Sashe 76
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dai-dai lokacin Dr ya nisa sannan ya zarce da fadin "(osteoarthritis) wannan nau'in shine yafi yawa yana farawa adalilin kokewar shimfidar kawunan kasusuwan(articular cartilage) wacce take hana kasusuwa gogar juna yayin motsi, daga karshe hakan na janyo sidewar kawunan kasusuwan da kuma curewar su zuwa 'Kashi guda daya.
Wannan nau'in na faruwa adalilin jin rauni a ga'ba ko shigar kwayoyin cututtuka".
"Na'aam" Mk ya furta cike da gamsuwa.
Dr ya cigaba da cewa "sai kuma na biyun (Rhematoid arthritis) mai farawa da kumburin shingen gabobi, wannan nau'in yana farawa da kumburin da ya zagaye gabobi wanda ya ke samar da ruwan gabobi. Daga baya kuma ya cigaba har ga kokewar shimfidar kawunan kasusuwan. Wannan nau'in na faruwa ne sammakon rikicewar Garkuwan jiki har ta kai suna yaki tare da lalata shingen da ya zagaye gabobi wato(synovial membrane).
Cikin nutsuwa Mk ya fahimci Farida na fama da ciwon Arthritics nau'i na biyu wato (Rhematoid arthritis). Dan haka ya ce "Na gode sosai Dr! Na gamsu da bayanin ka, amma me yake kawo wannan ciwon?"
Cikin rashin gazawa Babangida ya ce "zuwa yanzu dai an tabbatar tasirin wannan ciwon ya hada da
GADO- ana iya gadar wannan ciwon idan an samu wani a ciki dangi yana da wannan ciwon ma'ana yana bin jini.
SHEKARU- yawan shekaru na tasiri sosai wurin samuwar wannan ciwo.
MATA-Jinsin mata sunfi kamuwa da ciwon Rhematoid arthritis yayin da jinsin maza suka fi kamuwa da (Gouty arthritis).
NAUYI- nauyi fiye da kima na jagorantar kamuwa da wannan ciwon, da kuma buguwa a gabobi".
Kafin Mk ya yi magana Dr Babangida ya sake cewa "kalubalen da masu wannan ciwon suke fuskanta bayana rad'ad'in azabar ciwon, sun hada da Tankwarewar yatsu, hannu ko kafa, ciwo yayin motsa gaba, kumburi sosai a gabobi, dama daina aikin gabobin gaba'daya".
Mk ya ce "Madallah da hazikin Dr! shin wanne shawarwari zaka bani don kulawa da mai fama da irin wannan ciwon?".
"To shawarar da zan baka kasancewar wannan lalura kusan ta dindince, ma'ana za'a tabbata ne ana s!han magani. Mafi soyuwa a inganta abincin marar lafiya, a yawaita masa cin kifi, a karanta masa cin nama mussaman Jan nama.
Da kuma yawan motsa jiki da shan maganin da likita ya 'dora mai lalurar akan ka'ida, sai kuma rage kiba ga masu ita".
Mk ya mika masa hannu tare da cewa"likita na gode sosai da lokacin ka da ka bani tare da mini cikakken bayanin da na gamsu, ina rokon ubangiji ya yiwa rayuwar ka albarka, ya kara maka ilimi mai albarka, ya sa sunanka ya yi fice a cikin 'kasa da waje".
Babangida ya amsa da cewa "Amin Nima na ji 'Da'din yadda ka nemi bayanin likita, baka tafi kanka tsaye siyan maganin rage rad'ad'in ciwo ko kumburi ba, domin yawan shan irin waddanan magagunan na janyo ciwon ulsa da ma gazawar 'koda bagatatan, ubangiji ya bamu lafiya gaba'daya".
