Sashe 72
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bai yi kasa a guiwa ba ya je asibitjn data ke kwance da niyyan dubata, ai kuwa mahaifin ta yana asbitin suka gaisa, Farida ta gabatar da shi tare da cewa "Dadi yau ga Uncle Mukhtar a gabanka".
Ai kuwa budar bakin Dadi sai cewa yayi "madallah da Mukhtar ganin ka yau na ji ka shiga Raina Kamar yadda ka shiga ka kwanta a zuciyar 'diyata, na gode da alherin ka, ka turo mini waliyyan ka, na baka auren Farida ba tare da neman komai daga gurinka ba".
Daga Farida har Mk abin ya zo musu tamkar saukar aradu, barin Mk da yaji tamkar mummunar kaddarace ta kawo shi asibitin, ba dan ba ya son Farida ba, sai don bai shirya aure a yanzu ba, bai shirya aurenta ba, a yanzu da ya gama sanin kansa ya fahimci mata masu duhu sunfi burge shi fiye da farare 'Kal, yana jin tsoron kar ya kasa yi mata adalci, tunda yasan ba karamin so take masa ba.
Cikin hikima irin ta manya Alh Nasir ya tisa Mk a gaba ya bashi lambar Alh Isa a matsayin Babansa dan su Baba umaru sama sama suke da shi adalilin sakin da ya yiwa Sa'a sun kuma lashi takobin matu'kar ba Sa'a zai dawo da ita ba, ba za su sake neman masa aure ya kunya ta su ba.
Cikin cire girman kai mahaifin Farida ya gaisa da Alh Isa ya zarce da cewa "yaron ka na bawa matar aure amma na ga tsoron tunkarar ku da maganar ya ke yi, shiyasa Ni na gabatar maka da maganar, na fada maka cewar nutsuwar danka ta sa na bashi kyautar 'yata mafi soyuwa da fatan zaka karbar masa".
Matu'kar mutum yasan daddako wa za'a yiwa haka ya ce ba zai karba ba?
Jikin Alh Isa ya mutu ya ce "kyuatar dan mutum ba mahalu'kin da za'a bawa ya tankwabar mun gode zan zo in sha Allah da kaina zan zo na karbar masa na kuma yi godiya.
Washagari Alh Isa da Mk suka tarar da Baffan Sa'a suka masa bayanin Halin da ake ciki, idan ya ce bai ji rashin da'di ba ya yi 'karya, idan ya ce bai so Iyah ce zata koma 'dakinta ba yayi karya, hakan nan idan ya ce mahaifin Farida yasan ciwon kansaa Nan ma bai yi karya ba.
Amma ko dan ya ramawa Mk kadan cikin alherin da tunda yasan shi yake masa ba gajiya har yau yasa shi cewa "madallah jibin idan za ku tafi ku biyo ku dauke ni da ni za'a je neman aure tare da godiya ina fatan alheri tare da fatan ta kasance abokiyar arzikin ka ce".
Kafin jibin kuwa sai da Baffa ya siyar guda cikin filayen nan wadda kudin daya ya zarta kudin duka biyun sadda aka siya, sosai gurin ya yi daraja adalilin anata gine gine. Dubu 'dari uku da talatin aka siyar.
Da daddare ya Kira Mk ya danka masa dubu dari biyu akan ya bawa Alh Isa dan akai gidan su Farida.
Kunya ta kama Mk ya ki karba, ai kuwa Baffa ya rantse sai ya karba sai idan ya raina me ko yana ganin bashi da arzikin da zai masa alheri.
Da sauri Mk ya sa duka hannunsa ya karba yana cewa "Haba Baffa, mahaifana ne kawai suka mini alheri sama da kai, har yau kuma banga dattijon arziki sama da aki a idona ba gani na yi na doara maka nauyi mai yawa Baffa! Ina rokon na raba biyu na dauki rabi".
"Duka na baka Mutari sadaki ne haka nake so ka bayar dan su san iyayen ka sun san alheri, ko da sunce basu bu'katar komai daga garemu dole ka bada sadaki, burina ace na biya maka fiye da haka, ban son Alh Isa ya gane ni na bada kudin shiyasa na baka a hannunka da sai munje zan bayar, sannan shine wakilinka dole shine mai bayarwa".
Zuciyar Mk ta karye ya yi kasa da kansa yana jin hawaye na Shirin zubowa.
Haka kuwa! Da Baffah aka kai kudin auren Mk akasa 'daurin aure sati mai zuwa, tunda ba tarewa zata yi ba, sai sun dawo, can ingila zasu tafi.
