Sashe 96
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya sake cewa "ki yi zamanki, ko ban aure ki ba, aike kanwata ce da zan baki 'daki a gidana, bare kuma nine na karar miki da komai".
Ya juya ya fice zuwa dakinsa ya dinga ha'da kayansa. Sa'a ce ta ankara da yadda yake ta fito da kayayyakinsa tsakar gida.
Ta fito da sauri, cikin kuka sosai ta zube tana cewa "Na ro'ke ka Baffah ka yi hakuri, kar ka bar mu ina zaka tafi ka barmu?
Muryarsa na rawa ya ce "ko ina ma zan shiga menene matsalar ku, ina ce yanzu kun yi wayewar da zaku iya rike kanku, ku zartar da hukuncin da ni ne zan yi muku biyayya, ba kune zaku mini ba, saboda kuna gamsar da kanku da uwarku, kyale-kyalen duniya fiye da yadda zan yi muku. Dan haka gara na nesanta kaina da ku, tunda ban isa na ce ga yadda za'ayi a gidana ace mini to ba".
Inna da take bakin kofar daki hawayenta ya kasa tsayawa, da sauri ta tsugunna tana cewa "Ka mini hakuri, na yarda na yi kuskure, na yi laifi, ka gafarce Ni, na amince Muutar kaddarar Iya ne, ina fatan ubangiji ya sa karshen bacin ran mu kenan. Ka yi hakuri na ce to, na amince, ka yi yadda kake so da 'yarka".
Dadi ya mamaye zuciyar Baffa ya ce "Na gode miki Salamatu! Ubangiji ya kore shaidanun da suke son tarwatsa mana kyakkawan zaman mu".
Ya kalli Iyah ya ce "A lokacin da na barki ki yi karatun ki, na tabbatar miki bana so, amma na amince miki dan na yarda alfanu ne a gare mu baki'daya. A lokacin na ro'ke ki duk sadda nima zan zo miki da wata bukata ki daure ki mini biyayya ko da ba kya so, sai dan kin san ba zan dora ki akan abu marar alfanu ko cutarwa a gare ki ba".
Kafin ta amsa masa, ya sake zarcewa da fa'din "To yau ina son na roke ki, ki koma dakin ki, burina a duniya bai wuce ace kina dakin mijinki a zaune kin nutsu ba. Mutari shi nake so ya zame miki miji a karo na biyu".
Da rawar murya ta ce "To Baffah! Na ji, na kuma amince zan yi maka biyayya, zan yi ha'kuri na zauna lafiya da shi komai runtsi".
Da murna Baffa ya ke cewa "Na gode miki in sha Allah ba zaki yi nadama ba, ubangiji ya miki Albarka, ya zaunar da ku lafiya, ya baku zuri'a mai albarka".
Ya nisa ya ce " ku shirya gobe zamu je Gogel ki fa'dawa Yaya Ayuba kin amince ba dole na yi miki ba,
Sannan ku samu lokaci ku gano Mutari domin yana jin jiki"
Da sauri lya mike yana cewa "Bari na bi su Alhaji na fa'da musu wannan labarin mai da'di".
Inna ta bi bayansa da ido har ya fice daga gidan, tana ayyana girman soyayyar da yake yiwa Mukhtar.
Kai tsaye gidan Alh Isa ya dosa, a kofar gidan ys tarar da Dr 'Karfi zai shiga mota, ai kuwa ya ce "Mahmouda zo mu shiga, ba tafiya zaka yi ba".
Baffa da murna yake fa'da musu "ai yanzun nan yarinya ta tabbatar masa ta amince, dan haka ku zama cikin shirin zuwa Gogel, a satin nan. Domin a son raina ku tafi da sadaki, a ranar da kuka je a daura auren a huta, kafin ta sake botsarewa saboda na lura kishin banza ta bari yake rinjayar ta".
Daga Baba umaru har Baba Isa kowa ya yi shiru amma suma jinjina alherin bawan Allahn nan suke yi, da karfin son da yake yiwa 'dansu.
Baba Isa ne ya yi karfin halin cewa "Malam Basiru ka dai matsa mata ta amince, gashi muma zamu sake yin son rai, mu amince da abin da ka zartar domin a samu lafiyar yaron nan ta dai-daita, bamu da bakin godiya, abin da zamu ce maka daya ne, da ikon Allah mu kabawa amanar yarinyar nan, mune iyayensa abin da ya faru a farko ba zai sake maimaituwa ba da ikon ubangiji.
Kira mini yarinyar a waya"
Baffa da ya san bashi da fargaba da azama ya fito da wayarsa.