Har wajen ofis din Dr Bojuwa ya rako Mk dan karramawa ga yayan abokinsa Akil, Mk yana ta masa fatan alheri da samun mace ta gari, tare da jinjina fasahar Babangida, yana hakaito sadda yake biyowa Akil makaranta, oh rayuwa gaibu ce, ba wadda yasan me gobe zata zo da shi.
Yana tafe yana tunin bashi da matsalar gwajin rukunin jini, tunda tuni yasan Farida A.s ce yayin da ya kasance A.A basu da matsala, kawai fargabar sa daya ciwon da ta ke faama da shi ance ana iya gadarsa kenan akwai yiyuwar ta haifa masa mai irin ciwonta.
Alatilas zai yi auren nan, ko dan ya nuna mata martanin soyayyar da ta wanzu tana masa ba gajiyawa amma a zahirin gaskiya kaso mai yawa na zuciyar sa da gangar jikinsa gaba'daya Sa'adah suke so, da ita suke son su rayu muddin rai, shi da kansa yasan hukunta kansa yake yi da rashinta.
Yana tu'ki yana ayyano cikakken dirin jikinta bata da rama kamar Farida, duk da a yanzu ta tsiyaye, amma ya yi imani da zarar ta dawo hannunsa komai da ta rasa zai dawo mata tunda zata sami nutsuwa, ga iya girkin gargajiya tamkar Innarta, ga ga gayu, kullum tamkar mai Shirin shigaa gasar kyawawa saboda kwalliya. uwa uba ta kasance mace mai lafiya, A.A ce sannan O positive duk wadda ya san darajar lafiya ya san wadda ubangiji ya hada musu wannan nau'ikan ba karamin ni'imomin ubangiji suke ciki ba.
Kalamanta na karshe ya fado masa wai idan ya sake tura mata kudi ba zai gama da uwarsa lafiya ba! Bai taba ganin inda abin arziki ya zama sharri ba sai a gurin Sa'adatu.
Ba 'karamin bata masa rai wannan kalmar ta yi ba, bayan tasan ita mai laifi ce, ya tsani kaifin harshe, umm
Kusan Wannan bacin ran da ta haddasa masa ya rage masa fargabar auren Farida da yake ji.
Washagari asabar dai dai da 17/09 aka daura auren Mukhtar Kabir Bichi, da Farida Nasir Torondi.
Daurin auren da ya samu halarta manyan mutanen na Nijer da Nigeria.
Sosai aka yi hidima ta bangaren amarya, duk yadda Farida ta so ya halarci Dinner da zata yi a harabar gidansu ha'kuri ya bata, bai je ba, yana ji a ransa tunda bai yi irin wannan sha'anin a bikin Iyah ba, to yanzu ma ba zai yi ba da yake da shekaru talatin har da tara.
Bangaren Iyah kuwa sai da aka daura auren ta gane Farida ya aura.
Duk yadda ta so yin jarumtar boye yadda auren Farida ya bugeta kasawa ta yi, ta fito daga dakinta, daidai lokacin Baffanta ya dawo daga wurin daurin auren ya ci sabon dinki tamkar yarsa yake aurar wa.
Tana tsaye tana kallonsa , sai kuma ta fara ganinsa bibbiyu, basu ankaraba suka ji tim ta zube a kasa.
Dukkansu suka kai mata dauki, tsawon lokaci ana kanta har sai da aka kira Maman Ema wata kwararriyar nurse ce har ta kai mukamin metron, ita ta dinga dawainiya da ita har ta farfado, tana fa'da musu jininta ne ya yi kasa sosai adalilin rashin samun barci da kuma damuwa da ta sanya a ranta.
Kwana biyun da suka biyo baya ba karamin tsauri suka yiwa Sa'adah da iyayenta ba, domin ba karamin wahala ta sha ba, har zabura take ta kwasa da gudu, gaba'daya ta gigice ta fita a hankalin ta, ba kuma komai ke damunta ba illah matsananciyar damuwa wato (Desperation).
