Sashe 77
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Koda ya kammala kifa ta ya yi akan cikinsa fatar jikinsu na manne, yana jin nisha'di sosai ya dinga mata addu'a, yana gode ma ubangiji na yadda duk shine ya fara bude matan da ya aura, ya tsare kansa bai taba Zina ba, ubangijinsa kuma sai ya mutuntata shi ta hanyar bashi katangaggun mata.
Zuciyarsa ta buga da ya tuno Sa'a yasan sharrin zuciya ne da yake jin tamkar tana ha'intarsa ne, amma shi da kansa yasan zai yi wahalar gaske ta aikata wannan al'amarin.
Jikinsa ya dinga bari har Farida ta dinga jin barin, saboda yadda ya ke jin wani iri abu da baisan dalilinsa ba, yau gashi da Farida a cikin yanayin da Sa'adah kawai ya ta'ba tsintar kansa a ciki, ko ya take ji a dalilin aurensa yasan idan itace ta yi aure tabbas sai ya kwanta a gadon likita.
A sanyaye Farida ta ce "baka da lafiya ne? jikinka na rawa fa".
Murya a dashe ya ce" farin cikin yadda na same ki ne, duk son ki ne yake kidima Ni"
A ransa kuma fa'di yaushe zan iya fa'da miki abin da ya kidima ni ai ya zama tamkar cin fusaka ne, gangar jikinmu a hade amma tunanina da zuciyata na wani waje daban.
Ita kuma zuciyarta ta yi fari kal har tana ganin sannu a hankali zata iya mantar da shi Gogel kamar yadda Gogel din tasa ya manta da lamarinta a baya.
Yini zur Mk ya yi da Farida bai yarda ya mayar da ita ba sai bayan Isha, wadda sai da ta yi kuka, domin kuwa da murje idonsa zai yi ya kwana da amaryarsa, kafin su tafi ta fahimci mabukaci ne na gaske, domin sai da ya sake yin second round ,sannan yana daukar lokaci yana abu 'daya tabbacin yana da lafiya yana kuma kula da lafiyarsa.
A iya wannan awannin da suka yi sai da Farida ta dinga yiwa Iyah jajen rashin mijin da iya sarrafa mace, lalle Gogel jaruma ce da ta iya shafe wannan lokaci babu zumar da ya 'dade yana lasa mata, ita yau kadai da suka kasance da shi addu'a take yi, da neman tsarin abin da zai rabata da Mk.
Fata take ta kasance da shi muddin rai, zata yi dukkan ladabi da biyayyar da zata dauwamar da ita a zuciyarsa, zata yi ha'kuri da duk wani abin da baya so koda ita tana so, matu'kar zasu samu zaman lafiya , ta kuma rayu da shi, idan har zai iya rabuwa da Gogel tsawon lokaci bai waiwaye ta ba, to ta tabbatar ita idan ta yi kuskuren da suka rabu shafeta zai yi gaba'daya.
Suna tafe yana tuki yana ta mata hira da suke nuni da kololuwar jin dadin yadda ya sameta, ita kuma tana ta murmusawa alamun tana Jin dadin yabawar ta shi, a ranta tana fa'din karatu a Jami'a baya sa mace ta lalace sai idan dama lalatacciya ce.
***
Har Mk ya tafi ba su hadu da Sa'adah ba, domin ko da yaje gidan ana gobe zai tafi, ya fadawa Baffah zai tafi amma nan da sati biyu su Jawad za su bishi, cikin karfin hali Baffa ya yi masa addu'a tare da fatan alheri.
Inna kuwa ba yabo ba fallasa ta amsa gaisuwar sa, tare da yi masa fatan alheri a aurensa.
Ya jima a zaune bai ji Inna ta hau Kiran Iyah ba, dama ita ce take yin hakan a kokarinta na su dinga gaisawa har a samu ayi sulhu, amma wannan karon bai ji hakan ba, illah shigewa daki da Inna ta yi ta bar shi da Baffah akan tabarma.
Yayin da ita kuma Sa'a tana kwance akan gado tana fama da zugin zuciya duk da dai Alhamdulillah ansamu cigaba kwarai da gaske akan kwanakin ukun da suka shude.
