Sashe 46
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kuka kawai take yi, da kyar ta ce "Ni dai idan na mutu ki yafe mini, ba da gangan na ki zuwa ba".
Sai ta katse wayar tana goge hawayen, a fili ta ce, "Na san gobe zan gan ki kin zo, kin ga abin da nake boyewa."
Hakan kuwa! Inna kwana ta yi tana zullumin wane ciwo ne ya addabi Iyah haka?
Karfe goma na safe ta isa gidan don ma Baffa ne ya hana ta fitowar sassafe, da tuni ta dade da zuwa.
Mamakin cikin da ta gani jikin Iyah ya zarta wanda ta yi a lokacin cikin Jawad, ta rasa mai za ta ce musamman da ta ga ya yi kwari, har yana shirin fitowa duniya.
Ganin irin kallon mamakin da Innar ta bi ta da shi, yasa ta kifa kai a hannun kujera ta fara sana'ar kuka.
Da tausayawa Inna tace, "Ni kin san akan koke-koken nan naki, muke batawa, mene ne kuma na kukan? Mene ne yake damun ki?"
Sanin bata da matsalar komai sai na cikin nan da ya mata shigar sauri yasa ta kasa cewa uffan.
"Idan na fahimce ki, halin da kike ciki yasa kika mayar da kanki mujiya a cikin jama'a, ke baki san baiwa ce Uabngiji ya miki ba, ai ba kowacce mace ke samun damar samun irin wannan haihuwar ba".
Ta ja numfashi ta ci gaba da cewa "jiyan nan aka mana tarihin Nana Fadima a Islamiyyar da na shiga, ashe Sayyadi Hassan da Sayyadi Husain ba tagwaye ba ne?
Duk zatona 'yan biyu ne, ashe daban-daban aka haife su amma Malamai sun yi ittikafin wata goma sha daya ne tsakanin su, ashe matar da tayi irin wannan haihuwar abin alfahari ne a gurinta, abin a mata barka ne, don kuwa albarkar diyar Ma'aiki ta samu".
Haka ta dinga rarrashin ta har ta sami nutsuwa.
Ta kara da cewa "Har addu'a nake miki kar ki yi irin haihuwa ta, ko irin ta uwar mijinki, kin ga dai shi ma su uku ne a dakinsu, da bakin ki kika ce mini sai da ya shekara goma aka haifi Ahmad kaninsa, ni kuwa tun a kanki aka rufe mini kofa, ki kwantar da hankalinki, idan Allah ya sauke ki lafiya, idan mijinki ya yarda zan daukar miki Jawad ke ki ji da jariri ko jaririya".
Sai Azahar ta tafi, har girki ta mata, sannan ta tafi ta bar Jawad na kukan zai bi ta ya gan ta da Hijabi.
Ba ta da'de da tafiya ba, Sa'adah ta dinga jin kwankwasa kofa, ta san ba Mk ba ne tunda da key a hannun sa budewa kawai yake yi shi yasa ba ta sa sakata.
Da Jawad a hannunta, ta fita ta bude kofar, ta yi turus ganin Halima da Safina a tsaye, cikin kwalliya ta burgewa sai kamshi suke yi.
Har suka shiga cikin gidan wani irin kallo suke mata, na uku saura kwata, suka zauna, ita kuma ta fice zuwa kicin ta zuba pure water mai sanyi, akan tray, ta kawo musu tana cewa "Sannun ku, daga ina kuke haka?"
Safina ce ta ce "Daga makaranta kin san sai yanzu aka fara daukar sababbin dalibai saboda dogon yajin aikin da ASUU ta yi".
Sa'adah ta ri'ke baki ta ce "Oh kuce da students nake tare, wane course kuke yi?"
Still Safina ce ta sake cewa dukkan mu Diploma in Public Administration muke yi, ba mu samu degree ba, saboda points din mu ba su kai ba, amma a satin nan zamu cike JAMB tunda an fara za mu sake trying".
"Ma Sha llah! Congrats, na muku murna, ni ma In sha Allah zan yi JAMB din, gara da na ji da wuri, amma ni Sociology ne zabina ko kuma English Language".
Sai lokacin Halima ta ajiye wayarta da take ta latsawa ta dube ta sannan ta ce "A ina za ki yi wannan karatun da kike fa'da?
Kai tsaye Sa'adah ta ce " B.U.K mana".
