daidai.
Rayuwa suke cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, Mk ya shayar da Farida mamaki da ya samar mata gurbin karatu a Jami'ar da yake inda zata yi masters dinta duk dai akan sanin magungunan (Pharmacy).
Ya ce " wurin aikin ki sun baki damar tafiya ne dan ki zurfafa ilimin ki, gara mu ki kiyaye ka'ida, sannan kema baza ki yi zaman kadaici idan bana nan, kuma Jawad yana school"
Cikin gaskiya da amana take ri'ke da Jawad komai yake so yi masa take yi, duk sadda ta je makaranta bata mantawa sai ta siyo masa abinda zai ji da'di, sun shaku sosai, da ke mai son jiki ne indai suna zaune to kuwa rabin jikinsa yana jikinta, sau tari Mk ke cewa "kina fama da kanki, amma sai ki kama katon yaro ki jingina wa kanki".
Murmushi take yi ta ce "Duka duka nawa ne adadin nauyinsa?"
Sosai ta samu saukin Ciwonta duk tashin da zai yi baya kayar da ita, kamar sadda take Nigeria, domin kwararren likitan ('kashi) take gani a asibitin jamiar, sannan zurfafa ilimin da take a fannin magunguna ya na taimakawa wurin sake sanin maganin da ya kamace ta.
Jawad yana ta karatunsa domin haziki ne sosai kamar Babansa bai yiwo shiriritar uwarsa ba, ko acan da suke da tsarin ilimi mai nagarta sosai yake ja, domin parfomance dinsa is very high hakan na farantawa iyayen nasa rai shiyasa komai ya ce yana so suke rige rigen yi masa.
Ba abin da yake damunsa sai rashin Jin muryar uwarsa a waya, tunda Mk yana ha'dasu da Hajiyar Bichi, da kuma Baffah, amma ya kasa samun layin Inna da Sa'adah ta ke amfani da shi, ita kuma tunda take ganin missed call din lambar waje ta kuma gane lambar Ingila ce sai ta yi blocking din layin shiyasa basa samun layin. kunyar Baffah take hana Mk tambayarta. Rannan Jawad sun gaisa da Baffa ya ce "Baffah ka bawa Mami wayar zan yi magana da ita".
Baffah da bai san Iyah ta rufe musu hanyar samunta ba ya ce "yanzu tana makaranta, Ni kuma bana gida ku nemeta a layinta ko na Innar ta.
Domin kuwa basu jima da barin kasar ba ta ce da Sumayya tana son waya, a satin ta turo mata da kudin waya mai tsadar gaske, tunda murna suke yi ta yarda zata ri'ke waya, alamun ta cire komai a ranta akan Mk, zata fuskaanci rayuwarta ta gaba.
Tsawon wattanni takwas kenan Jawad bai ji muryar uwarsa ba, a hankali sai abin yake 'dan ta'ba shi har abin ya fara bayyana a komai nasa, ya rage yawan surutu, ya daina walwala a tsakanin su, ya zama shiru shiru, sannan yafi son zaman daki fiye da falo.
Abin ya fara damun su mussaman Farida, ta yi tambayar duniya ya ce ba komai, Mk da ya gaji da yadda Farida take yawan damuwa da canjin Jawad ya ce "kifa daina damuwa, tunda dai ba wani abin aka masa ba, miskilin yaro ne na gaske, ni na yi mamakin yadda ya sake da ke tashi guda".
A marairaice ta ce "gaskiya akwai abin da yake damunsa domin ai ba haka ya ke ba, kamata yayi mu gano damuwarsa ko da cikin hikima ne".
Ranar alhamis da yamma, Mk da Jawad suna gida, yayin da Farida ta ke makaranta adalilin tana da lectures.
Cikin hikima ya hilaci Jawad akan ya ji me ya kawo changes din da suke gani a tare da shi, tunda bai fi sati da canjin nasa ba.
Cikin muryar kuka Jawad ya ce "Mamina! Na dade ban ganta ba, sannan tunda na zo bamu yi waya ba".
ya fada yana rushewa da kukan sosai.