Bugu 'daya ta dauka, ya ce " Baban ku na Na'ibawa ne zai yi magana da ke".
Kalaman kwantar da hankali tare da yabo da kuma girman mai hakuri Alh Isa ya dinga yi Mata, ya sake jaddada mata kar ta sake yin shiru har sai abu ya girmama, komai ya taso matu'kar yafi karfinta to ta sanar da shi zai magance mata da ikon Allah.
Ya rufe maganar da cewa ko kina da korafi domin mun tsayar da kwanaki biyar masu zuwa na daurin auren ku".
Zuciyarta ta buga sosai, cikin rishin kuka ta ce "Ba ni da matsala Baba! Amma zan ro'ke ka dan Allah a bari sai na kintsa sannan ayi tariya".
Da sauri ya ce "Na miki Wannan laminin ki shirya a nutse, ai na san tutsiye Malam Basiru ya Miki ko na ce karfa-karfa, dan haka daga wata daya zuwa wattanni shida ki yi shirinki a hankali, bu'katar mu dama a daura auren hankalin kowa ya kwanta".
A yammacin ranar suka je asibiti ita da Inna har da Sumayya.
Har suka gama zamansu barci yake yi, wannan barcin shike daga hankalin kowa, ya rame kwarai da gaske.
Har waje Hajiyar Bichi ta rako su, tana ta faman godiya, yayin da tausayin Hajiya ya lullube Sa'a, kallonta kawai take yi saboda yadda ta zabge ta yi zuru zuru tabbacin tare suke yin jinyar ita da Mk.
Cike da rauni ta ce musu "Idan har zuwa gobe bai samu sassauci ba, zan tura Ahamad ya dauko Jawad ya zo ya ga ubansa don".. sai kuka ya kwace ta kasa karasawa.
Jikin Inna ya mutu kwarai da gaske, ta dinga bata ha'kuri tare nuna cewa cuta ai ba mutuwa ba ce.
Har suka isa gida ba mai cewa komai saboda ba su zaci haka jikin Mk ya yi tsanani ba.
Washagari cikin ikon ubangiji jikin Mk ya yi sau'ki domin har cire masa oxygen aka yi, sannan ya yini idonsa biyu.
Akan idonsa Inna da Sumayya suka iso, sosai ya ji da'din zuwan su tunda ya lura, sune kanwa uwar gamin wurin tunzura Iyah, sune suka hau dokin na ki, da tallafin su ta sami kwarin guiwar yi masa bore.
Amma da ya tuna wai Sa'adah ya gani da Khalil sai ya ji wani irin kunci ya mamaye zuciyarsa! Tabbas ya yarda a duniyarsa bashi da wani kalubale irin Yaron nan, sannan yadda Khalil ya zama tsalelen saurayi na kerewa Sa'a ya sake tayar masa da hankali kwarai da gaske, domin kowacce mace ta ganshi zata so mallakarsa a matsayin miji.
Ba komai ke nukurkusar Mk ba irin kishin Khalil, a sanadinsa ya rasa aurensa da matar da yake so fiye da kansa, gashi har yanzu basu rabu ba, ya tabbatar Khalil ne ke da nasara akansa, wani irin karfin zuciya ya shige shi, ya dinga kalubalantar kansa meyasa ya kasa mantar da shi a zuciyar Sa'a tamkar yadda ta mantar da shi soyayyar Farida a lokacin da suke tare.
Ya saki ajiyar zuciya yana jin ciwo mai yawa a kirjinsa mafi girma a ciki haushin Sa'adah yake ji kwarai da gaske, a gaban kowa take fa'din bata sonsa, amma dan lalacewa tana soyayya da yaro sa'anta.
Su Innah na zaune Farida ta iso dauke da kwandon zuba abinci. Tana kallon Sumayya ta gane sister din Gogel ce, duk kuwa da Sumayya fara ce tas. Har kasa ta tsugunna ta gaishe su.
Hajiyar Bichi ta ce mata "Kakar Jawad ce da Yayar Mamansa"
Da girmamawa ta sake gaishe su, a ranta sai take ganin Gogel da yayarta dan sun yi kyau ba zai zama abin mamaki ba, domin ko a yanzu da Inna take cikin shekarun tsufa, tana nan da kyaunta, mai kyakkawan jiki ce da yake boye tsufa. Wata'kila haka mahaifin su yake, dan ta lura ba kammanin Inna a tare da Gogel, Sumayya ta fi kama da ita, wanda hakan na alamta cewa mahaifinsu ma ba baya bane.
