← Book details Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 55 OF 113

Sashe 55

Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Cike da shauki yace "Na gane duk da bai gama zuwa mana ba, nasan kema a finan finan ketare kike ganin kicin din, ba damuwa za'a miki irinsa Ummu Jawad my dear".

Ta rufe ido tana jin duk wani kunci na zuciyarta ya wanke mata tas. Shikuma yana ta barin jiki wirin sake sata walwala.

Tafiya ya shirya musu zuwa Abuja, duk a kokarinsa na son dawo da amincin dake tsakanin su.

Gidan Mahmoud da yake Goron Dutse, aka kai Jawad saboda makaranta, kuma yafi kusa.

Ranar Alhamis suka tafi, sun Isa lafiya, karfe uku suna madaidaicin Hotel din da ya kama musu daki.

Sallah suka yi, sai cin abinci ya biyo baya, wadda a hanya suka tsaya ya siyo, sai da suka koshi, suka yi wanka dan warware gajiya, sannan suka dora da sallar la'asar.

Barcine ya gwada musu fin karfi, Mk ne yafara yi, Sa'adah ta zuba masa ido tana kallon kyakkawar fuskarsa, da yadda yake sauke numfashi a hankali cikin nutsuwa, wani irin shauki na mamayarta, tana jin sonsa na bin duk wata kafa ta jikinta. A haka itama barci ya wuce da ita ba zato.

Sai daf da maghrib suka farka, suna mamakin lokacin da suka shafe suna barci.

A gurguje, Mk ya dora alwallah ya fita neman massalaci, ai kuwa cikin sa'a bai yi tafiya mai yawa ba, ya samu.

Kafin ya dawo Sa'adah ta ninke shimfidar gadon, ta dauko bedsheet din da ta zo da shi ta shimfida, ta sake dauko burner ta jona ta zuba turaren wuta, nan da nan daki ya dauki daddadan kamshi.

Ganin lokaci ya tafi bai dawo ba ta gane sai ya sallaci isha lafin ya shigo.

Ya dawo ya sameta cikin kwalliya sosai, ga sanyi ac da kamshin turarenta da kuma na turaren wuta ya cakude, dakin ya zama na mussaman.

Da sauri ya yi wurgi da ledojin hannunsa wadda gasasshiyar kazace, sai kuma ruwa da yogurt masu sanyi. ya isa kusa da ita yasa hannun ya rungumeta tsantsan yana ta shin shinarta, ita kuma ta lafe a jikinsa tana jinta in a new world.

Sun jima a hakan, kafin ya saketa, ya zauna a kasan kafet, idonsa ya kada, leda ta bude ta dauko plate da ta juye musu kazar, suna ci ta gabatar masa da shayi a dan karamin flask ga kuma cup da spoon a ciki, ya kalleta da murmushi yace "shiri kika yi haka?" Murmushi ta yi kawai.

Suna kammalawa Sa'adah ta yo brush, ta hadawa Mk ruwan wanka. Kafin ya fito ta shirya cikin sabbin nighties masu daukan hankali. Ya fito daure da faffadan tawul, ya tarar da jallabiya da gajeran wando akan gado, ga kuma body spray dinsa na Malizia.

Turaren kawai ya fesa ya dauke kayan ya dorasu kan side drower.

Ya zauna sanyi dakin na ratsa shi, yana ayyana suna komawa zai sanya musu Ac.

Tana tsaye tace "ba zaka sanya kayan ba?" Ido ya kanne tare da fadin "Ban bukatar su a yanzu".

Kunya ta kamata, ta waske da fadin "Mai ba zaka shafa ba shima?"

Maimakon ya amsa mata sai ware ya dukkan hannuwansa biyu alamun ta zo gare shi, ta tsaya tana kallon sa, ta kasa motsawa, yace "plz Dear come to me".