Har zuciyar Alh Isa yake jin rashin da'di, har jinyar kwana biyu ya yi adalilin kunyar Malam Basiru da takaicin Mukhtar.
Haka kuma Mk da yake jin tamkar 'kasa ta tsage ya shige dan tsananin kunyar Baffah.
*SURAYYA DAHIRU*
✍️✍️.
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
Na
*SURAYYA DAHIRU GWARAM*.
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*
*Comments din ku na sani nisha'di kwarai da gaske! Na gode muku ubangiji ya bamu damuna mai albarka*.
*Gaisuwa da fatan alheri ga dukkan yan KUNGIYAR LAFAZEE WRITERS*.
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*
85-86.
Murna wurin Farida tamkar ta zuba ruwa a kasa ta sha, ta godewa Allah, ta godewa mahaifinta Ashe da gaske yake da ya ce sai inda karfinsa ya kare wurin nemo mata farin cikinta. Ta tuno sadda Mk ya auri Sa'a irin kukan da ta yi a kirjin mahaifin ta, yana lallashinta da kalmomi masu da'di, tare da al'kawarin matu'kar yana raye sai ta auri wadda ya fi Mukhtar, ko kuma shi Mukhtar din kansa. A wanccan lokacin bata gasgata ba, kawai ta dauka saboda ya kwantar Mata da hankali ne.
"Wa yake da uba irin nawa?" ta furta a fili, hawaye na zirarowa wadda ta tabbatar sune na karshe akan rashin Masoyi.
Sa'a kuwa ba tasan me yake faruwa ba, har sai da auren ya rage kwanaki uku, Zainab ta gano musu a group, da farko bata gasgata ba, amma da yake Rukayya Mustapha aminyar Faridan suna dan gaisawa da Zainab sama sama tunda duk class mate ne, anan ta tabbatar jibi Uncle Mk Bichi zai angwance da Farida Torondi.
Hankalin Zainab ya kasa kwanciya, a gigice ta tafi gidan su Sa'a amma da ta lura Sa'adah bata san mai yake going ba, sai ta fasa fa'da dan kuwa be kamata ace a bakinta aminiyarta zata ji wannan ba'kin labarin ba.
Tasan da tana da waya da ta ji.
Baffah da kansa ya fa'da wa Innah da Iyah auren Mk, ba Sa'a kawai ba hatta Inna kuka ta fashe da shi mussaman da ya tabbatar musu ya siyar da fili daya cikin filayen Sa'a ya biyawa Mk sadakin auren.
Sosai suka tayar masa da hankalin sa domin irin kukan da suke tamkar ance Sumayya ta yi mutuwar fuju'a ne.
Har cikin ran Inna take jin wani irin azabben kishi na ratsa ta, bata
san kishi ba sai a ranar tunda ta wanzu ita kadai ne a wurin mijinta
A kuma ranar ta fara jin tsanar Mk irin wadda bata yi zaton zata yi masa ba.
Kuka na fitar hankali Sa'adah take yi 'karshe ta dinga kelaya amai ta hanci da baka. Hankalin Inna da Baffah ya yi tashin gauron zabi.
Ranar Inna a wurin Sa'adah ta kwana karon farko da ta bar mijinta shi ka'dai alhalin suna gida 'daya.
Sosai Inna ta ke jin takaicin Baffah a ranta, idan ba zai yi kishin 'yarsa ba, menene zai siyar mata da kadararta ya bawa tsohon mijinta kudin dan yayi aure, babbar damuwar ba wai Rashi ne yasa akayi hakan ba, kawai dan ya nunawa duniya har da shi a cikin masu musgunawa farin-cikin Iyah.
Washagari da rashin kuzari ainun Iyah ta tashi, babban damuwarta ta ga Mk, ganin Inna ta shiga wanka yasa ta dauko wayarta ta 'kira layinsa, tana ta wasi-wasi ko an rufe layin?.
Ai kuwa bugu 'daya ya shiga, da sauri ya 'daga zuciyar sa tana bugawa.
"Malam ina son ganinka, ya za'a yi?"
Yadda ya ji muryar ta, da yadda ta yi maganar ya san zancen aurensa ya sameta.
"Ki saurare ni zan zo nan da awa guda".
"Ni dai mu ha'du gidan 'KARFI".
"Ok yanzu haka Ina gidan sai kin iso, ina jiran ki".
