← Book details Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 69 OF 113

Sashe 69

Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yasan Jawad kawai ke da asarar rashin mahaifi, amma ita Hajiya tana da Ahamad, haka nan Sa'adah zata auri wani ya iya mantar da shi a ranta, amma Jawad fa?
Duk yadda yake da tabbacin Abbas da Ahamad har ma da 'Karfi baza su bar tilon 'dansa ya yi kukan maraici ba, ya tabbatar Jawad ba zai rasa uba ba, amma tabbas zai yi asarar rashin mahaifi da ba a samun biyu.

A hankali ya ja motar yabi bayan su Hajiya. Tsawon lokaci yana gurfane gabanta, ita kuma ta yi 'diban karan mahaukaciya da shi.
"Hajiya Dan Allah ki gafarce ni, ban san me na yi miki ba, fishin ki dafi ne a rayuwata, ki mini ha'kuri dan Allah". Karo na hudu kenan yana maimaita wannnan kalamin, ta kalle shi ta ga duk ya sake firgicewa, da gaske tasan yana tsananin gudun zuciyar ta, amma dole ta nuna masa ita ba UWA bace irin Agwagwa ba, yaranta a gaba ita tana binsu a baya. Ita kaza ce da ta ke gaba 'ya'yanta na bayanta, sannan idan ta ga 'da ya yi rashin 'da'a ta take shi ba dan bata sonsa ba sai dan ya zama nagari abin so da kwatance a ckin alumma.

A raunane ta ce "Kai ne da ha'kuri da na yi laifin da zaka iya mini fishi, har yaushe ka yi motar? da zaka dauko ni ka hade mini fuska tamkar wadda ka mini alfarma, ka sani ai ni ba bakuwar mota bace, idan ana sako wadda suka fara mallakar mota a Bichi da kewaye sai ansako gidanmu. sannan tun kafin a haifeka duk inda zani a mota ake kaini, bude ido ka yi ka ga mota a gidannan bare ka mini wani iyashege".

A matu'kar gajiye Mk yake fa'din "Na yi kuskure, ki yi hakuri abin ne yafi 'karfi na, ki mini uzziri Hajiya, ki sake dagewa wurin yi mini addu'a".

Ya Dora hannunsa daidai setin zuciyar sa ya ce, "zuciyata ciwo take mini sosai, tana mini zafi, wataran har numfashi bana iya yi, dan Allah ki yafe mini kar mutuwa ta zo mini kina fishi da ni, zan roke ki, komai na miki, da wadda zan miki nan gaba ki dubi Allah ki yafe mini, Ina rayuwa ne kawai amma wani lokacin bana sanin me nake ciki".

Tausayinsa ya kama Hajiya sosai, ta zuba masa ido tana nazarinsa.ta sassauta murya tace kana son ka warke daga ciwon da keke 'dan'dana, kana son nutsuwa ta zo maka, ka dinga sanin halin da kake ciki, kana son nutsuwar da ta yi maka tutsu ta dawo maka?

Ya ri'ke hannun ta muryar sa na rawa ya hau cewa 'ina so Hajiya, bana iya barci fa, ko abinci da na fara ci sai na ji ya tokare mini a wuya shikenan sai na kasa ci, kuma ina jin yunwar".

Hajiya tace "fada mini laifin da Sa'a ta maka na san shine yake neman kassara ka, rashinta kusa da kai ne yasa kake rasa gane halin da kake ciki domin kana sonta, farincikinka na 'damfare da ita ne".

Bai musawa Hajiya ba domin kuwa yasan gaskiya ta fada, amma sai ya saukar da kansa 'kasa ya ce 'kaddara ce ta rabamu Hajiya".

Cikin rarrashi ta ce "Ni uwarka ce, duk wadda zai ri'ke maka sirrinka a bayana yake, me yasa kake gudun abin da ka ke so da gangan?"

