Sashe 52
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sannan a drower yake ajiye kudinsa baya mata iyaka, ya zara , ta zara, har su 'kare a haka, a wannan lokacin sai ya zauna ya yi 'kiyasin 200 zai isheta kullum da sunan kudin cefane, dan haka sai ya adana kudinsa yake bata wannan darin biyun, Jawad yake bawa ya kai mata.
A wannan lokacin da ya rikice mata, ya canja sosai, sai ta gane ashe dai da kirkinsa har yawa ya yi.
Ta fara neman hanyan sulhu, amma ta rasa yadda zata yi, yaki ya bata dama ko kadan, ko ta kai masa abinci baya ta'bawa haka take daukan abinta, ta fara daukan wanka da kwalliya, shikuma sai yake runtse idanuwansa daga kallonta.
Ta rasa mai kuma zata yi, sai ta dawo da gyara masa dakinsa, kullum idan ya fita, zata shiga ta gyara, gyara na mussaman, ranar da ta fara, da ya dawo ya gani, a ransa yace zaki san ba ke ka'dai kika iya neman masifa da tashin hankali ba.
Ganin ta debi kwanaki tana bin hanyoyin neman sulhu, amma ya yi biris da ita, sai ta canja salo.
Rannan da daddare ya dawo, ta kai masa abinci da tea din da ya zame masa ka'idar sha duk dare, tana ajiyewa yace " fita da su na gode".
Ta yi shiru tana kallon sa shikuma yana zaune, yana nazari a waya, amma yana jin kallon ta a jikinsa.
"Dan Allah Malam ka sha shayin nan na roke'ka".
Ya girgiza kai yace "Na koshi ne, ki ajiye zan sha da safe".
Da murna tace "Na gode".
Ta mayar kicin ta adana abincin a fridge, a gurguje ta yi wanka, ta bi dukkan jikinta ta shafa Arabians perfume masu kamshi sosai.
Ta dauko rigar barci ruwan madara, mai santsi ce kuma very transparent, ta gyara gashin kanta ta shafe shi da man gashi na Kuza. ta tsaya gaban madubi tana kallon kanta, tabbas ko ita ta burge kanta, ta tsinci bakinta da yin tasbihi da godiya gurin ubangiji,hakika an kyautata halittar ta.
Har taje falo kuma sai ta dawo, tana bin cinyoyinta da kallo, iyakacin Rigar rabin cinyarta ne, ko kusa da guiwata bata zo ba, bugu da kari, bata sa komai a kasan rigar ba.
Shaidan da zuciya suka fara wasan kura da hankalinta, suna kitsa mata idan taje a haka, ta yarda itace mai laifi, bayan duk irin yadda ya nuna mata ita da babu basu da maraba.
Ta tuna yadda ya shafe sama da sati biyu bai nemeta ba, shaidan ya sake tunzuro ta, yana jaddada mata irin zalamarsa akanta, idan ba wata ya samu a waje ba, yaushe zai iya jure tsawon kwanaki bai rabeta ba, tabbas mata yake bi na banza.
''
Ta koma ta kwanta a gadonta, tana Jin hawaye na bin fuskarta.
Sai juyi take yi, tana kallon yadda Jawad yake barcinsa cikin nutsuwa, tana jin inama itace shi, da bashi da wata matsala a duniyar sa, indai zai ci abinci, a masa wanka, a bashi sweet shikenan baisan komai na bacin Rai ba.
Ta kasa barci ta zabura ta sauko daga gadon, tana jin dolensa ya fada mata mai yake nufi da ita, ya kuntata mata, ya kuma fita fishi🤔
Ta kunna fitilar dakin, ta fice ba tare da ta kashe ba, saboda Jawad .
A zaune ta same shi, yana marking din exams din 'dalibai.
Ya amsa sallamarta, hankalinsa na kan takardar da ke gabansa.
Ganin bai 'dago ba, yasa tace "Ina son magana da kai".
Yana cigaba da marking yace "Amma dai kinga aikin da ke gabana ko? Sai ki jira na kammala, ko ki tari lokacina na gaba".