Yana ajiye wayar Mahmoud na fitowa daga kicin 'dauke da ruwan roba da tumblers guda biyu, ya dire wa Mk yana ta faman cin magani, ko abincin da suka gama ci, haka suka ci tamkar kurame adalilin fishin da Mahmoud yake yi da auren da Mk zai yi nan da kwanaki biyu.
Mk ya kalli Mahmod ya ce "Karfi ka daina wannan tunbatsar! kwanaki 'kalilan suka rage mini, na bar maka 'kasar ka huta da ganina".
Da rauni ya yi maganar hakan yasa Mahmoud sassautawa ya ce "Mk tunda ka amince zaka auri yarinyar nan, to ka hada su da Sa'adah, wallahi kai take jira, ko mai ta yi maka ai ka hukunta ta, shekaru hudu ba wata hudu bane, ba kuma sati hudu bane, Ni kaina na taya ka jin kunyar Baffah, wallahi tallahi karfin hali kawai yake yi akan lamarin ku, shi ya haifi Sa'adah, alkunyar da yake yi fa ta kai geji".
Kallo 'daya zaka yi wa Mk ka gane kalamin Mahmod sun sanyaya masa jiki kwarai da gaske, amma baya jin zai iya yin wannan al'amarin, ya kalle shi ya ce.
"Mahmoud na 'dade da gane ban da kirki, Ni da kaina zaluntar kaina nake yi, saboda wallahi har ya zuwa yau ban huta da kewarta ba, ban daina jin cewar na tafka asarar rashinta ba, ina son na rayu da ita, amma tsoron ta nake ji, ko ayyanawa na yi a zuciyata ya kamata na bata wata damar, sai na shiga ru'du da tashin hankali".
Ya yi shiru yana sakin ajiyar zuciya! Ya 'dora da cewa "wata'kila wannan na cikin 'kaddarata, na rayu a duniya ba da wadda nake so ba, alhalin tana raye".
Mahmoud ya rasa abin cewa, tausayin Sa'a yake ji, amma yanzu har Mukhtar 'din tausayi ya bashi, ya tabbatar a matu'kar takure yake da 'kadddarar da ta fado masa na auren Farida ba'katatan
Suna cikin haka! Yayan Mahmoud ya kira shi a waya, da sauri ya mi'ke yana cewa " yau tawa ta same ni wurin Auwal, sai da ya yi ta gargadi kar na bar shi yana jirah na.
Ai kuwa budar bakin Dadi sai cewa yayi "madallah da Mukhtar ganin ka yau na ji ka shiga Raina Kamar yadda ka shiga ka kwanta a zuciyar 'diyata, na gode da alherin ka, ka turo mini waliyyan ka, na baka auren Farida ba tare da neman komai daga gurinka ba".
Daga Farida har Mk abin ya zo musu tamkar saukar aradu, barin Mk da yaji tamkar mummunar kaddarace ta kawo shi asibitin, ba dan ba ya son Farida ba, sai don bai shirya aure a yanzu ba, bai shirya aurenta ba, a yanzu da ya gama sanin kansa ya fahimci mata masu duhu sunfi burge shi fiye da farare 'Kal, yana jin tsoron kar ya kasa yi mata adalci, tunda yasan ba karamin so take masa ba.
Cikin hikima irin ta manya Alh Nasir ya tisa Mk a gaba ya bashi lambar Alh Isa a matsayin Babansa dan su Baba umaru sama sama suke da shi adalilin sakin da ya yiwa Sa'a sun kuma lashi takobin matu'kar ba Sa'a zai dawo da ita ba, ba za su sake neman masa aure ya kunya ta su ba.
Cikin cire girman kai mahaifin Farida ya gaisa da Alh Isa ya zarce da cewa "yaron ka na bawa matar aure amma na ga tsoron tunkarar ku da maganar ya ke yi, shiyasa Ni na gabatar maka da maganar, na fada maka cewar nutsuwar danka ta sa na bashi kyautar 'yata mafi soyuwa da fatan zaka karbar masa".
Matu'kar mutum yasan daddako wa za'a yiwa haka ya ce ba zai karba ba?
Jikin Alh Isa ya mutu ya ce "kyuatar dan mutum ba mahalu'kin da za'a bawa ya tankwabar mun gode zan zo in sha Allah da kaina zan zo na karbar masa na kuma yi godiya.