Sai lokacin bacin rai ya sake taso masa cikin fitar hayyaci ya ke firzar da maganganu " Ina sonta sosai, Ina son na rayu da ita, komai Ina yi mata, har da wadda ya fi 'karfina yi mata nake yi, amma kullum cikin zullumi nake zaune da ita, fa'da mini Hajiya me na gaza da ban cancanci na sami kwanciyar hankali da ita ba?".

"Ba ka gaza ta ko Ina ba, itama ai kullum cikin damuwar take tunda kishin rashin hankali ta 'dorawa kanta".

"Yanzu fa'da mini abin da ya kawo musabbabin rabuwar dan nasan irin hukuncin da zanyi, na kuma daina zarginka da manta alheri, da kuma rashin ha'kuri".

"BA KOMAI QADDARAR MU CE".

Ta zuba masa ido ta ce "Ko dai Ni ta zaga ko mahaifinku ko Hajiya Babba?".

A hankali ya girgiza kansa ya ce "Haba dai, ai komin tsiyarta ba ta isa ta mini hakan akan idona, na barta haka salin alin ba, sannan fa Hajiya yadda kike sonta haka take son ki, Ina mata shaida ko giyar wake ta sha ba abin da zan yi mata ta zage ku".

Ta kalle shi tana tuna fa'dar gaskiyarsa tun yana Yaro yana cikin abin da ya janyo masa soyayya a zuciyar mahaifinsa.

"To Ni dai indai ba wannan laifin ba, banga me zata yi ka 'ki yafe mata har haka ba".

Zuciyar Hajiya ta kasa daurewa tace "ko dai kama ta ka yi da wani?"

A zabure ya mi'ke yana fa'din subhanllah! haba dai Hajiya me yasa za ki yi wannan hasashen, har abada Sa'a ba zata yi hakan ba, in sha Allah ba zata yi hakan ba duk lalacewar *HALIN YAU* SA'ADATU ba zata yi hakan ba".

*SURAYYA DEE*
✍🏼✍🏼.

🌺 *HALIN YAU*! 🌺

•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•

*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*

*A kiyayi ta'ba wannan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.

*Fatan alheri ga*
*UMM ASGHAR NOVELS*.
*NOVEL ONLY GROUP*.
*Da dukkan grops din da ake tura wannan labarin ake sharhi tare da fatan alheri, ina ji ina kuma godiya da fatan Allah ya bamu damina mai albarka*.

*Gaisuwa ga*

*Fati Eshaik(Ummu Asghar)*
*Zalhatu Umar(Yayar mu)*
*Hauwa Umar(Mrs Nasir)*
*Zainab Abdullahi(Beneficial group)*.
*Fatima (Maman Aslam)*
*Aunty Ai'nau*
*Hauwa'u Umar Gwaram*
*Balki Sani*.
*Rahma Shu'aibu Kankara*.
*Kulsum Baffah Azare*.

*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.

83-84.

Sosai Hajiya ke nazarinsa, sannan ta sami nutsuwa da ya kasance ba abin da shaidan ke kissima mata bane. Dan haka sai ta ce "idan kuwa hakane banga menene mai zafi da ba zaka yafe mata ba, wallahi ta gane kuskuren ta, ka bata wata damar Ina tabbatar maka lafiya lau za ku zauna".

A hankali ya ce "Dan Allah Hajiya na ro'ke ki, ki bar wannan maganar, ki mini afuwa, ki kuma yi mini alfarmar daina yin wannan maganar, kawai fatana ki mini addua".

"To shikenan Allah ya yi zabin alheri".
Ta fa'da jikinta a sanyaye.

Ta bangaren Sa'a kuwa, har lokacin tana yawan 'kiransa a waya ta bashi ha'kuri, ko ta yi text, har ta kai har makaranta ta bishi, ta tsugunna a gaban sa cikin cire girman kai, tana bashi ha'kuri, a irin haka Farida ta fa'do ofis 'din ta tarar da su a hakan, ta juya da mugun sauri tana fa'din "Sorry excuse me"

Ganin da Farida da ta yi mata gurfane a gabansa ya matu'kar dukan zuciyar Sa'a, da muryar kuka ta kalle shi tace "yanzu ita ka ke so shiyasa ka rufe mini 'kofar afuwa ko?"