Sumayya ta 'karewa Farida kallo tsab, takaicin Iyah na kamata da ta dinga kukan Mk ya auri Farida dan ta fita kyau ne, a yau da taga zahairin Farida ba hoto iya fuska ba, sai take ganin ba karamin kerewa Iyah ta yi mata ba. Kawai fararen mutane suna da kwarjini ne ta yadda ake ganin kyaunsu ko da kuwa masu 'karancin kyau ne.
Farida bata dade da isowa ba, su Inna suka yi sallama suka tafi.
Suna isa gida suka tarar da Sa'adah cikin kwalliya ta birgewa, amma tana kwance a falo tana kallo.
Inna ko zama ba ta yi ba, ta hau ta da fa'da "Iyah cewa ki ka yi zaku tarad da mu a asibitin tare da Zainab, ashe karya kika yi mini?"
Cikin rashin damuwa ta ce "na shirya jiranta nake yi".
Kafin Inna ta sake magana Zainab ta kira wayarta, sannan suna jiyo horn dinta tabbacin ta fita, ba shigowa zata yi ba.
Ta mike tana fa'din "gata nan ma, sai mun dawo".
Sumayya ta ce Yanzu irin wannan kwalliya tamkar kin manta asibiti zaki ba gidan biki ba?".
Dake Yan darun akusa suke ta ce "Anty ke kika manta cewa ni wannan ban dauketa kwalliya ba, domin ko a gida haka nake".
Da sauri Sumayya ta ce "gaskiya ce sai na fa'da miki, Hajiyar Bichi na gurin, duka danginsa suna gurin, ki je dubiya cikin irin wannan kwalliyar tamkar me shirin shiga gasar miss Beauty. Ba nadama ba komai a al'amuranki".
Inna ta ce "ta shi ki wanke fuskarki sai ki dauko Hijabin ki dora, ai kinsan yadda hijabi ma yake karbar ki".
Ta mike tana kunkuni wadda yake nuna Sumayya ta fitineta da yawa, dan yanzu ta fi zaman gidanta, to wannan satin ma ba komawa zata yi ba, har sai ta nemeta da kanta.
Yayin da Sumayya ta ce "Ai yanzu kin tabbatar zaki samu burin ranki dole ki tattaro dukkan iyashege ki dawo da shi".
Ai kuwa Sa'aadah ta fasa uban ihun kuka. dai dai lokacin Baffah ya shigo, ya dinga tambayar ba'asin kukan da take yi mai daukar hankali.
Ya juya ya fice zuwa dakinsa ya dinga ha'da kayansa. Sa'a ce ta ankara da yadda yake ta fito da kayayyakinsa tsakar gida.
Ta fito da sauri, cikin kuka sosai ta zube tana cewa "Na ro'ke ka Baffah ka yi hakuri, kar ka bar mu ina zaka tafi ka barmu?
Muryarsa na rawa ya ce "ko ina ma zan shiga menene matsalar ku, ina ce yanzu kun yi wayewar da zaku iya rike kanku, ku zartar da hukuncin da ni ne zan yi muku biyayya, ba kune zaku mini ba, saboda kuna gamsar da kanku da uwarku, kyale-kyalen duniya fiye da yadda zan yi muku. Dan haka gara na nesanta kaina da ku, tunda ban isa na ce ga yadda za'ayi a gidana ace mini to ba".
Inna da take bakin kofar daki hawayenta ya kasa tsayawa, da sauri ta tsugunna tana cewa "Ka mini hakuri, na yarda na yi kuskure, na yi laifi, ka gafarce Ni, na amince Muutar kaddarar Iya ne, ina fatan ubangiji ya sa karshen bacin ran mu kenan. Ka yi hakuri na ce to, na amince, ka yi yadda kake so da 'yarka".
Dadi ya mamaye zuciyar Baffa ya ce "Na gode miki Salamatu! Ubangiji ya kore shaidanun da suke son tarwatsa mana kyakkawan zaman mu".
Ya kalli Iyah ya ce "A lokacin da na barki ki yi karatun ki, na tabbatar miki bana so, amma na amince miki dan na yarda alfanu ne a gare mu baki'daya. A lokacin na ro'ke ki duk sadda nima zan zo miki da wata bukata ki daure ki mini biyayya ko da ba kya so, sai dan kin san ba zan dora ki akan abu marar alfanu ko cutarwa a gare ki ba".
Kafin ta amsa masa, ya sake zarcewa da fa'din "To yau ina son na roke ki, ki koma dakin ki, burina a duniya bai wuce ace kina dakin mijinki a zaune kin nutsu ba. Mutari shi nake so ya zame miki miji a karo na biyu".