Jikin Mk ya yi sanyi yasan Jawad ya yi kokari wattanni takwas da yawa, domin bai taba yin wata daya bai ganta ba, ko da yake hannun Hajiya duk karshen wata sai ya je ya yi kwanaki biyu.
Sannan tun farko yafi kulafacin uwarsa fiye da shi.
Jikinsa ya janyo shi yana fa'din ka yi shiru yau din nan zaku gaisa, ai da tun farko ka fa'da mini wannan ne damuwarka da tuni na magance maka ita.
Da kuka sosai Jawad ya ce "Am scared Malam".
Da mamaki sosai ya ce "Mai ya ke firgita ka?"
Last week na kalli wani firm a Fox movie (pendamic) yaron ciki ya tafi boarding school, shiru shiru bai ga mamar ta je ba, sannan baya samunta a waya Ashe she was died bai sani ba".
Kuka sosai ya sake barkewa da shi, zuciyar Mk ta dinga bugawa tamkar Sa'adatu ta mutu ne da gaske sune basu sani ba, domin yadda ya santa da Jawad bai zaci za'a shafe wannan wattannin bata nemi jin lafiyarsa ba.
Anya tunanin Jawad ba gaskiya bane?
Ya kasa cewa komai bare ya rarrashe shi wani irin abu ke masa yawo a jikinsa, ga dai sanyi a garin amma wata irin zufa ne ta fara karyo masa.
Ya dauko waya ya dinga gwada layin Inna amma sam baya tafiya.
Dabara ta fa'dowa Mk ya dinga lalubo lambar Zainab Ma'aji amma bashi da ita. Ya rasa yadda zai yi sosai Jawad ya firgita shi shima.
Da kyar ya shawo kan Jawad ya yi shiru bayan ya yi masa al'kawarin idan har ba'a sameta a waya ba, zai shirya musu tafiya Nigeria next week.
Jikinsu ya sake yin sanyi, suna gasgata maganganunsa, mussaman Sa'adah da take jin karfin zuciya na dirar mata, tana hango ya kamata ta budewa kanta kofofin farin-ciki, zata dawo da kwalliyar da ta da'de da daina yi, sannan zata sake dagewa a makaranta domin a yanzu da Mukhtar ya auri Farida sai take ganin tamkar ya raina arzikinsu ne.
*SURAYYA DAHIRU*
✍️✍️.
16/06.
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*
*A guji ta'ba wannan LABARIN ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.
*Gaisuwa da fatan alheri ga*
*HADIZA TINAU*.
*Ki yi yadda kike so da wannan shafin, farar mai farar zuciya, ubangiji ya yi mana abin da bamu yi zati ba na alheri*
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
89- 90.
Maganganun Baffah sun sake 'karawa Sa'a kwarin guiwar gina sabuwar rayuwar da babu Mk a cikinta.
Tana kwance har tsakiyar dare tana nazarin yadda zata koma sabuwar Sa'adah da bata san Mk ba, ta nisa tana hakaito abubawan da zata nema, bata da bu'katar sutura domin tana da su ba adadi tsadaddun gaske, da yawansu ma bata sake waiwaryasu ba.
Kayan kwalliya da waya tafi bukata a yanzu, sai hanyar da zata dinga samun ku'di tunda yanzu bata bu'katar na Mukhtar, tasan shima ba zai yi gigin bata ba.
Ta sani iyayenta da Sumayya suna iyakar kokarinta amma dai ba zai yiwu ace dukkan lalurarta sai an yi mata ba.
Saura kwana uku tafiyar su Jawad, Ahamad ya kawo shi gurin Sa'adah inji Hajiya ya kwana mata biyu, tare da sallama, tunda Mk ya yi aure Hajiya ta shiga cikin wani hali na kunyar Sa'a da iyayen ta, mussaman da Mk ya fada mata Baffan Sa'a ne ya biya masa sadaki, sai ta ji inama ace Hajiya Babbace a raye ita kuma a mace, tasan Hajiyar ta fita juriya da shanye 'bacin rai.
Sosai Sa'adah ta samu sau'kin zuciya cikin sati biyu nan, domin ko da ta ji tafiyar da Farida da Jawad za su yi bata wani damu ba, illah ta ji ba da'di, Jawad ne ma ya nemi karya mata zuciya da yawan tambayoyinsa akan me yasa ba zata bisu ba?