Yadda take zabura da suratai ya matu'kar tada hankalin ahalinta mussaman Inna da ta ke uwa, ansan kuwa raunin uwa akan danta.
Bayan maganin asibiti har rubutu Baffa yake zama da kansa ya ke mata wadda na dangana ne da samun sukunin zuciya.
A wannan lokacin Inna ta kudiri aniyar Mukhtar ko shine namiji tilo a duniya da ya hallata Iyah ta yi zaman aure da shi, to kuwa ita ta Haramta mata shi, wannan abin da ya yiwa Iyah ta tabbatar ya yi tsauri da yawa ya wuce laifinta, ta yi imanin 'yarta ba zata yi zina ko sata ko wani mugun kaba'irar da zai kasa yi mata afuwa ba, ta lura so yake ya susuta mata yarinya ya sa zuciyarta ta buga, tunda shi bashi da asara ya angwance da 'diyar masu kambun susa.
Asalima Inna sai take ganin tamkar so yake ya shafawa Sa'adah kashin kaji. kuma raina arzikinsu ya yi.
Kwanaki biyu suka ragewa Mk ya wuce, ya dauki Farida da hantsi suka je ta gaida Hajiyar Bichi, duk yadda Hajiya take jin dama Sa'a ya dawo da ita, ta karbi Farida da sakakkiyar fuska, yayin da Jawad ya ke ta murnar Malam ya ce zasu bishi Ingila a jirgi da wannan balabiyar Auntin. Dai dai lokacin shekarun Jawad goma.
Kunyar Farida da sanyin ta yasa Hajiya ta dan rage 'kin data ke yiwa auren na su.
A hanyar su ta komawa gida ta ga ya sauka daga kan titin da zai bi ta unguwar su, ya hau wani daban.
Bata ce kala ba, ta zuba masa ido kawai.
Bai tsaya ko ina ba sai a harabar hotel din Tahir.
Jikin Farida ya yi sanyi sosai, ta shiga cikin rudani da fargaba, amma haka ta bishi, har dakin da ya riga da ya kama a safiyar yau, domin taga a aljihunsa ya fito da mukallin daki mai lamba 008.
A dadare ta shiga ta zauna, shikuma ya juya ya fita, ba'a jima ba ya dawo da leda mai dauke da yougurt da gasasshen kifi, sai lemuka masu sanyi hadi da ruwa.
Ka'dan ta dan ta'ba adalilin matsawar da ya mata, shi kuwa da dama yunwa yake ji sosai ya ci, sannan ya shiga ya yo wanka, ya fito daure da tawul iya kugunsa.
Mk da kansa ya dinga mamakin kansa bai yi zaton zai ji sha'awar wata macen bayan Sa'a ba, bai yi zaton zai yi rawar jiki har ya kasa ha'kuri su isa Uk kafin ya tare da amaryarsa ba, amma abin mamaki jiya kwana ya yi yana juyi, rabon da ya shiga irin wannan yanayin ya manta, bai sani ba ko dan yasan bai da wadda ta halatta a gare shi ne.
Ganin abin na neman kassara shi, shiyasa ya murje kunya ya je har gidansu ya daukota da zummar zai kaita ta gaida mahaifiyarsa sannan sisters dinsa na son ganinta sosai.
Sanin mijinta ne yasa ba a nemi ba'asi ko fargabar fitar su tare ba, asalima kyakkawan shiri aka mata, domin turaren da mahaifiyarta ta dinga bin duk wata ga'ba tana shafa mata na alfarma ne, takanas ake yiwa manyan matan da suka amsa sunansu a sanin duniyar kamshi.
Sannan ta bata wani irin tsumi da tunda aka fara aurenta kullum sai ancika mata ciki da shi, akan Dole Farida ke Sha, saboda kasancewarta masaniyar magaganuwa bata yarda da Shan kowanne irin abu da sunan magani ba.