Dariya Halima ta yi irin ta iyashege sannan ta kalle ta, ta kalli cikin jikinta, ta sake mahar da kallon ta ga Jawad, ta ce, "Sai dai idan a gaban Uncle za ki yi karatun, tunda shi ma harshen Turanci ya karanta, yake kuma koyarwa".
"Ban gane ba?" Sa'adah ta tambaya da alamun karin bayani.
Ba kunya ba komai Halima ta kalli cikin idonta ta ce "Na ga ya mayar da ke akuya ne, ke kuma kin biye masa, don Allah dubi yadda kika zama just one year da aure".
Kalmar akuyar nan ta bugi Sa'adah, ta kasa hakuri ta ce, ni ce na zama akuya?"
"To mene ne banbancin ki da ita? Ki kalli kanki mana, 'da a hannu, 'da a ciki".
Idon Sa'adah ya cika da kwalla tabbas da gaskiyar Halima irin haihuwar akuya za ta yi.
Kafin ta yi magana, Safina ta tsoma baki ta ce "Ni fa tunda na zauna mamakin Gogel nake yi, ta saki jiki za ta mayar da kanta tamkar irin jakunan matan nan na kauye da ba su san komai ba sai dai su ci, su haihu duk shekara, duk iyashegen da namiji zai musu ba yadda za su yi saboda sun tara garke da shi, yo a wannan karnin wacce macen ce za ta yi irin wannan?"
Halima ta cafe da fa'din "Ba ki ga yadda ta susuce ba? tamkar ba Gogel fine girl din nan ba, duk ta tsofe, ta sakar masa jiki, shi ya tsotseta da daddare, dansa ya yini yana tsotsarta, duk kuma abin da zata ci sai anraba musu da unborn, in and out suke lasar ta, ba dole ta fita a hayyacinta ba".
"Sai ikon Allah, ke da karatu, sai ya gama tsofar da ke, kin daina burge shi, kiga ya dallo sabuwar yarinya, da ilimi ya gogar da ita, tunda kullum yana ganin yan mata sabbin 'kyan 'kyasa".
Hankali Sa'a ba karamin tashi ya yi ba, saboda yadda ta gasgata maganganunsu, mussaman da tasan kullum a cikin ganin tsala tsalan yan matan Jami'a ya ke.
A sanyaye tace "ya zanyi ne? ni kaina ban shirya haihuwa yanzu ba, sannan kuma shine yaki yarda! da nace sai dai a cire"
Dukkansu dariya suka sa mata, sai da suka tsagaita da dariyar! sannan suka ce, mai
yasa da kika yi arbain, ba ki je asibiti an dora ki akan maganin tsarin iyali ba?"
Kafin ta amsa, sun zarce da fadin " kar ki sake yin ganganci irin haka, idan kuma kin ki ji, ba Kya ki gani ba".
"Tuwo Inna ta yi mana zaku ci ko na dafa muku indomie?"
Shiru suka yi tamkar basu ji ba, sai can kuma Safina tace "Ni kam bana cin tuwo".
Halima bata dago ba, tace yi Indomie din kawai, amma plz kisa mana pepper sosai".
Haka ta dafa musu indomie da ta ji albasa da attaruhu, ta hada musu lemon Tang a jug ta fasa kankara ta jefa a ciki.
Sai da suka ci, suka gyatse, suka yi la'asar sannan suka tafi bayan sun jefa mata wasiwasi a zuciyar ta.
Daf da maghrib ya dawo gida, a gurguje yayi wanka ya tafi masallaci, sai da ya dawo, ya dauko musu abincin, suna ci, ya lura Sa'adah ba ta da walwala sosai, ya tambayi ko bata jin dadi ne! ta ce kalau take, ta isar da sakon gaisuwar Inna, da fara'a ya ce "Ina amsawa, ta biyo sawunki kenan? Ina fatan dai kin fa'da mata, bani da alhakin rashin ganin ki a gidansu?"
Kai tsaye ta ce "ko ban fada ba, ai tasan kaine, tunda ka mayar da Ni Akuya".
Maganar ta shige shi, amma sai ya ce ban gane na mayar da ke akuya ba?"
"Eh mana wata biyu da haihuwa ka sake dirka mini wani cikin, ai akuya ce mai hakan".
Ya kalleta soasai ya tabbatar wannan maganar ba daga zuciya da kwakwalwarta ta fito ba, ya kuma tabbatar ba a bakin mahaifiyarta ta ji ba.
Ya numfasa yace " Inna bata yi farincikin ganin ki da cikin ba kenan?"