Cikin kunya ta isa gare shi, ya zaunar da ita kan cinyoyinsa ya rungume ta tamkar zai hade su.
Ta lafe a kirjinsa tamkar wadda zai shayar da ita, ya sunkuyar da fuskarsa daf da tata, numfashin su ya dinga haduwa, tsinin hancinsa akan nata, jikinsu ya dauki wani irin tsimi.

Ya raba hancinsu, amma fuskokinsu a hade. Cikin wata murya da Sa'adah bata sanshi da shi ba yace "Ina sonki, ina son na rayu da ke! Dan Allah stay with me".

Jikin Sa'adah ya yi la'asar, da murya marar amo tace "kana ganin zan iya barinka ne Malam?"

"Matu'kar kina tare da su Halima, kina basu damar da suke cusa miki ra'ayinsu Ina tabbatar miki zasu raba ni da ke" ya fada cikin rawar murya.
Kafin ta yi magana ya zarce da fadin "Ina miki son da zan sadaukar miki da komai, idan nace komai, ina nufin har rayuwa ta amma ke baki fahimci hakan ba"

Ya sake ri'keta sosai, cikin wata murya irin ta karaya da lamari yace "Bana son kaifin harshe Sa'a, bana miki akan me zaki dinga mini? zan ro'ke ki! dan Allah fada mini inda na kuskure miki da ban cancanci ki zauna da ni lafiya da kyautatawa ba?"

Ta yi shiru tana jin hawaye na cika mata idanuwa, haka kawai take jin tamkar wani abu na tashin hankali zai biyo baya.

Jin shirunta sai ya zarce da fadin "ki bude baki, ki mini magana, ki fada min inda na gaza sai na gyara tunda ubangiji ya dora mini sonki da son zama da ke".

Ta girgiza kai muryar ta na rawa tace "Ba ka gaza ba Malam".

Ya nisa yace "Am not good in bed?".

Kunya ta kamata, ta cusa fuskar ta a kirjinsa, yace "magana muke yi ta gaskiya".

Ta dinga dan dukan kirjinsa tana cewa "Ai kasan dai kure ni ka ke yi anan ma."

"Idan kuwa hakane, to mai ya kawo Kika canja, mai yasa kike bijire mini?"

"Ka yi hakuri zan canja".

Yaushe zaki canja din?".

Ta tura mai Baki gaba cikin shagwaba tace "Na canja fah".

Da'di ya kamashi ya dinga kai mata kisses ta ko ina tamkar mayunwacin zaki.hannuwansa suna ta kai komo a jikinta.

Da kyar ya sarara mata, dukkansu sai numfashi suke mayarwa, daga inda yake ya mika hannu ya janyo ledar yogurt ya bude ya fara bata a baki, Yana cewa "ke Amaryace yau! irin Amaryar da ta kerewa mata hudu"

Da'di ya kamata, ta sha iyakar shanta, ya shanye ragowan da ta bari daga nan ya sa harshe yana lashe mata baki, ya janyo harshenta Yana sucking irin deep din nan, daga haka suka fada zazzafar soyayya mai dimautarwa.

Haduwar ta zama so ma sha Allah, saboda hadin kai da Sa'adah ta bayar, sabanin kwanakin baya da take zame mishi very doll.

*Surayya Dahiru*
✍️✍️
07/04.

🌺 *HALIN YAU*!🌺

NA

*SURAYYA DAHIRU*.

lafazee writers.

*A guji taba Wañnan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.

*Doka mi lamba ta 68 ta yi nuna cewa satar fasaha Babban laifine da yake dai-dai da satar Dukiya*.

*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*

*Tukuici ga*
*HAJIYA RABI SANI*
*Bisa yaddda kike son rubutun Halin Yau, Na gode, Allah ya shirya zuri'a*
*SA'ADAH NA GAISUWA*.

71-74.

Wannan dare ya shiga cikin dararen da ba zai shafe a zukatan su ba, saboda sun jiyar da junansu farin ciki na ban mamaki. Sosai Mk ya bawa Sa'adah soyayya da kulawa mai yawa, kullum suna tare ba inda yake zuwa idan ba masallaci ba, itama kuma bata komai sai gyaran daki, wannan hutun ya sabunta soyayyar su, ya kara musu shakuwa, ya kuma goge dukkan tsattsar dake zukatan su, aminci da Nishadi ya cika 'kalbinsu.