Hawaye ta ji na neman kwace mata, da ta tuna kafin su fara takun saka, baya iya yin aiki sosai matu'kar suna tare, ya fi kauri wurin tsokanarta, ta hanyar dumbulan kirjinta, ko ya biyeta su yi ta shiririta, tana bashi labarin ai tana yawan mafarki ta zama Hajiya, ta zama big madam, shikuma ya yi kudi, ya zama Alhaji, ya gina musu katon mansion.
sai yace Ina fatan dai ba kiga na 'kara aure ba? Wani lokacin tace bata gani ba cikin da'din Rai, wani lokacin tace abin da yake ransa ne, sai ta hau bori, shikuma ya lalace wurin rarrashin ta, a haka har su cinye lokaci mai yawa basu farga ba.
Amma a yau, gata a gabansa yana nuna mata bashi da lokacin saurarenta, aikin da yake yi ya fita muhimmanci kenan?.
Da gaske ita da Babu 'daya ne a gurinsa? sai kawai ta fashe masa da kuka irin wadda ta tabbatar yana gigita shi.
Surayya Dahiru
✍️✍️.
30/03.
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
NA
*Surayya Dahiru*.
Lafazee writers.
*Doka mai lamba ta 68 ta nina cewa satar fasaha babban laifine da yake dai-dai da satar Dukiya*.
*A kiyayi ta'ba wannan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*
67-70.
Ya yi shiru yana jin kukan da take masa, yana ayyana rashin mutuncin ta kullum kara gaba yake yi. ransa ya baci iyaka, mussaman yadda ta ware murya tana masa kuka tamkar wadda ya ke mata dukan kawo wu'ka.
Ya kasa cewa komai, domin zuciyarsa sai fada masa take, ya daketa kawai, ko ya huce kadan cikin takaicin da take guma masa, itama kuma sai ta yi kukan mai dalili.
Tsawon lokaci tana kukanta, jikinta ya yi sanyi tubus, a dalilin halin ko in kula daya ya mata, da gaske dai Malam ya gaji da ita, hakan ya sake sa ta fashe da sabon kuka fiye da wadda take yi.
A harzuke ya nuna ta da yatsa yana cewa " tashi ki koma dakin ki, kici gaba da kukan a can. Idan kuma ba ki gama min tuya a gurin makwabta ba, sai ki kara himma har su shigo su ceceki."
Jin hakan yasa ta rage sautin kukanta, shikuma ya cigaba da aikinsa amma bashi da sukuni ko kadan, ya kuma yi al'kawarin ba zai ce ta daina kukan da take yi ba.
Aikuwa kusan raba dare ta yi, tana masa gunjin kukan da babu shagwaba, sai zallar bacin rai, irin kukan da me yinsa yake son a rarrashe shi, lura da hakan da yayi shikuma ya yi biris da ita, dan kuwa bai ga dalilin kukanta ba, shi ta musganawa, ta masa rashin kunya, bata bashi hakuri ba, shine take sa ran shi ya risina mata, lokaci ya yi da zai daina biyewa son zuciyar sa akan lamarin ta.
A inda take zaune barci ya sureta, sai sakin ajiyar take yi.
Sai da ya gama aikinsa, ya kammala komai, ya dauko Jawad ya kwantar da shi, ya dauko bargo ya lulluba mata, sannan ya kashe fitila ya kwanta bayan ya rungumo Jawad a jikinsa.
Da asuba ta tashi ta ganta lullube da bargo, ta ji dadi, sai dai rashin tashinta ta yi sallah ya dakushe waccan jin dadin, ta kalleshi har ya dawo daga masallaci, ta zuba masa idon da ya kumbura saboda kuka, murya a dashe tace "Malam abin har ya gagareka tashina na yi sallah?"
Ya yi mata shiru tamkar ba da shi take yi ba.
Takaicinsa ya sake kumeta, tace "Ma'aiki dai yace Allah ya jikan mijin da ya tashi cikin dare ya kuma tashi iyalinsa suka yi sallar nafila, to ina kuma ga wadda ya tashi, ya kuma tashi iyalinsa dan sallar Farillah? ka rasa wannan ladan, ba nice da asara ba".
Ya zuba mata ido yana kallon ta, Yana jin sabon tashin hankali na shigarsa, tabbas ta kerewa tunaninsa, an mata famfo fiye da duk yadda yake zato.
Haka ta gama sakin magaganu sannan ta fita zuwa dakinta, don yin sallah.