Tana jinsa Amma sai ta ji a duniya ba halittar da bata son gani kamar Mk, tabbas ya wulakanta ta, ya tozarta mafi munin tozarci, hawaye ya dinga silalowa ta gefen kunnenta, ta dinga hasashen me ya Mata na alheri ne, me ya mata na kyautatawa wadda bai cancanci ta ji wannan tsanar da take ji akansa ba, ta gama duk lissafinta ta yi alkalanci, ta yarda a zamansu bai zalunce ta ba, ta kuma gamsu ya kyautata mata, ta kuma gasgata itace ta janyo komai.
Amma kuma hukuncin da ya dauka akanta ya yi tsauri matu'ka da gaske, zargin da ya jefeta da shi ya ketare iyaka, haka nan kin mayar da ita, kafin ya sake aure tozarci ne Babba ya mata, kishi ya daure mata kirji, duk irin alheri da dawainiyar da ya mata har bayan ya rabu da ita a yanzu duk sai ya tashi a banza a idonta, tana jin ba wani alherinsa data sani da zai lullube cin mutuncin da ya mata, a kuma wannan lokacin ta yanke duk wata mu'amala da shi, tana jin idan har ta sake yiwa Mk kallon masoyi, ko kallon Rahma tabbas ta zama asararriya.
Kunya sosai ta hana Mk tambayar Baffah Sa'a! Sai ya buge da sake bawa Baffah hakuri, tare da neman afuwa.
Duk da a ran Baffa ba ya jin da'din yadda yake ganin Iyah adalilin Mukhtar, sai ya ce " Ba komai Mutari, har yau kuma ban kullace ka ba, kawai dai ina son ka ka daina mini kallon wannan matsalar zata lalata amincin da ke tsakanina da Kai, kallon uba kake mini, Nima kallon 'da nake yi maka, har abada mun hadu ga Jawad nan a tsakanin mu".
Jikin Mk ya sake yin sanyi tunda a da cewa yake yi, idan da saura zama a tsakanin ka da Iyah da kanku zaku shirya kanku, bana ji a jikina an rabu kenaan ba, sai kuma yau ya ce ga Jawad a tsakani, kenan Baffah ya karaya ya daina jin zasu sake zama ma'aurata a tsakaninsa da Iyah.
Ya dade zaune Baffa na ta yi masa nasihar ya kula da amanar yarinyar da aka bashi tunda zai dauketa ne ya kaita wata duniyar da ba ta san kowa ba sai shi, sannan ya sa ido sosai akan Jawad kar ya bari ya koyo dabi'un yahudu wal Nasar😀
Da kyar ya mike ya na kallon dakin Sa'adah da fitila a kunne tabbacin idonta biyu, ya tuna idan ya zo gidan ta dinga sintiri tsakanin dakinta da tsakar gida, ta dinga bare bare kenan, ba ita ba hatta mahaifiyarta rawar jiki take yi, ta dinga fa'din Iyah kaza, zo ki kawo masa kaza mana, amma yau duk sun yi likimo tabbacin sun watsa shi a kwandon shara.p
A sanyaye sosai ya bar gidan.
Washagari kuwa ya bi jirgin Mangal air zuwa Lagos daga can ya shiga jirgin arik air zuwa kasar Birtaniya.
Haka Sa'adah ta cigaba da jinyar zuciyarta, tana samun karfin guiwa wurin mahaifanta da Sumayya, domin Baffah da ya ga sun hade masa kai a gidan dole ya ajiye powaer sa ta maigida ya lallashe su da kalmomi masu laushi, da kuma sanin muhimmancin hakuri.
Ya sake fa'da musu ba su fi shi takaicin auren Mukhtar ba, amma tunda shari'a bata hana shi ba, akan me shi zai kullace shi?
Ya rufe da cewa "kuna ganin laifina dan ban roki Mutari ya zauna da ke akan dole ba, alakawari na yi ba zan bada auren 'yata ba sai a inda nasan za ta yi daraja, a farko da yake so ai na bashi, idan kum zaki fadi gaskiya ai ya ri'ke ki da daraja! a yanzu kuma, da baya so, bashi da abin da zan kalla da zan nemi ya zauna da ke akan tilas, hakuri wuya ne da shi, idan aka daure sannu a hankali za'a cimma buri".