Washagari Alh Isa da Mk suka tarar da Baffan Sa'a suka masa bayanin Halin da ake ciki, idan ya ce bai ji rashin da'di ba ya yi 'karya, idan ya ce bai so Iyah ce zata koma 'dakinta ba yayi karya, hakan nan idan ya ce mahaifin Farida yasan ciwon kansaa Nan ma bai yi karya ba.
Amma ko dan ya ramawa Mk kadan cikin alherin da tunda yasan shi yake masa ba gajiya har yau yasa shi cewa "madallah jibin idan za ku tafi ku biyo ku dauke ni da ni za'a je neman aure tare da godiya ina fatan alheri tare da fatan ta kasance abokiyar arzikin ka ce".
Kafin jibin kuwa sai da Baffa ya siyar guda cikin filayen nan wadda kudin daya ya zarta kudin duka biyun sadda aka siya, sosai gurin ya yi daraja adalilin anata gine gine. Dubu 'dari uku da talatin aka siyar.
Da daddare ya Kira Mk ya danka masa dubu dari biyu akan ya bawa Alh Isa dan akai gidan su Farida.
Kunya ta kama Mk ya ki karba, ai kuwa Baffa ya rantse sai ya karba sai idan ya raina me ko yana ganin bashi da arzikin da zai masa alheri.
Da sauri Mk ya sa duka hannunsa ya karba yana cewa "Haba Baffa, mahaifana ne kawai suka mini alheri sama da kai, har yau kuma banga dattijon arziki sama da aki a idona ba gani na yi na doara maka nauyi mai yawa Baffa! Ina rokon na raba biyu na dauki rabi".
"Duka na baka Mutari sadaki ne haka nake so ka bayar dan su san iyayen ka sun san alheri, ko da sunce basu bu'katar komai daga garemu dole ka bada sadaki, burina ace na biya maka fiye da haka, ban son Alh Isa ya gane ni na bada kudin shiyasa na baka a hannunka da sai munje zan bayar, sannan shine wakilinka dole shine mai bayarwa".
Zuciyar Mk ta karye ya yi kasa da kansa yana jin hawaye na Shirin zubowa.
Haka kuwa! Da Baffah aka kai kudin auren Mk akasa 'daurin aure sati mai zuwa, tunda ba tarewa zata yi ba, sai sun dawo, can ingila zasu tafi.
Har zuciyar Alh Isa yake jin rashin da'di, har jinyar kwana biyu ya yi adalilin kunyar Malam Basiru da takaicin Mukhtar.
Haka kuma Mk da yake jin tamkar 'kasa ta tsage ya shige dan tsananin kunyar Baffah.
*SURAYYA DAHIRU*
✍️✍️.
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
Na
*SURAYYA DAHIRU GWARAM*.
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*
*Comments din ku na sani nisha'di kwarai da gaske! Na gode muku ubangiji ya bamu damuna mai albarka*.
*Gaisuwa da fatan alheri ga dukkan yan KUNGIYAR LAFAZEE WRITERS*.
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*
85-86.
Murna wurin Farida tamkar ta zuba ruwa a kasa ta sha, ta godewa Allah, ta godewa mahaifinta Ashe da gaske yake da ya ce sai inda karfinsa ya kare wurin nemo mata farin cikinta. Ta tuno sadda Mk ya auri Sa'a irin kukan da ta yi a kirjin mahaifin ta, yana lallashinta da kalmomi masu da'di, tare da al'kawarin matu'kar yana raye sai ta auri wadda ya fi Mukhtar, ko kuma shi Mukhtar din kansa. A wanccan lokacin bata gasgata ba, kawai ta dauka saboda ya kwantar Mata da hankali ne.
"Wa yake da uba irin nawa?" ta furta a fili, hawaye na zirarowa wadda ta tabbatar sune na karshe akan rashin Masoyi.
Sa'a kuwa ba tasan me yake faruwa ba, har sai da auren ya rage kwanaki uku, Zainab ta gano musu a group, da farko bata gasgata ba, amma da yake Rukayya Mustapha aminyar Faridan suna dan gaisawa da Zainab sama sama tunda duk class mate ne, anan ta tabbatar jibi Uncle Mk Bichi zai angwance da Farida Torondi.
Hankalin Zainab ya kasa kwanciya, a gigice ta tafi gidan su Sa'a amma da ta lura Sa'adah bata san mai yake going ba, sai ta fasa fa'da dan kuwa be kamata ace a bakinta aminiyarta zata ji wannan ba'kin labarin ba.
Tasan da tana da waya da ta ji.