Kan Mk ya kulle, ya rasa mai zai mata, ya yi fushin, ya bagarar da ita, Amma duk a banza, wai ya zai mata ne? kawai sai ya tsinci kansa da daga hannunsa sama yana cewa "Allah kasan irin son da nake yiwa Sa'adah, Allah ka shirya min ita, ka bude kirjinta ta gane gaskiya, ta fahimci bani da nufin zaluntarta, ka zaunar da mu lafiya, Allah ka kara min ha'kurin zama da ita cikin adalci".
Ya kishingida yana tunano kafin shigowar su Halima cikin rayuwar aurensu, ko ya ya taga ya canja mata, ta dinga tambayar me ya same shi, ko itace ta masa laifi? Ta dinga bashi hakuri kenan, ko yace bata masa komai ba, kawai yanayi ne, ko baya jin dadi ne, duk da haka hankalin ta baya kwanciya sai ya dawo da walwalarsa, amma a yanzu kusan sati uku suna dauki ba dadi, amma kullum da abin da zata yi da zai sake bakanta masa Rai, karon farko da ya fara zargin Anya kuwa dama Sa'adah da gaske tana sonsa?
Ya dinga hasaso yadda yake gudun zuciyarta, har wasu da yawa suna ganin tsoronta yake ji, alhalin ba haka bane, kawai tsananin sonta da yake yi ne, yasa baya shiri da duk abin da zaisa ta koka, mussaman na rashin wani abu, zai ha'kura da dukkan bukatun kansa, matu'kar ita zata wadatu. Amma duk su Safina sun lalata mata tunani, sun jefa mata shubuha, wai yan mata ne da shi na banza! Tabbas suna neman raba shi da ita ne.
A fili ya furta " Allah kana ganin masu son shiga tsakanin aure, Allah ka min maganinsu".
Sai da ya isa makaranta! Ya na cikin motarsa ya ciro wayarsa, ya lalubo lambar Anty Sumayya, cike da girmamawa ya gaisheta, sai kuma ya yi shiru ya na jin nauyin zartar da kudiransa. Jin yanayinsa yasa ta tambayarsa ko akwai matsala ne?
Cikin jin nauyi ainun yace " So nake ki yiwa Sa'adah magana, mun dade cikin rashin nutsuwa, na yi iyakacin kokarina dan mu fahimci juna abin yaci tura, bana son na tayarwa da su Baffah hankali".
Hakuri Sumayya ta dinga bashi, tare da al'kawarin yanzun nan zata kirata.
Kai tsaye yace "ba waya a hannun ta".
A wannan lokacin da ya rikice mata, ya canja sosai, sai ta gane ashe dai da kirkinsa har yawa ya yi.
Ta fara neman hanyan sulhu, amma ta rasa yadda zata yi, yaki ya bata dama ko kadan, ko ta kai masa abinci baya ta'bawa haka take daukan abinta, ta fara daukan wanka da kwalliya, shikuma sai yake runtse idanuwansa daga kallonta.
Ta rasa mai kuma zata yi, sai ta dawo da gyara masa dakinsa, kullum idan ya fita, zata shiga ta gyara, gyara na mussaman, ranar da ta fara, da ya dawo ya gani, a ransa yace zaki san ba ke ka'dai kika iya neman masifa da tashin hankali ba.
Ganin ta debi kwanaki tana bin hanyoyin neman sulhu, amma ya yi biris da ita, sai ta canja salo.
Rannan da daddare ya dawo, ta kai masa abinci da tea din da ya zame masa ka'idar sha duk dare, tana ajiyewa yace " fita da su na gode".
Ta yi shiru tana kallon sa shikuma yana zaune, yana nazari a waya, amma yana jin kallon ta a jikinsa.
"Dan Allah Malam ka sha shayin nan na roke'ka".
Ya girgiza kai yace "Na koshi ne, ki ajiye zan sha da safe".
Da murna tace "Na gode".
Ta mayar kicin ta adana abincin a fridge, a gurguje ta yi wanka, ta bi dukkan jikinta ta shafa Arabians perfume masu kamshi sosai.
Ta dauko rigar barci ruwan madara, mai santsi ce kuma very transparent, ta gyara gashin kanta ta shafe shi da man gashi na Kuza. ta tsaya gaban madubi tana kallon kanta, tabbas ko ita ta burge kanta, ta tsinci bakinta da yin tasbihi da godiya gurin ubangiji,hakika an kyautata halittar ta.