Da daddare suna kwance kansa na kirjinta yana bata labarin abubuwan da zai siyo mata idan zai dawo.
Can ya ce "to kawai Mami mu tafi tare mana, kema ai baki taba hawa jirgi ba".
A hankali ta ce "Malam bai ce na je ba, Aunty Amarya ya ce ta je".
"Mami idan kin je ai ba zai yi fa'da ba".
Cike da soyayyar 'danta ta ce "Ai bai biya mini kudin jirgi ba".
Ya yi shiru sai ya ce "Na ji kafin ya tafi ya fa'dawa Hajiya, Baban Antin ya ce shi zai biya kudin tafiyar mu".
Zuciyarta'daya ta ce " To ka ga ba ni a tafiya kenan tunda Ni Baffahna bashi da ku'di".
Ya yi shiru, can kuma ya kalleta tamkar wadda aka kitsa masa ya nisa! ya ce "Ni zan tara ku'di da yawa na kai ki, har jirgin ma zan siya miki".
Hawaye ya cika mata idanuwa, ta yi kokarin gogewa ba tare da ya gani ba.
Sai da ta shanye kukan da ya zo mata ta shafa kansa ta ce "Allah ya nufa Jawad, ubangiji ya maka albarka, idan ka je ka dinga sallah da wuri, komai Anti ta ce ka yi, kada ka yi mata musu kawai ka yi, ka dage da karatu sosai banda wasa, domin wadda zai siyi jirgi sai ya zama mai jin maganar iyayensa ya kuma yi karatu tukuru.
U.K.
A airport suka tarar da Mk yana fama jiran isowar su, da Jawad ya hango shi, da gudu ya nufe shi, da azama Mk ya daga shi sama domin abin da Jawad ya ke so kenan ya ga Babansa ya daga shi sama ya'ki yarda ya girma.
Taxi suka hau, zuwa gidan da zasu zauna, a hawa na takwas gidan yake dan haka Suka shiga lifta abin da ya burge Jawad, domin dai shine bai santa ba, tunda Farida ta saba fita kasashen waje.
Gajiyar hanyar da suka kwaso bai hana Mk sake dorawa Farida wata gajiyar ba, domin a matu'kar takure yake sai da ya samu ya zubar da abin da ya takura shi sannan ya ji shi daidai.
Rayuwa suke cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, Mk ya shayar da Farida mamaki da ya samar mata gurbin karatu a Jami'ar da yake inda zata yi masters dinta duk dai akan sanin magungunan (Pharmacy).
Ya ce " wurin aikin ki sun baki damar tafiya ne dan ki zurfafa ilimin ki, gara mu ki kiyaye ka'ida, sannan kema baza ki yi zaman kadaici idan bana nan, kuma Jawad yana school"
Cikin gaskiya da amana take ri'ke da Jawad komai yake so yi masa take yi, duk sadda ta je makaranta bata mantawa sai ta siyo masa abinda zai ji da'di, sun shaku sosai, da ke mai son jiki ne indai suna zaune to kuwa rabin jikinsa yana jikinta, sau tari Mk ke cewa "kina fama da kanki, amma sai ki kama katon yaro ki jingina wa kanki".
Murmushi take yi ta ce "Duka duka nawa ne adadin nauyinsa?"
Sosai ta samu saukin Ciwonta duk tashin da zai yi baya kayar da ita, kamar sadda take Nigeria, domin kwararren likitan ('kashi) take gani a asibitin jamiar, sannan zurfafa ilimin da take a fannin magunguna ya na taimakawa wurin sake sanin maganin da ya kamace ta.
Jawad yana ta karatunsa domin haziki ne sosai kamar Babansa bai yiwo shiriritar uwarsa ba, ko acan da suke da tsarin ilimi mai nagarta sosai yake ja, domin parfomance dinsa is very high hakan na farantawa iyayen nasa rai shiyasa komai ya ce yana so suke rige rigen yi masa.