Ya nisa ya sake 'daure su da cewa "A zatona Salamatu, da ke da yaran da kika haifa mini da kuma duk abin da kuka mallaka zan yi iko da ku kai tsaye, ba tare da jin shakku ko fargaba ba, amma tunda laifine dan na yi ikon da abin da yake mallakin Iyah ne to ku mini afuwa, Iyah ta bini bashi in sha Allah zan biya a hankali"
Kunyar kalamansa suka kama su mussaman Innah da ta bari hankalinta ya kwace akan wannan lamarin. A ranta ta dinga fa'din babbar jarrabawar da aka yiwa mata kishi ne, domin da yawa Mata sun halaka adalilin kishi, da yawa sun rasa Imani, ubangiji ka tsare mu ka sau'ka'ka mana.
Hakuri suka bashi, Innah ta ce "Ba siyar da filin bane ya ta'ba ni ba, yadda ka shiga cikin lamarin auren ka yi kane kane ne ya kidima ni, amma ka mini afuwa wallahi ban taba jin bin da ya dama mini lissafi irin halin da na ga Iyah a ciki ba, amma Alhamdulillah komai ai ya wuce ina rokon kar Allah ya sake maimata mana wannan wakiar".
Sa'adah ta nisa ta ce " Dayan filin ma na barka maka Baffa tsakani da Allah bana so, tunda na mallakesu ne adalilin Mukhtar. Kawai so nake ka daina nunawa ya fini a gurin ka, sannan ka mini afuwa akan komai ka daina fushi da ni, domin a yanzu Ni Mukhtar ya zalunta".
Ya yi murmushi ya ce " ko Sumayya ba ta fiki ba Iyata, amma ina son ki gane gaskiya ko kuna tare da Mutari ba zan 'ki shiga hidimar auren sa ba, domin ya mini alkairori daban daban da bazan mance su ba, duk girman kuskure kuwa bai kamata Dan adam ya shafawa idonsa toka ya mance alheri ba, nasani hukuncin da ya dauka akan ki ya yi tsauri da yawa, adalcin da nake yi masa shine ban san mai kika yi masa ba, sannan auren da yayi ba zaluntarki ya yi ba, domin kuwa ko kuna tare zai yi aure shari'a ta bashi dama, idan yana so kuma zai iya adalci. Fatana ki kwantar da hankalin, ki yi hakuri in sha Allah komai zai daidaita miki, Na da'de da ya yafe miki Iyah, fatana ki bu'de zuciyarki ki fuskanci goben ki, sai kinyi nazari hadi da tsinkaye masu zurfi sannan gobenki zata inganta, na yarda da nutsuwar ki a yanzu, na kuma gamsu a kame kike dan haka bana fargabar zamanki!
Zuciyarsa ta buga da ya tuno Sa'a yasan sharrin zuciya ne da yake jin tamkar tana ha'intarsa ne, amma shi da kansa yasan zai yi wahalar gaske ta aikata wannan al'amarin.
Jikinsa ya dinga bari har Farida ta dinga jin barin, saboda yadda ya ke jin wani iri abu da baisan dalilinsa ba, yau gashi da Farida a cikin yanayin da Sa'adah kawai ya ta'ba tsintar kansa a ciki, ko ya take ji a dalilin aurensa yasan idan itace ta yi aure tabbas sai ya kwanta a gadon likita.
A sanyaye Farida ta ce "baka da lafiya ne? jikinka na rawa fa".
Murya a dashe ya ce" farin cikin yadda na same ki ne, duk son ki ne yake kidima Ni"
A ransa kuma fa'di yaushe zan iya fa'da miki abin da ya kidima ni ai ya zama tamkar cin fusaka ne, gangar jikinmu a hade amma tunanina da zuciyata na wani waje daban.
Ita kuma zuciyarta ta yi fari kal har tana ganin sannu a hankali zata iya mantar da shi Gogel kamar yadda Gogel din tasa ya manta da lamarinta a baya.
Yini zur Mk ya yi da Farida bai yarda ya mayar da ita ba sai bayan Isha, wadda sai da ta yi kuka, domin kuwa da murje idonsa zai yi ya kwana da amaryarsa, kafin su tafi ta fahimci mabukaci ne na gaske, domin sai da ya sake yin second round ,sannan yana daukar lokaci yana abu 'daya tabbacin yana da lafiya yana kuma kula da lafiyarsa.
A iya wannan awannin da suka yi sai da Farida ta dinga yiwa Iyah jajen rashin mijin da iya sarrafa mace, lalle Gogel jaruma ce da ta iya shafe wannan lokaci babu zumar da ya 'dade yana lasa mata, ita yau kadai da suka kasance da shi addu'a take yi, da neman tsarin abin da zai rabata da Mk.