Har taje falo kuma sai ta dawo, tana bin cinyoyinta da kallo, iyakacin Rigar rabin cinyarta ne, ko kusa da guiwata bata zo ba, bugu da kari, bata sa komai a kasan rigar ba.
Shaidan da zuciya suka fara wasan kura da hankalinta, suna kitsa mata idan taje a haka, ta yarda itace mai laifi, bayan duk irin yadda ya nuna mata ita da babu basu da maraba.
Ta tuna yadda ya shafe sama da sati biyu bai nemeta ba, shaidan ya sake tunzuro ta, yana jaddada mata irin zalamarsa akanta, idan ba wata ya samu a waje ba, yaushe zai iya jure tsawon kwanaki bai rabeta ba, tabbas mata yake bi na banza.
''
Ta koma ta kwanta a gadonta, tana Jin hawaye na bin fuskarta.
Sai juyi take yi, tana kallon yadda Jawad yake barcinsa cikin nutsuwa, tana jin inama itace shi, da bashi da wata matsala a duniyar sa, indai zai ci abinci, a masa wanka, a bashi sweet shikenan baisan komai na bacin Rai ba.
Ta kasa barci ta zabura ta sauko daga gadon, tana jin dolensa ya fada mata mai yake nufi da ita, ya kuntata mata, ya kuma fita fishi🤔
Ta kunna fitilar dakin, ta fice ba tare da ta kashe ba, saboda Jawad .
A zaune ta same shi, yana marking din exams din 'dalibai.
Ya amsa sallamarta, hankalinsa na kan takardar da ke gabansa.
Ganin bai 'dago ba, yasa tace "Ina son magana da kai".
Yana cigaba da marking yace "Amma dai kinga aikin da ke gabana ko? Sai ki jira na kammala, ko ki tari lokacina na gaba".
Hawaye ta ji na neman kwace mata, da ta tuna kafin su fara takun saka, baya iya yin aiki sosai matu'kar suna tare, ya fi kauri wurin tsokanarta, ta hanyar dumbulan kirjinta, ko ya biyeta su yi ta shiririta, tana bashi labarin ai tana yawan mafarki ta zama Hajiya, ta zama big madam, shikuma ya yi kudi, ya zama Alhaji, ya gina musu katon mansion.
sai yace Ina fatan dai ba kiga na 'kara aure ba? Wani lokacin tace bata gani ba cikin da'din Rai, wani lokacin tace abin da yake ransa ne, sai ta hau bori, shikuma ya lalace wurin rarrashin ta, a haka har su cinye lokaci mai yawa basu farga ba.
Amma a yau, gata a gabansa yana nuna mata bashi da lokacin saurarenta, aikin da yake yi ya fita muhimmanci kenan?.
Da gaske ita da Babu 'daya ne a gurinsa? sai kawai ta fashe masa da kuka irin wadda ta tabbatar yana gigita shi.
Surayya Dahiru
✍️✍️.
30/03.
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
NA
*Surayya Dahiru*.
Lafazee writers.
*Doka mai lamba ta 68 ta nina cewa satar fasaha babban laifine da yake dai-dai da satar Dukiya*.
*A kiyayi ta'ba wannan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*
67-70.
Ya yi shiru yana jin kukan da take masa, yana ayyana rashin mutuncin ta kullum kara gaba yake yi. ransa ya baci iyaka, mussaman yadda ta ware murya tana masa kuka tamkar wadda ya ke mata dukan kawo wu'ka.
Ya kasa cewa komai, domin zuciyarsa sai fada masa take, ya daketa kawai, ko ya huce kadan cikin takaicin da take guma masa, itama kuma sai ta yi kukan mai dalili.
Tsawon lokaci tana kukanta, jikinta ya yi sanyi tubus, a dalilin halin ko in kula daya ya mata, da gaske dai Malam ya gaji da ita, hakan ya sake sa ta fashe da sabon kuka fiye da wadda take yi.
A harzuke ya nuna ta da yatsa yana cewa " tashi ki koma dakin ki, kici gaba da kukan a can. Idan kuma ba ki gama min tuya a gurin makwabta ba, sai ki kara himma har su shigo su ceceki."
Jin hakan yasa ta rage sautin kukanta, shikuma ya cigaba da aikinsa amma bashi da sukuni ko kadan, ya kuma yi al'kawarin ba zai ce ta daina kukan da take yi ba.
