← Book details Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 113

Sashe 3

Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yace , "Haba yara mu da muka ga jiya muka yau, ku duba fa duk iya shegen da ta yi akan ba za ku bi shi ba, bai fa iya tafiya ba har sai da ya ga tashinmu, wannan kadai ya isa kowa yasa lunzami a bakinshi akan lamarinsu, suna da yara ne?"

Zainab ce ta ce "Yaro ne daya har ya fara girma, shi suka jewa visiting"

Ya ce, "Ai shike nan magana ta 'kare, ko kowa bai musu sulhu ba, yaron zai zama tsanin afuwa a tsakaninsu, mu yi musu addu'ar fatan alheri, amma soyayya akwai ta"

Aka sake sa dariya ban da Sa'ada da ta yi kicin-kicin da fuska.

Tsohon ya sake cewa, "Ina cewa da za mu zo ita ce a gaban motar nan haka da za mu dawo,har muka zo inda motar ta lalace ita ce a gaban?amma ina ganinsu da za ta shiga gaba ya galla mata harara sai kawai naga ta shige baya."

Gabadaya aka sake dariya har da Sa'ada wadda ita ta karfin halin wannan bawan Allah ne, ita ba ta ga harara ba, ta san kuma tabbas bai yi 'karya ba, kaifin idon Malam ne yasa ta kasa shiga gaban motar wani akan idonsa, sai ta bige da cewa "Lallai Baba ba komi na gode" da haka ta sace ta daina fishi.

Shi ko Malam yana tafe yana ayyana abubuwa masu girma game da lamarin ta, komai nata burgeshi yake, bai ta ba ganin halittar da ke daukan hankalinsa irin surar ta ba, kawai wasu daga cikin halayyarta ke 'dimauta tunaninshi su hana shi zaman lafiya amma duk sanda zai dora idonshi a kanta sai ya ji bai ganin komai da kowa sai ita.

Har yau har gobe yana son ta, amma ta riga ta shayar da shi bakin cikin da zaman aure zai yi wuya tare da su. Har suka iso Kano tunaninta yake idan ya tuna *happy moments* dinsu yayi murmushi, idan ya tuna *though times* dinsu sai ya ja tsaki ko ya furta ya *Salam* ko *SubhanAllah.*

Ba su rabu ba sai da suka zo Gandu ya yi wa direbansu fitila ya wuce, a nan ma sai da Baba ya tsokaneta da cewa

"To Sa'adatu wannan fitilar fa da ya yi bata kowa bace, taki ce!"

Suka hada baki wurin fadin, "Ai kuwa dai Baba!" suna kuma dariya.

```Alkalamin
SURAYYA DAHIRU``` ✍🏼✍🏼

🌺 *HALIN YAU*! 🌺

```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

`

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/

*SADAUKARWA GABA'DAYA GA*
*SADIQ ABUBAKAR*

5-6

Har 'kofar gidan yayarta Sumayya suka kaita dake kan titin Kwankwaso Gandun Albasa, sannan suka juya,
Baba direba, nata jaddada mata ta daina saurin fushi mabudin fitina ne, ta yi godiya, tana cewa su Zainab sai nan da kwana uku za ta dawo unguwar tasu lokacin innarta ta dawo daga tafiyar da ta yi.

Da sallamarta ta isa cikin katafaren falon Sumayya, ba kowa sai TV da take ta babatu hadi da dan dirin AC da ke tashi a hankali, ga 'kamshin *Air Freshner* dake tashi sannu a hankali, take ta ji duk gajiyar da ta kwaso ta taso mata gabadaya.

Dan haka sai kawai ta zube a Kan doguwar kujera ta yi kwanciyar ta ba ta jima da kwanciyar ba, barci mai nauyi ya yi gaba da ita.

Sumayya fitowa tayi daga bangaren maigidan, da a yammacin yau aka sallamosu daga asibiti, ta ganta tana ta barci. Murmushi ta yi tare da cewa, "Oh a 'yar wannan tafiyar ne kika gaji har haka?" Ta gyara mata rigarta da ta 'dage, ta shige kicin don hada tea.

Hayaniyar yaran gidan ne da suka taso da ga lesson wadda takanas aka dauki malamin da zai zo har gida yana musu bita, yasa ta tashi musamman da 'karamar cikinsu ta fada kanta tana fadin, "Mami yaushe kika dawo?"

"Khairat kin san yadda na gaji!" Ta 'daga ta, tana cewa "Ina Yaya Jawad?"

"Ya na lafiya, ya ce duk yana gaishe ku"

Ta sake cewa, "Mami bai ba da komai ki bani ba?"

Daga Sumayya har Sa'adah dariya suka yi yadda Khairat din ta yi.

Jakarta ta bude ta dauko wani dan abu a nade da wrapping paper ta ce, "ga shi nan ni kaina sai da ya ro'ke ni kar na bude tunda ban san ma ya saba, ya dai ce mini zan ga abin Khairat don Allah kar na bude."

Yayansu Ayman wanda shi ma yana da yayu Abba da Khalifa suna Egypt suna karatu, ta nufa tana cewa, "Bude mini yaya!" Nan da nan ko ya hau warwarewa sai ga Lush Cookies Biscuit har guda biyar sai Teddy Bear 🧸 'yar 'karama mai kyau da yar 'karamar takarda an rubuta little Khairat.

Da murna soasai tace "Yaushe to zai dawo Mami?"

Anis ne ya ce, "Sai nan da 6 weeks."

Ta galla mishi harara, "Na tambaye ka ne?" Da yake sa'kuwar shi ce ba su cika jituwa ba. Ta juya ga yayansu,"Yaya Ayman kwana nawa ne a 6 weeks?"