Fata take ta kasance da shi muddin rai, zata yi dukkan ladabi da biyayyar da zata dauwamar da ita a zuciyarsa, zata yi ha'kuri da duk wani abin da baya so koda ita tana so, matu'kar zasu samu zaman lafiya , ta kuma rayu da shi, idan har zai iya rabuwa da Gogel tsawon lokaci bai waiwaye ta ba, to ta tabbatar ita idan ta yi kuskuren da suka rabu shafeta zai yi gaba'daya.
Suna tafe yana tuki yana ta mata hira da suke nuni da kololuwar jin dadin yadda ya sameta, ita kuma tana ta murmusawa alamun tana Jin dadin yabawar ta shi, a ranta tana fa'din karatu a Jami'a baya sa mace ta lalace sai idan dama lalatacciya ce.
***
Har Mk ya tafi ba su hadu da Sa'adah ba, domin ko da yaje gidan ana gobe zai tafi, ya fadawa Baffah zai tafi amma nan da sati biyu su Jawad za su bishi, cikin karfin hali Baffa ya yi masa addu'a tare da fatan alheri.
Inna kuwa ba yabo ba fallasa ta amsa gaisuwar sa, tare da yi masa fatan alheri a aurensa.
Ya jima a zaune bai ji Inna ta hau Kiran Iyah ba, dama ita ce take yin hakan a kokarinta na su dinga gaisawa har a samu ayi sulhu, amma wannan karon bai ji hakan ba, illah shigewa daki da Inna ta yi ta bar shi da Baffah akan tabarma.
Yayin da ita kuma Sa'a tana kwance akan gado tana fama da zugin zuciya duk da dai Alhamdulillah ansamu cigaba kwarai da gaske akan kwanakin ukun da suka shude.
Tana jinsa Amma sai ta ji a duniya ba halittar da bata son gani kamar Mk, tabbas ya wulakanta ta, ya tozarta mafi munin tozarci, hawaye ya dinga silalowa ta gefen kunnenta, ta dinga hasashen me ya Mata na alheri ne, me ya mata na kyautatawa wadda bai cancanci ta ji wannan tsanar da take ji akansa ba, ta gama duk lissafinta ta yi alkalanci, ta yarda a zamansu bai zalunce ta ba, ta kuma gamsu ya kyautata mata, ta kuma gasgata itace ta janyo komai.
Amma kuma hukuncin da ya dauka akanta ya yi tsauri matu'ka da gaske, zargin da ya jefeta da shi ya ketare iyaka, haka nan kin mayar da ita, kafin ya sake aure tozarci ne Babba ya mata, kishi ya daure mata kirji, duk irin alheri da dawainiyar da ya mata har bayan ya rabu da ita a yanzu duk sai ya tashi a banza a idonta, tana jin ba wani alherinsa data sani da zai lullube cin mutuncin da ya mata, a kuma wannan lokacin ta yanke duk wata mu'amala da shi, tana jin idan har ta sake yiwa Mk kallon masoyi, ko kallon Rahma tabbas ta zama asararriya.
Kunya sosai ta hana Mk tambayar Baffah Sa'a! Sai ya buge da sake bawa Baffah hakuri, tare da neman afuwa.
Duk da a ran Baffa ba ya jin da'din yadda yake ganin Iyah adalilin Mukhtar, sai ya ce " Ba komai Mutari, har yau kuma ban kullace ka ba, kawai dai ina son ka ka daina mini kallon wannan matsalar zata lalata amincin da ke tsakanina da Kai, kallon uba kake mini, Nima kallon 'da nake yi maka, har abada mun hadu ga Jawad nan a tsakanin mu".
Jikin Mk ya sake yin sanyi tunda a da cewa yake yi, idan da saura zama a tsakanin ka da Iyah da kanku zaku shirya kanku, bana ji a jikina an rabu kenaan ba, sai kuma yau ya ce ga Jawad a tsakani, kenan Baffah ya karaya ya daina jin zasu sake zama ma'aurata a tsakaninsa da Iyah.