Aikuwa kusan raba dare ta yi, tana masa gunjin kukan da babu shagwaba, sai zallar bacin rai, irin kukan da me yinsa yake son a rarrashe shi, lura da hakan da yayi shikuma ya yi biris da ita, dan kuwa bai ga dalilin kukanta ba, shi ta musganawa, ta masa rashin kunya, bata bashi hakuri ba, shine take sa ran shi ya risina mata, lokaci ya yi da zai daina biyewa son zuciyar sa akan lamarin ta.
A inda take zaune barci ya sureta, sai sakin ajiyar take yi.
Sai da ya gama aikinsa, ya kammala komai, ya dauko Jawad ya kwantar da shi, ya dauko bargo ya lulluba mata, sannan ya kashe fitila ya kwanta bayan ya rungumo Jawad a jikinsa.
Da asuba ta tashi ta ganta lullube da bargo, ta ji dadi, sai dai rashin tashinta ta yi sallah ya dakushe waccan jin dadin, ta kalleshi har ya dawo daga masallaci, ta zuba masa idon da ya kumbura saboda kuka, murya a dashe tace "Malam abin har ya gagareka tashina na yi sallah?"
Ya yi mata shiru tamkar ba da shi take yi ba.
Takaicinsa ya sake kumeta, tace "Ma'aiki dai yace Allah ya jikan mijin da ya tashi cikin dare ya kuma tashi iyalinsa suka yi sallar nafila, to ina kuma ga wadda ya tashi, ya kuma tashi iyalinsa dan sallar Farillah? ka rasa wannan ladan, ba nice da asara ba".
Ya zuba mata ido yana kallon ta, Yana jin sabon tashin hankali na shigarsa, tabbas ta kerewa tunaninsa, an mata famfo fiye da duk yadda yake zato.
Haka ta gama sakin magaganu sannan ta fita zuwa dakinta, don yin sallah.
Kan Mk ya kulle, ya rasa mai zai mata, ya yi fushin, ya bagarar da ita, Amma duk a banza, wai ya zai mata ne? kawai sai ya tsinci kansa da daga hannunsa sama yana cewa "Allah kasan irin son da nake yiwa Sa'adah, Allah ka shirya min ita, ka bude kirjinta ta gane gaskiya, ta fahimci bani da nufin zaluntarta, ka zaunar da mu lafiya, Allah ka kara min ha'kurin zama da ita cikin adalci".
Ya kishingida yana tunano kafin shigowar su Halima cikin rayuwar aurensu, ko ya ya taga ya canja mata, ta dinga tambayar me ya same shi, ko itace ta masa laifi? Ta dinga bashi hakuri kenan, ko yace bata masa komai ba, kawai yanayi ne, ko baya jin dadi ne, duk da haka hankalin ta baya kwanciya sai ya dawo da walwalarsa, amma a yanzu kusan sati uku suna dauki ba dadi, amma kullum da abin da zata yi da zai sake bakanta masa Rai, karon farko da ya fara zargin Anya kuwa dama Sa'adah da gaske tana sonsa?
Ya dinga hasaso yadda yake gudun zuciyarta, har wasu da yawa suna ganin tsoronta yake ji, alhalin ba haka bane, kawai tsananin sonta da yake yi ne, yasa baya shiri da duk abin da zaisa ta koka, mussaman na rashin wani abu, zai ha'kura da dukkan bukatun kansa, matu'kar ita zata wadatu. Amma duk su Safina sun lalata mata tunani, sun jefa mata shubuha, wai yan mata ne da shi na banza! Tabbas suna neman raba shi da ita ne.
A fili ya furta " Allah kana ganin masu son shiga tsakanin aure, Allah ka min maganinsu".
Sai da ya isa makaranta! Ya na cikin motarsa ya ciro wayarsa, ya lalubo lambar Anty Sumayya, cike da girmamawa ya gaisheta, sai kuma ya yi shiru ya na jin nauyin zartar da kudiransa. Jin yanayinsa yasa ta tambayarsa ko akwai matsala ne?
Cikin jin nauyi ainun yace " So nake ki yiwa Sa'adah magana, mun dade cikin rashin nutsuwa, na yi iyakacin kokarina dan mu fahimci juna abin yaci tura, bana son na tayarwa da su Baffah hankali".
Hakuri Sumayya ta dinga bashi, tare da al'kawarin yanzun nan zata kirata.
Kai tsaye yace "ba waya a hannun ta".