Kwanaki biyar suka yi amma fahimtar da suka samu a cikinsu ya zarta na wattanni biyar.
Ana gobe za su dawo da daddare, suna kwance ya rungumeta sosai tamkar zai maida su halitta 'daya, hatta bugun zuciyar su suna ji, sai dai bugun da zuciyar Mk yake yi ta zarce ka'ida.

A hankali Sa'adah ta ce "Malam baka da lafiya ne?"

Murya a dakushe ya ce "me kika gani?"

"Bugawar da zuciyarka take yi yanzu ya sha ban ban".

Cike da rauni ya ce "fargaba nake yi Sa'adah! bana son mu koma Kano ki canja mini, na fi son wannan rayuwar da muke yi, mai cike da nutsuwa da girmamawa".

"Nace komai ya wuce fa, sannan ai na baka ha'kuri, mai yasa ba ka gamsu ba?"

Kai tsaye ya ce "ki mini al'kawarin yanke kawancenku da su Halima, Ina rokon ki, ki rabu dasu, sannan ki mini al'kawarin baza ki dinga 'daga mini hankali ba, komai kike so a hankali zan miki kin ji? Ni dai fatana mu zauna lafiya".

Haka kawai ta ji hawaye na zubar mata karon farko da ta ji tausayinsa ya cika mata zuciya, sai take jin tamkar mutuwa ce zata sure wani a cikinsu.

Jin 'dumin hawayenta na zuba akan kirjinsa, yasa nasa hawayen da tun dazu yake kokawa da su, suka kwace masa! kwatsam Sa'adah sai jin saukar hawayensa ta yi akan goshinta, karon farko da ta ga ko jin hawayensa a cikin shekaru biyar da ta yi tare da shi, hatta mutuwar Hajiya Babba da ta masa mugun bugu, ita dai bata ga hawayensa ba.

Kuka sosai Sa'adah ta saka tana cewa "Malam me kake yi haka, me na yi haka? me yasa kake zullumi har haka akaina? Kai baka ganin laifin kanka sai nawa ka'dai?"

Da rawar murya ya ce " Nan duniya ba wadda zai cusa mini ra'ayi akan ki na yarda, saboda na fishi sanin ki, hakanan son da nake miki ba za bani kuzarin da zan cutar da ke ba".

"Nima ba a cusa mini ra'ayi akan ka ba".
Murmushi mai sauti ya yi wadda baya dau'ke da nishadi ko ka'dan.
Ya ce "shikenan fatana dai ki kulle kofofin da kika bude wasu suke shigowa cikin matsalar mu, wadda Ni da ke kawai ta shafa".

"To Malam ya maganar makaranta ta?"

"Da gaske za ki yi, amma sai kin dawo mini Sa'adah ta, kinsan tun farko bana shiri da Gogel badan komai ba, sai dan rudeness dinta, shine yanzu zaki dawo mini a Gogel din?"

Ta 'dan dara kadan! kafin ta yi magana, ya rigata da cewa "Ban so na fada miki yanzu ba, amma bari ki ji, kinsan naje Abuja na yi jarrabawar scholarship, idan na Sami nasara, zan yi PhD dina tsawon shekaru hudu a kasar England, so nake idan na tafi, naga da yiwuwar ku bini ke da Jawad sai ku bini, sai kiyi karatun ki acan, amma ba al'kawarin hakan na yi ba, Ina fatan dai hakan ya kasance, muna komawa zaku yi passport, na riga na yi nawa, idan hakan bai samu ba sai kiyi anan, kafin na dawo kinci karfin karatun ki".

"Allah ya zaba mafi alheri"
Inji Sa'adah.

"Ameen ameen" MK ya amsa mata.
Chapter 55 · 0% Book details