"Hmm ita da take ta murna wai dama har addu'a take yi mana kar na gado rashin yawan haihuwar su ita da Hajiyar Bichi".
Ya sauke ajiyar zuciya, hankalinsa ya sake tashi, tabbas akwai wacce ta zo take kokarin birkita masa zaman lafiya a gidansa.
A zahiri sai ya murmusa ya ce " Ashe adduar Innace ta sauka akan mu, ba wai akuya na maida ki ba".
Ta tura baki gaba, tana jin ba zata sake yarda ta yi irin wannan gangancin ba a gaba.
A kicin ya ga tray din da aka ci indomie mai dauke da fork guda biyu.
duk yadda akayi wadannan bakin da ta yi ne, suka kitsa mata maganganu, tunda duk boren da ta masa a farko, ai tunanin ta bai bata irin wannan kalamin ba.
Bai sake shan mamaki ba, sai da suka kwanta, ya ji ta ce zasu yi magana, ya ce "Ina jinki".
"Uncle so nake yi nima na cike jamb foam".
Ya ji zuciyar sa ta buga, sai ya danne, cikin dabara dan ya fahimci inda ta dosa.
Ya ce " da kam ina da buri ki yi a wannan shekarar, kafin lokacin da komai zai kammala na samun admission kin yaye Jawad sai ki fara karatun ki, ba wata matsala".
"Yanzu kuma shikenan sai ba zan yi ba?"
Ta fa'da da gatsali.
"Ya sake dannar zuciyarsa ya ce " za ki yi mana, amma dai sai next year".
Ta tunzuro sosai ta ce "kenan sai nan da shekaru biyu kake nufi zan fara?"
Ba ja in ja ya ce " eh".
Jin haka ta fara sakin magaganu "Ni wallahi bazan yarda ba, kafin nan da shekaru biyu only God knows mai zaka mayar da Ni".
Ya yi shiru yana ta neman tsarin Allah ya kare zuciyar sa daga sharrin shaidan da fishi.
Jin ya mata shiru ba'kin cikin ta ya karu,ta fashe masa da kuka mai sauti, tana fadin son kansa ya yi yawa, duk 'kawayenta kowa na karatu sai ita kadaice mai zaman banza da kashe wando.
Rukota yayi zuwa jikinsa tana fizgewa, kan dole ya kwantar da ita, yasa hannun sa ya zagayeta.
Sai ta katse wayar tana goge hawayen, a fili ta ce, "Na san gobe zan gan ki kin zo, kin ga abin da nake boyewa."
Hakan kuwa! Inna kwana ta yi tana zullumin wane ciwo ne ya addabi Iyah haka?
Karfe goma na safe ta isa gidan don ma Baffa ne ya hana ta fitowar sassafe, da tuni ta dade da zuwa.
Mamakin cikin da ta gani jikin Iyah ya zarta wanda ta yi a lokacin cikin Jawad, ta rasa mai za ta ce musamman da ta ga ya yi kwari, har yana shirin fitowa duniya.
Ganin irin kallon mamakin da Innar ta bi ta da shi, yasa ta kifa kai a hannun kujera ta fara sana'ar kuka.
Da tausayawa Inna tace, "Ni kin san akan koke-koken nan naki, muke batawa, mene ne kuma na kukan? Mene ne yake damun ki?"
Sanin bata da matsalar komai sai na cikin nan da ya mata shigar sauri yasa ta kasa cewa uffan.
"Idan na fahimce ki, halin da kike ciki yasa kika mayar da kanki mujiya a cikin jama'a, ke baki san baiwa ce Uabngiji ya miki ba, ai ba kowacce mace ke samun damar samun irin wannan haihuwar ba".
Ta ja numfashi ta ci gaba da cewa "jiyan nan aka mana tarihin Nana Fadima a Islamiyyar da na shiga, ashe Sayyadi Hassan da Sayyadi Husain ba tagwaye ba ne?
Duk zatona 'yan biyu ne, ashe daban-daban aka haife su amma Malamai sun yi ittikafin wata goma sha daya ne tsakanin su, ashe matar da tayi irin wannan haihuwar abin alfahari ne a gurinta, abin a mata barka ne, don kuwa albarkar diyar Ma'aiki ta samu".
Haka ta dinga rarrashin ta har ta sami nutsuwa.