Ya dade zaune Baffa na ta yi masa nasihar ya kula da amanar yarinyar da aka bashi tunda zai dauketa ne ya kaita wata duniyar da ba ta san kowa ba sai shi, sannan ya sa ido sosai akan Jawad kar ya bari ya koyo dabi'un yahudu wal Nasar😀
Da kyar ya mike ya na kallon dakin Sa'adah da fitila a kunne tabbacin idonta biyu, ya tuna idan ya zo gidan ta dinga sintiri tsakanin dakinta da tsakar gida, ta dinga bare bare kenan, ba ita ba hatta mahaifiyarta rawar jiki take yi, ta dinga fa'din Iyah kaza, zo ki kawo masa kaza mana, amma yau duk sun yi likimo tabbacin sun watsa shi a kwandon shara.p
A sanyaye sosai ya bar gidan.
Washagari kuwa ya bi jirgin Mangal air zuwa Lagos daga can ya shiga jirgin arik air zuwa kasar Birtaniya.
Haka Sa'adah ta cigaba da jinyar zuciyarta, tana samun karfin guiwa wurin mahaifanta da Sumayya, domin Baffah da ya ga sun hade masa kai a gidan dole ya ajiye powaer sa ta maigida ya lallashe su da kalmomi masu laushi, da kuma sanin muhimmancin hakuri.
Ya sake fa'da musu ba su fi shi takaicin auren Mukhtar ba, amma tunda shari'a bata hana shi ba, akan me shi zai kullace shi?
Ya rufe da cewa "kuna ganin laifina dan ban roki Mutari ya zauna da ke akan dole ba, alakawari na yi ba zan bada auren 'yata ba sai a inda nasan za ta yi daraja, a farko da yake so ai na bashi, idan kum zaki fadi gaskiya ai ya ri'ke ki da daraja! a yanzu kuma, da baya so, bashi da abin da zan kalla da zan nemi ya zauna da ke akan tilas, hakuri wuya ne da shi, idan aka daure sannu a hankali za'a cimma buri".
Ya nisa ya sake 'daure su da cewa "A zatona Salamatu, da ke da yaran da kika haifa mini da kuma duk abin da kuka mallaka zan yi iko da ku kai tsaye, ba tare da jin shakku ko fargaba ba, amma tunda laifine dan na yi ikon da abin da yake mallakin Iyah ne to ku mini afuwa, Iyah ta bini bashi in sha Allah zan biya a hankali"
Kunyar kalamansa suka kama su mussaman Innah da ta bari hankalinta ya kwace akan wannan lamarin. A ranta ta dinga fa'din babbar jarrabawar da aka yiwa mata kishi ne, domin da yawa Mata sun halaka adalilin kishi, da yawa sun rasa Imani, ubangiji ka tsare mu ka sau'ka'ka mana.
Hakuri suka bashi, Innah ta ce "Ba siyar da filin bane ya ta'ba ni ba, yadda ka shiga cikin lamarin auren ka yi kane kane ne ya kidima ni, amma ka mini afuwa wallahi ban taba jin bin da ya dama mini lissafi irin halin da na ga Iyah a ciki ba, amma Alhamdulillah komai ai ya wuce ina rokon kar Allah ya sake maimata mana wannan wakiar".
Sa'adah ta nisa ta ce " Dayan filin ma na barka maka Baffa tsakani da Allah bana so, tunda na mallakesu ne adalilin Mukhtar. Kawai so nake ka daina nunawa ya fini a gurin ka, sannan ka mini afuwa akan komai ka daina fushi da ni, domin a yanzu Ni Mukhtar ya zalunta".
Ya yi murmushi ya ce " ko Sumayya ba ta fiki ba Iyata, amma ina son ki gane gaskiya ko kuna tare da Mutari ba zan 'ki shiga hidimar auren sa ba, domin ya mini alkairori daban daban da bazan mance su ba, duk girman kuskure kuwa bai kamata Dan adam ya shafawa idonsa toka ya mance alheri ba, nasani hukuncin da ya dauka akan ki ya yi tsauri da yawa, adalcin da nake yi masa shine ban san mai kika yi masa ba, sannan auren da yayi ba zaluntarki ya yi ba, domin kuwa ko kuna tare zai yi aure shari'a ta bashi dama, idan yana so kuma zai iya adalci. Fatana ki kwantar da hankalin, ki yi hakuri in sha Allah komai zai daidaita miki, Na da'de da ya yafe miki Iyah, fatana ki bu'de zuciyarki ki fuskanci goben ki, sai kinyi nazari hadi da tsinkaye masu zurfi sannan gobenki zata inganta, na yarda da nutsuwar ki a yanzu, na kuma gamsu a kame kike dan haka bana fargabar zamanki!