Kai tsaye ya ce mata, "42 days." Da sauri ta ce, "Gobe zan samo stones 42, kullum na dinga minus, ranar da suka 'kare to ranar zai dawo saboda na soya mishi wainar fulawa."
Dukkan su dariya ta ba su, amma Sa'adah mamakin wayonta take, tana kallon Anis tana tuna daidai lokacin haihuwar sa ta shiga matsaloli masu yawa da Malam.

Shekarunta biyar a duniya amma wayonta da azancinta ya zarce na 'yan shekaru bakwai.
mutumiyar Jawad ce sosai ta fi shiri da shi fiye da yayyenta.

Shi ma kuma haka yake ji da ita musamman da shi ba shi da 'kani ko 'kanwa sai ya tattara dukkan 'kaunar da yaya yake yi wa 'kanwarshi a kanta.

*Bayan kwanaki uku*

" Iya Iya dai, na san tabbas daga shigarki ba za ki ce mini wai har kin yi barci mai nauyin da za ki kasa jin kuwwar da wayar ke faman yi ba."

Da kanta ta tashi ta leka, ganinta ta yi tana kwance ta 'kudundune ta rufe fuskarta da dukkan hannayenta,
"Kin san Allah? Idan kika bari na shigo ba ki tashi ba sai na ci mutuncinki, ai na san sarai kina ji na"

Tashin ta yi tana murtsika idanuwanta "Ni fa Inna barci nake yi!" Kafin Innar ta yi magana wayar ta sake daukan ruri a karo na uku dan haka ta kafeta da idanuwa, akan dole Sa'adah ta sa hannu ta amsa wayar.

Sannan Inna ta juya ta fita tana fadin, "Shashasha haka ki ke tunanin za mu bar ki ki yi ta zama? Ai tunda kin gama karatun to kuwa wallahi sai dai ki fito da miji cikin jerin wadanda suke son ki dan ba zan yarda da wannan zaman ba. Haka kawai kowa ya zo ki ce bai yi miki ba, kowa bai miki ba, wanda ya yi mikin kuma bai shirya sake zama dake ba. Amma kin kasa gane gaskiya, kin kasa gane ita mace lokacin ta 'kan'kani ne! Bari Baffan naku ya dawo na gaji da halinki!"

Sa'adah kuwa da alatilas ta dauki wayar Alh. Mamman wanda dan majalisar tarayya ne mai ci a yanzu, ya so ta tun tana budurwa, a lokacin yana dan majalisar dokoki na jaha, shi ne har yau yake ta bibiya, tun lokacin budurcinta ta san komai game da shi.

Mutum ne mai yawan kyauta da kyautatawa, ta tabbatar da hakan, ita kanta ta san ya mata 'barin kudi. Tun a lokacin yana da mata biyu da yara takwas wanda wannan dalilin yana cikin dalilin da ya sa ba tayi marmarin ma auren shi ba, Illa dan ta sami rabonta kawai, to yanzu kuma amaryar ce ta rasu shekaru biyu da suka wuce a wurin haihuwa, shi ne yake ta bin kanta ta maye mishi gurbinta, tunda ya riga ya saba da mace biyu ga kuma tsananin 'kaunarta da yake.

A nata bangaren kuwa ba ta fatan 'kaddara ta 'kaddaro ya zamo miji a gareta shi yasa tun watanni shida da suka shude ta yakice shi a dukkan lamarinta, tunda dai kam ai ta riga da samun rabonta🤔.

Ta yi amfani da alfarmar shi ta cimma burinta, da kuma mallakar kayan 'kawa na alfarma, idan ko hakane dole ta yi gaggawan wullar da shi tun kafin reshe ya juye da mujiya.

Uzirin tana aiki ta ba shi akan za ta 'kira shi anjima, murmushi ya yi ya ce, "Ranar da na ga 'kiran ki a wayata Sa'adah tabbas rana ce mai muhimmanci a raina!"

Ya'ke ta yi tare da fadin, "Aiko idan hakane zan baka mamaki, ka saurare ni zuwa anjima"..

Ba ta jira cewar shi ba ta daste kiran, ta yi wulli da wayar ta na neman tsari da 'kaddarar da za ta hada su zaman aure da wannan mai tulelen ciki.

Kanta ta ji ya cushe musamman yadda Inna ta fara matsa mata a cikin kwanakin nan akan lalle sai ta tsayar da miji cikin manemanta, har zuwa yanzu ba ta jin akwai wani da za ta yi zaman aure da shi kamar Mukhtar Kabir Bichi.

Amma ko shi da ta tabbatar da abu 'daya, ta ha'kura da shi ba dan ba ta so ba sai dan ha'kurin shi yafi.

Ta kuma gamsu ita ke da laifi da kaso mai yawa na 'kaddarar rabuwar su da Abban Jawad, ta tabbatar ya so ta, son da ba algus amma *HALIN YAU* da rudin 'kawaye ya jefa ta cikin kogin nadama.
Irin wanda ake cewa tsalle daya mai jefa mutum rijiya, ya yi dubu bai fito ba! A hankali ta koma ta kwanta tana tariyo rayuwar ta, ta baya, tun kafin haduwarta da Mk Bichi. haduwarsu, aurensu, rabuwarsu, har zuwa yau da take jin duniyar ta yi mata daurin goro.

Ashe 'dan Adam baya rabuwa da matsala? Ashe duk matsalar da mace za ta fuskanta indai tana zaune a dakin aurenta matsalar da sauki, akan matsalar rashin auren, da rabuwa da 'ya'yanta? Wanne tabbas mace keda shi a wannan halin na yau, za ta sake samun damar aure a karo na biyu? Idan ta samu din ma ba za ta kauce wa matsalar *HALIN YAU* ba, ko kuma ta tabbata tana aure-aure.
Chapter 3 · 0% Book details