Ba abin da yake damunsa sai rashin Jin muryar uwarsa a waya, tunda Mk yana ha'dasu da Hajiyar Bichi, da kuma Baffah, amma ya kasa samun layin Inna da Sa'adah ta ke amfani da shi, ita kuma tunda take ganin missed call din lambar waje ta kuma gane lambar Ingila ce sai ta yi blocking din layin shiyasa basa samun layin. kunyar Baffah take hana Mk tambayarta. Rannan Jawad sun gaisa da Baffa ya ce "Baffah ka bawa Mami wayar zan yi magana da ita".
Baffah da bai san Iyah ta rufe musu hanyar samunta ba ya ce "yanzu tana makaranta, Ni kuma bana gida ku nemeta a layinta ko na Innar ta.
Domin kuwa basu jima da barin kasar ba ta ce da Sumayya tana son waya, a satin ta turo mata da kudin waya mai tsadar gaske, tunda murna suke yi ta yarda zata ri'ke waya, alamun ta cire komai a ranta akan Mk, zata fuskaanci rayuwarta ta gaba.
Tsawon wattanni takwas kenan Jawad bai ji muryar uwarsa ba, a hankali sai abin yake 'dan ta'ba shi har abin ya fara bayyana a komai nasa, ya rage yawan surutu, ya daina walwala a tsakanin su, ya zama shiru shiru, sannan yafi son zaman daki fiye da falo.
Abin ya fara damun su mussaman Farida, ta yi tambayar duniya ya ce ba komai, Mk da ya gaji da yadda Farida take yawan damuwa da canjin Jawad ya ce "kifa daina damuwa, tunda dai ba wani abin aka masa ba, miskilin yaro ne na gaske, ni na yi mamakin yadda ya sake da ke tashi guda".
A marairaice ta ce "gaskiya akwai abin da yake damunsa domin ai ba haka ya ke ba, kamata yayi mu gano damuwarsa ko da cikin hikima ne".
Ranar alhamis da yamma, Mk da Jawad suna gida, yayin da Farida ta ke makaranta adalilin tana da lectures.
Cikin hikima ya hilaci Jawad akan ya ji me ya kawo changes din da suke gani a tare da shi, tunda bai fi sati da canjin nasa ba.
Cikin muryar kuka Jawad ya ce "Mamina! Na dade ban ganta ba, sannan tunda na zo bamu yi waya ba".
ya fada yana rushewa da kukan sosai.
Jikin Mk ya yi sanyi yasan Jawad ya yi kokari wattanni takwas da yawa, domin bai taba yin wata daya bai ganta ba, ko da yake hannun Hajiya duk karshen wata sai ya je ya yi kwanaki biyu.
Sannan tun farko yafi kulafacin uwarsa fiye da shi.
Jikinsa ya janyo shi yana fa'din ka yi shiru yau din nan zaku gaisa, ai da tun farko ka fa'da mini wannan ne damuwarka da tuni na magance maka ita.
Da kuka sosai Jawad ya ce "Am scared Malam".
Da mamaki sosai ya ce "Mai ya ke firgita ka?"
Last week na kalli wani firm a Fox movie (pendamic) yaron ciki ya tafi boarding school, shiru shiru bai ga mamar ta je ba, sannan baya samunta a waya Ashe she was died bai sani ba".
Kuka sosai ya sake barkewa da shi, zuciyar Mk ta dinga bugawa tamkar Sa'adatu ta mutu ne da gaske sune basu sani ba, domin yadda ya santa da Jawad bai zaci za'a shafe wannan wattannin bata nemi jin lafiyarsa ba.
Anya tunanin Jawad ba gaskiya bane?
Ya kasa cewa komai bare ya rarrashe shi wani irin abu ke masa yawo a jikinsa, ga dai sanyi a garin amma wata irin zufa ne ta fara karyo masa.
Ya dauko waya ya dinga gwada layin Inna amma sam baya tafiya.
Dabara ta fa'dowa Mk ya dinga lalubo lambar Zainab Ma'aji amma bashi da ita. Ya rasa yadda zai yi sosai Jawad ya firgita shi shima.
Da kyar ya shawo kan Jawad ya yi shiru bayan ya yi masa al'kawarin idan har ba'a sameta a waya ba, zai shirya musu tafiya Nigeria next week.