Ta kara da cewa "Har addu'a nake miki kar ki yi irin haihuwa ta, ko irin ta uwar mijinki, kin ga dai shi ma su uku ne a dakinsu, da bakin ki kika ce mini sai da ya shekara goma aka haifi Ahmad kaninsa, ni kuwa tun a kanki aka rufe mini kofa, ki kwantar da hankalinki, idan Allah ya sauke ki lafiya, idan mijinki ya yarda zan daukar miki Jawad ke ki ji da jariri ko jaririya".
Sai Azahar ta tafi, har girki ta mata, sannan ta tafi ta bar Jawad na kukan zai bi ta ya gan ta da Hijabi.
Ba ta da'de da tafiya ba, Sa'adah ta dinga jin kwankwasa kofa, ta san ba Mk ba ne tunda da key a hannun sa budewa kawai yake yi shi yasa ba ta sa sakata.
Da Jawad a hannunta, ta fita ta bude kofar, ta yi turus ganin Halima da Safina a tsaye, cikin kwalliya ta burgewa sai kamshi suke yi.
Har suka shiga cikin gidan wani irin kallo suke mata, na uku saura kwata, suka zauna, ita kuma ta fice zuwa kicin ta zuba pure water mai sanyi, akan tray, ta kawo musu tana cewa "Sannun ku, daga ina kuke haka?"
Safina ce ta ce "Daga makaranta kin san sai yanzu aka fara daukar sababbin dalibai saboda dogon yajin aikin da ASUU ta yi".
Sa'adah ta ri'ke baki ta ce "Oh kuce da students nake tare, wane course kuke yi?"
Still Safina ce ta sake cewa dukkan mu Diploma in Public Administration muke yi, ba mu samu degree ba, saboda points din mu ba su kai ba, amma a satin nan zamu cike JAMB tunda an fara za mu sake trying".
"Ma Sha llah! Congrats, na muku murna, ni ma In sha Allah zan yi JAMB din, gara da na ji da wuri, amma ni Sociology ne zabina ko kuma English Language".
Sai lokacin Halima ta ajiye wayarta da take ta latsawa ta dube ta sannan ta ce "A ina za ki yi wannan karatun da kike fa'da?
Kai tsaye Sa'adah ta ce " B.U.K mana".
Dariya Halima ta yi irin ta iyashege sannan ta kalle ta, ta kalli cikin jikinta, ta sake mahar da kallon ta ga Jawad, ta ce, "Sai dai idan a gaban Uncle za ki yi karatun, tunda shi ma harshen Turanci ya karanta, yake kuma koyarwa".
"Ban gane ba?" Sa'adah ta tambaya da alamun karin bayani.
Ba kunya ba komai Halima ta kalli cikin idonta ta ce "Na ga ya mayar da ke akuya ne, ke kuma kin biye masa, don Allah dubi yadda kika zama just one year da aure".
Kalmar akuyar nan ta bugi Sa'adah, ta kasa hakuri ta ce, ni ce na zama akuya?"
"To mene ne banbancin ki da ita? Ki kalli kanki mana, 'da a hannu, 'da a ciki".
Idon Sa'adah ya cika da kwalla tabbas da gaskiyar Halima irin haihuwar akuya za ta yi.
Kafin ta yi magana, Safina ta tsoma baki ta ce "Ni fa tunda na zauna mamakin Gogel nake yi, ta saki jiki za ta mayar da kanta tamkar irin jakunan matan nan na kauye da ba su san komai ba sai dai su ci, su haihu duk shekara, duk iyashegen da namiji zai musu ba yadda za su yi saboda sun tara garke da shi, yo a wannan karnin wacce macen ce za ta yi irin wannan?"
Halima ta cafe da fa'din "Ba ki ga yadda ta susuce ba? tamkar ba Gogel fine girl din nan ba, duk ta tsofe, ta sakar masa jiki, shi ya tsotseta da daddare, dansa ya yini yana tsotsarta, duk kuma abin da zata ci sai anraba musu da unborn, in and out suke lasar ta, ba dole ta fita a hayyacinta ba".
"Sai ikon Allah, ke da karatu, sai ya gama tsofar da ke, kin daina burge shi, kiga ya dallo sabuwar yarinya, da ilimi ya gogar da ita, tunda kullum yana ganin yan mata sabbin 'kyan 'kyasa".
Hankali Sa'a ba karamin tashi ya yi ba, saboda yadda ta gasgata maganganunsu, mussaman da tasan kullum a cikin ganin tsala tsalan yan matan Jami'a ya ke.