Kai tsaye ya ce "kinsan ba haka bane ,amma idan haka zuciyar ki ta rinjayar miki to bazan 'karyatata ba! Kar ki kuma zuwa mini nan, idan kina son magana da ni ki kira Ni a waya, Ni Kuma zan zo!amma wannan ya zama shine zuwan ki na karshe if not, zan fa'dawa Baffah".

Da kuka sosai ta isa gida, ta wuce Inna, ta fa'da dakinta, ta kwanta tana rusar kuka mai tada hankali.

Ada Inna ta 'kudiri aniyar duka zata mata, tunda ta fita bata sani ba, to kuwa zata nuna mata dan ta yi aure ta haihu ba ta fi karfin ta ba, bata wuce ta zaneta ba.😀

Amma ganin yadda ta shigo a kidime ga kuka tana yi na fitar hankali sai wanccan alwashin ya bi iska, ta ajiye lagwanin rishon da ta ke gyarawa, ta bita dakin.

Ta shiga! ta zauna kusa da ita, ta sassauta murya ta ce "Iyah Ina son ki gane gaskiya, ki gane sunnar rayuwa, ba komai ne kake samunsa a lokacin da kake so ba, mata da yawa basu sami nasarar auren wanda suke so ba, amma sun yi ha'kuri da wanda 'kaddara ta za'ba musu, suna cigaba da rayuwar su tamkar basu da damuwa.
Sa'banin ke da kin samu cikar burinki, sai dai *HALIN YAU* yasa kin tankwabar da dukkan daukakar da minjin ki ya miki, Ni na haife ki, ko Baffanki bai fini sonki ba Iyah".

Wannan maganganun na Inna ya sake karyar da zuciyar Sa'a, ta kasa daina kuka.

Yayin da Inna ta cigaba da cewa "Sai dai duk soyayyar da nake miki ba zan 'ki fadar gaskiya ba! Na tabbatar ke kika 'kullawa kanki wannan salalar tsiyar, ke Kika biyewa'kawar zuciya da shedanun 'kawaye suka jefa ki a kogin nadama, na shaida Muuutar mutum ne har da rabin mutum!

Abin da nake so ki fahimta 'daya ne, A yanzu dai bae zai mayar da ke ba, na tabbatar da zai mayar da ke da sauri haka, da ya ha'diye abin da kika shuka masa ko dan mahaifin ki!
Ki fuskanci rayuwar ki ta gaba, kin rayu a duniya shekaru goma sha shida zuwa Sha bakwai babu Muutar a cikinta, yanzu ma kuwa dole ki rayu babu shi, idan mutuwa yayi ai dole ki ha'kura bare yana raye, kuna sha'kar numfashi a duniya 'daya".

Cikin rarrashi Inna ta sake cewa"Zan fa'da miki wani abu ki ri'ke shi da kyau, Wannan bibiyar da kike masa ita take sake sawa Yana nesanta da ke, kin yi laifi, kin bashi ha'kuri tamkar yawun baki zai 'kafe, kin yi nadama, nadama ta gaskiya, to ki barwa Allah lamarinki ya miki za'bi, zabin Allah kuwa gaba yake da son ranmu, idan Kika ha'kura kika yarda da kaddarar da ta afkoiki, kika gamsu idan kin samu wata damar baza ki sake maimata kuskuren ki na baya ba, kika gane darasin da rayuwa ta koya miki, ina tabbatar miki Allah ba zai barki haka ba, ko dai ya dawo miki da Muutar da kansa ta yadda zaki fi 'kima da daraja, ko kuma ya baki wani mafi alherin".
Chapter 69 · 0% Book details