Da rawar murya ta ce "To Baffah! Na ji, na kuma amince zan yi maka biyayya, zan yi ha'kuri na zauna lafiya da shi komai runtsi".
Da murna Baffa ya ke cewa "Na gode miki in sha Allah ba zaki yi nadama ba, ubangiji ya miki Albarka, ya zaunar da ku lafiya, ya baku zuri'a mai albarka".
Ya nisa ya ce " ku shirya gobe zamu je Gogel ki fa'dawa Yaya Ayuba kin amince ba dole na yi miki ba,
Sannan ku samu lokaci ku gano Mutari domin yana jin jiki"
Da sauri lya mike yana cewa "Bari na bi su Alhaji na fa'da musu wannan labarin mai da'di".
Inna ta bi bayansa da ido har ya fice daga gidan, tana ayyana girman soyayyar da yake yiwa Mukhtar.
Kai tsaye gidan Alh Isa ya dosa, a kofar gidan ys tarar da Dr 'Karfi zai shiga mota, ai kuwa ya ce "Mahmouda zo mu shiga, ba tafiya zaka yi ba".
Baffa da murna yake fa'da musu "ai yanzun nan yarinya ta tabbatar masa ta amince, dan haka ku zama cikin shirin zuwa Gogel, a satin nan. Domin a son raina ku tafi da sadaki, a ranar da kuka je a daura auren a huta, kafin ta sake botsarewa saboda na lura kishin banza ta bari yake rinjayar ta".
Daga Baba umaru har Baba Isa kowa ya yi shiru amma suma jinjina alherin bawan Allahn nan suke yi, da karfin son da yake yiwa 'dansu.
Baba Isa ne ya yi karfin halin cewa "Malam Basiru ka dai matsa mata ta amince, gashi muma zamu sake yin son rai, mu amince da abin da ka zartar domin a samu lafiyar yaron nan ta dai-daita, bamu da bakin godiya, abin da zamu ce maka daya ne, da ikon Allah mu kabawa amanar yarinyar nan, mune iyayensa abin da ya faru a farko ba zai sake maimaituwa ba da ikon ubangiji.
Kira mini yarinyar a waya"
Baffa da ya san bashi da fargaba da azama ya fito da wayarsa.
Bugu 'daya ta dauka, ya ce " Baban ku na Na'ibawa ne zai yi magana da ke".
Kalaman kwantar da hankali tare da yabo da kuma girman mai hakuri Alh Isa ya dinga yi Mata, ya sake jaddada mata kar ta sake yin shiru har sai abu ya girmama, komai ya taso matu'kar yafi karfinta to ta sanar da shi zai magance mata da ikon Allah.
Ya rufe maganar da cewa ko kina da korafi domin mun tsayar da kwanaki biyar masu zuwa na daurin auren ku".
Zuciyarta ta buga sosai, cikin rishin kuka ta ce "Ba ni da matsala Baba! Amma zan ro'ke ka dan Allah a bari sai na kintsa sannan ayi tariya".
Da sauri ya ce "Na miki Wannan laminin ki shirya a nutse, ai na san tutsiye Malam Basiru ya Miki ko na ce karfa-karfa, dan haka daga wata daya zuwa wattanni shida ki yi shirinki a hankali, bu'katar mu dama a daura auren hankalin kowa ya kwanta".
A yammacin ranar suka je asibiti ita da Inna har da Sumayya.
Har suka gama zamansu barci yake yi, wannan barcin shike daga hankalin kowa, ya rame kwarai da gaske.
Har waje Hajiyar Bichi ta rako su, tana ta faman godiya, yayin da tausayin Hajiya ya lullube Sa'a, kallonta kawai take yi saboda yadda ta zabge ta yi zuru zuru tabbacin tare suke yin jinyar ita da Mk.
Cike da rauni ta ce musu "Idan har zuwa gobe bai samu sassauci ba, zan tura Ahamad ya dauko Jawad ya zo ya ga ubansa don".. sai kuka ya kwace ta kasa karasawa.
Jikin Inna ya mutu kwarai da gaske, ta dinga bata ha'kuri tare nuna cewa cuta ai ba mutuwa ba ce.
Har suka isa gida ba mai cewa komai saboda ba su zaci haka jikin Mk ya yi tsanani ba.
Washagari cikin ikon ubangiji jikin Mk ya yi sau'ki domin har cire masa oxygen aka yi, sannan ya yini idonsa biyu.
Akan idonsa Inna da Sumayya suka iso, sosai ya ji da'din zuwan su tunda ya lura, sune kanwa uwar gamin wurin tunzura Iyah, sune suka hau dokin na ki, da tallafin su ta sami kwarin guiwar yi masa bore.