Baffah da kansa ya fa'da wa Innah da Iyah auren Mk, ba Sa'a kawai ba hatta Inna kuka ta fashe da shi mussaman da ya tabbatar musu ya siyar da fili daya cikin filayen Sa'a ya biyawa Mk sadakin auren.
Sosai suka tayar masa da hankalin sa domin irin kukan da suke tamkar ance Sumayya ta yi mutuwar fuju'a ne.
Har cikin ran Inna take jin wani irin azabben kishi na ratsa ta, bata
san kishi ba sai a ranar tunda ta wanzu ita kadai ne a wurin mijinta
A kuma ranar ta fara jin tsanar Mk irin wadda bata yi zaton zata yi masa ba.
Kuka na fitar hankali Sa'adah take yi 'karshe ta dinga kelaya amai ta hanci da baka. Hankalin Inna da Baffah ya yi tashin gauron zabi.
Ranar Inna a wurin Sa'adah ta kwana karon farko da ta bar mijinta shi ka'dai alhalin suna gida 'daya.
Sosai Inna ta ke jin takaicin Baffah a ranta, idan ba zai yi kishin 'yarsa ba, menene zai siyar mata da kadararta ya bawa tsohon mijinta kudin dan yayi aure, babbar damuwar ba wai Rashi ne yasa akayi hakan ba, kawai dan ya nunawa duniya har da shi a cikin masu musgunawa farin-cikin Iyah.
Washagari da rashin kuzari ainun Iyah ta tashi, babban damuwarta ta ga Mk, ganin Inna ta shiga wanka yasa ta dauko wayarta ta 'kira layinsa, tana ta wasi-wasi ko an rufe layin?.
Ai kuwa bugu 'daya ya shiga, da sauri ya 'daga zuciyar sa tana bugawa.
"Malam ina son ganinka, ya za'a yi?"
Yadda ya ji muryar ta, da yadda ta yi maganar ya san zancen aurensa ya sameta.
"Ki saurare ni zan zo nan da awa guda".
"Ni dai mu ha'du gidan 'KARFI".
"Ok yanzu haka Ina gidan sai kin iso, ina jiran ki".
Yana ajiye wayar Mahmoud na fitowa daga kicin 'dauke da ruwan roba da tumblers guda biyu, ya dire wa Mk yana ta faman cin magani, ko abincin da suka gama ci, haka suka ci tamkar kurame adalilin fishin da Mahmoud yake yi da auren da Mk zai yi nan da kwanaki biyu.
Mk ya kalli Mahmod ya ce "Karfi ka daina wannan tunbatsar! kwanaki 'kalilan suka rage mini, na bar maka 'kasar ka huta da ganina".
Da rauni ya yi maganar hakan yasa Mahmoud sassautawa ya ce "Mk tunda ka amince zaka auri yarinyar nan, to ka hada su da Sa'adah, wallahi kai take jira, ko mai ta yi maka ai ka hukunta ta, shekaru hudu ba wata hudu bane, ba kuma sati hudu bane, Ni kaina na taya ka jin kunyar Baffah, wallahi tallahi karfin hali kawai yake yi akan lamarin ku, shi ya haifi Sa'adah, alkunyar da yake yi fa ta kai geji".
Kallo 'daya zaka yi wa Mk ka gane kalamin Mahmod sun sanyaya masa jiki kwarai da gaske, amma baya jin zai iya yin wannan al'amarin, ya kalle shi ya ce.
"Mahmoud na 'dade da gane ban da kirki, Ni da kaina zaluntar kaina nake yi, saboda wallahi har ya zuwa yau ban huta da kewarta ba, ban daina jin cewar na tafka asarar rashinta ba, ina son na rayu da ita, amma tsoron ta nake ji, ko ayyanawa na yi a zuciyata ya kamata na bata wata damar, sai na shiga ru'du da tashin hankali".
Ya yi shiru yana sakin ajiyar zuciya! Ya 'dora da cewa "wata'kila wannan na cikin 'kaddarata, na rayu a duniya ba da wadda nake so ba, alhalin tana raye".
Mahmoud ya rasa abin cewa, tausayin Sa'a yake ji, amma yanzu har Mukhtar 'din tausayi ya bashi, ya tabbatar a matu'kar takure yake da 'kadddarar da ta fado masa na auren Farida ba'katatan
Suna cikin haka! Yayan Mahmoud ya kira shi a waya, da sauri ya mi'ke yana cewa " yau tawa ta same ni wurin Auwal, sai da ya yi ta gargadi kar na bar shi yana jirah na.