A sanyaye tace "ya zanyi ne? ni kaina ban shirya haihuwa yanzu ba, sannan kuma shine yaki yarda! da nace sai dai a cire"
Dukkansu dariya suka sa mata, sai da suka tsagaita da dariyar! sannan suka ce, mai
yasa da kika yi arbain, ba ki je asibiti an dora ki akan maganin tsarin iyali ba?"
Kafin ta amsa, sun zarce da fadin " kar ki sake yin ganganci irin haka, idan kuma kin ki ji, ba Kya ki gani ba".
"Tuwo Inna ta yi mana zaku ci ko na dafa muku indomie?"
Shiru suka yi tamkar basu ji ba, sai can kuma Safina tace "Ni kam bana cin tuwo".
Halima bata dago ba, tace yi Indomie din kawai, amma plz kisa mana pepper sosai".
Haka ta dafa musu indomie da ta ji albasa da attaruhu, ta hada musu lemon Tang a jug ta fasa kankara ta jefa a ciki.
Sai da suka ci, suka gyatse, suka yi la'asar sannan suka tafi bayan sun jefa mata wasiwasi a zuciyar ta.
Daf da maghrib ya dawo gida, a gurguje yayi wanka ya tafi masallaci, sai da ya dawo, ya dauko musu abincin, suna ci, ya lura Sa'adah ba ta da walwala sosai, ya tambayi ko bata jin dadi ne! ta ce kalau take, ta isar da sakon gaisuwar Inna, da fara'a ya ce "Ina amsawa, ta biyo sawunki kenan? Ina fatan dai kin fa'da mata, bani da alhakin rashin ganin ki a gidansu?"
Kai tsaye ta ce "ko ban fada ba, ai tasan kaine, tunda ka mayar da Ni Akuya".
Maganar ta shige shi, amma sai ya ce ban gane na mayar da ke akuya ba?"
"Eh mana wata biyu da haihuwa ka sake dirka mini wani cikin, ai akuya ce mai hakan".
Ya kalleta soasai ya tabbatar wannan maganar ba daga zuciya da kwakwalwarta ta fito ba, ya kuma tabbatar ba a bakin mahaifiyarta ta ji ba.
Ya numfasa yace " Inna bata yi farincikin ganin ki da cikin ba kenan?"
"Hmm ita da take ta murna wai dama har addu'a take yi mana kar na gado rashin yawan haihuwar su ita da Hajiyar Bichi".
Ya sauke ajiyar zuciya, hankalinsa ya sake tashi, tabbas akwai wacce ta zo take kokarin birkita masa zaman lafiya a gidansa.
A zahiri sai ya murmusa ya ce " Ashe adduar Innace ta sauka akan mu, ba wai akuya na maida ki ba".
Ta tura baki gaba, tana jin ba zata sake yarda ta yi irin wannan gangancin ba a gaba.
A kicin ya ga tray din da aka ci indomie mai dauke da fork guda biyu.
duk yadda akayi wadannan bakin da ta yi ne, suka kitsa mata maganganu, tunda duk boren da ta masa a farko, ai tunanin ta bai bata irin wannan kalamin ba.
Bai sake shan mamaki ba, sai da suka kwanta, ya ji ta ce zasu yi magana, ya ce "Ina jinki".
"Uncle so nake yi nima na cike jamb foam".
Ya ji zuciyar sa ta buga, sai ya danne, cikin dabara dan ya fahimci inda ta dosa.
Ya ce " da kam ina da buri ki yi a wannan shekarar, kafin lokacin da komai zai kammala na samun admission kin yaye Jawad sai ki fara karatun ki, ba wata matsala".
"Yanzu kuma shikenan sai ba zan yi ba?"
Ta fa'da da gatsali.
"Ya sake dannar zuciyarsa ya ce " za ki yi mana, amma dai sai next year".
Ta tunzuro sosai ta ce "kenan sai nan da shekaru biyu kake nufi zan fara?"
Ba ja in ja ya ce " eh".
Jin haka ta fara sakin magaganu "Ni wallahi bazan yarda ba, kafin nan da shekaru biyu only God knows mai zaka mayar da Ni".
Ya yi shiru yana ta neman tsarin Allah ya kare zuciyar sa daga sharrin shaidan da fishi.
Jin ya mata shiru ba'kin cikin ta ya karu,ta fashe masa da kuka mai sauti, tana fadin son kansa ya yi yawa, duk 'kawayenta kowa na karatu sai ita kadaice mai zaman banza da kashe wando.
Rukota yayi zuwa jikinsa tana fizgewa, kan dole ya kwantar da ita, yasa hannun sa ya zagayeta.