Amma da ya tuna wai Sa'adah ya gani da Khalil sai ya ji wani irin kunci ya mamaye zuciyarsa! Tabbas ya yarda a duniyarsa bashi da wani kalubale irin Yaron nan, sannan yadda Khalil ya zama tsalelen saurayi na kerewa Sa'a ya sake tayar masa da hankali kwarai da gaske, domin kowacce mace ta ganshi zata so mallakarsa a matsayin miji.
Ba komai ke nukurkusar Mk ba irin kishin Khalil, a sanadinsa ya rasa aurensa da matar da yake so fiye da kansa, gashi har yanzu basu rabu ba, ya tabbatar Khalil ne ke da nasara akansa, wani irin karfin zuciya ya shige shi, ya dinga kalubalantar kansa meyasa ya kasa mantar da shi a zuciyar Sa'a tamkar yadda ta mantar da shi soyayyar Farida a lokacin da suke tare.
Ya saki ajiyar zuciya yana jin ciwo mai yawa a kirjinsa mafi girma a ciki haushin Sa'adah yake ji kwarai da gaske, a gaban kowa take fa'din bata sonsa, amma dan lalacewa tana soyayya da yaro sa'anta.
Su Innah na zaune Farida ta iso dauke da kwandon zuba abinci. Tana kallon Sumayya ta gane sister din Gogel ce, duk kuwa da Sumayya fara ce tas. Har kasa ta tsugunna ta gaishe su.
Hajiyar Bichi ta ce mata "Kakar Jawad ce da Yayar Mamansa"
Da girmamawa ta sake gaishe su, a ranta sai take ganin Gogel da yayarta dan sun yi kyau ba zai zama abin mamaki ba, domin ko a yanzu da Inna take cikin shekarun tsufa, tana nan da kyaunta, mai kyakkawan jiki ce da yake boye tsufa. Wata'kila haka mahaifin su yake, dan ta lura ba kammanin Inna a tare da Gogel, Sumayya ta fi kama da ita, wanda hakan na alamta cewa mahaifinsu ma ba baya bane.
Sumayya ta 'karewa Farida kallo tsab, takaicin Iyah na kamata da ta dinga kukan Mk ya auri Farida dan ta fita kyau ne, a yau da taga zahairin Farida ba hoto iya fuska ba, sai take ganin ba karamin kerewa Iyah ta yi mata ba. Kawai fararen mutane suna da kwarjini ne ta yadda ake ganin kyaunsu ko da kuwa masu 'karancin kyau ne.
Farida bata dade da isowa ba, su Inna suka yi sallama suka tafi.
Suna isa gida suka tarar da Sa'adah cikin kwalliya ta birgewa, amma tana kwance a falo tana kallo.
Inna ko zama ba ta yi ba, ta hau ta da fa'da "Iyah cewa ki ka yi zaku tarad da mu a asibitin tare da Zainab, ashe karya kika yi mini?"
Cikin rashin damuwa ta ce "na shirya jiranta nake yi".
Kafin Inna ta sake magana Zainab ta kira wayarta, sannan suna jiyo horn dinta tabbacin ta fita, ba shigowa zata yi ba.
Ta mike tana fa'din "gata nan ma, sai mun dawo".
Sumayya ta ce Yanzu irin wannan kwalliya tamkar kin manta asibiti zaki ba gidan biki ba?".
Dake Yan darun akusa suke ta ce "Anty ke kika manta cewa ni wannan ban dauketa kwalliya ba, domin ko a gida haka nake".
Da sauri Sumayya ta ce "gaskiya ce sai na fa'da miki, Hajiyar Bichi na gurin, duka danginsa suna gurin, ki je dubiya cikin irin wannan kwalliyar tamkar me shirin shiga gasar miss Beauty. Ba nadama ba komai a al'amuranki".
Inna ta ce "ta shi ki wanke fuskarki sai ki dauko Hijabin ki dora, ai kinsan yadda hijabi ma yake karbar ki".
Ta mike tana kunkuni wadda yake nuna Sumayya ta fitineta da yawa, dan yanzu ta fi zaman gidanta, to wannan satin ma ba komawa zata yi ba, har sai ta nemeta da kanta.
Yayin da Sumayya ta ce "Ai yanzu kin tabbatar zaki samu burin ranki dole ki tattaro dukkan iyashege ki dawo da shi".
Ai kuwa Sa'aadah ta fasa uban ihun kuka. dai dai lokacin Baffah ya shigo, ya dinga tambayar ba'asin kukan da take yi mai daukar hankali.