Wannan kamshin ya sake rikita Mk yana jin tamkar wani maganadisu ke jansa ga Farida, shi ka'dai yasan yaddda ya kosa su kadaice.
Duk yadda Farida ta ke da kunya ta yi iyakcin bakin kokarinta ta bashi hadin kai, duk da yadda ta ke cin kwakwa a hannunsa kasancewar ita din cikakkiyar budurwa ce ta daure ya samu nutsuwa sosai.
Wannan nau'in na faruwa adalilin jin rauni a ga'ba ko shigar kwayoyin cututtuka".
"Na'aam" Mk ya furta cike da gamsuwa.
Dr ya cigaba da cewa "sai kuma na biyun (Rhematoid arthritis) mai farawa da kumburin shingen gabobi, wannan nau'in yana farawa da kumburin da ya zagaye gabobi wanda ya ke samar da ruwan gabobi. Daga baya kuma ya cigaba har ga kokewar shimfidar kawunan kasusuwan. Wannan nau'in na faruwa ne sammakon rikicewar Garkuwan jiki har ta kai suna yaki tare da lalata shingen da ya zagaye gabobi wato(synovial membrane).
Cikin nutsuwa Mk ya fahimci Farida na fama da ciwon Arthritics nau'i na biyu wato (Rhematoid arthritis). Dan haka ya ce "Na gode sosai Dr! Na gamsu da bayanin ka, amma me yake kawo wannan ciwon?"
Cikin rashin gazawa Babangida ya ce "zuwa yanzu dai an tabbatar tasirin wannan ciwon ya hada da
GADO- ana iya gadar wannan ciwon idan an samu wani a ciki dangi yana da wannan ciwon ma'ana yana bin jini.
SHEKARU- yawan shekaru na tasiri sosai wurin samuwar wannan ciwo.
MATA-Jinsin mata sunfi kamuwa da ciwon Rhematoid arthritis yayin da jinsin maza suka fi kamuwa da (Gouty arthritis).
NAUYI- nauyi fiye da kima na jagorantar kamuwa da wannan ciwon, da kuma buguwa a gabobi".
Kafin Mk ya yi magana Dr Babangida ya sake cewa "kalubalen da masu wannan ciwon suke fuskanta bayana rad'ad'in azabar ciwon, sun hada da Tankwarewar yatsu, hannu ko kafa, ciwo yayin motsa gaba, kumburi sosai a gabobi, dama daina aikin gabobin gaba'daya".
Mk ya ce "Madallah da hazikin Dr! shin wanne shawarwari zaka bani don kulawa da mai fama da irin wannan ciwon?".
"To shawarar da zan baka kasancewar wannan lalura kusan ta dindince, ma'ana za'a tabbata ne ana s!han magani. Mafi soyuwa a inganta abincin marar lafiya, a yawaita masa cin kifi, a karanta masa cin nama mussaman Jan nama.
Da kuma yawan motsa jiki da shan maganin da likita ya 'dora mai lalurar akan ka'ida, sai kuma rage kiba ga masu ita".
Mk ya mika masa hannu tare da cewa"likita na gode sosai da lokacin ka da ka bani tare da mini cikakken bayanin da na gamsu, ina rokon ubangiji ya yiwa rayuwar ka albarka, ya kara maka ilimi mai albarka, ya sa sunanka ya yi fice a cikin 'kasa da waje".
Babangida ya amsa da cewa "Amin Nima na ji 'Da'din yadda ka nemi bayanin likita, baka tafi kanka tsaye siyan maganin rage rad'ad'in ciwo ko kumburi ba, domin yawan shan irin waddanan magagunan na janyo ciwon ulsa da ma gazawar 'koda bagatatan, ubangiji ya bamu lafiya gaba'daya".
Har wajen ofis din Dr Bojuwa ya rako Mk dan karramawa ga yayan abokinsa Akil, Mk yana ta masa fatan alheri da samun mace ta gari, tare da jinjina fasahar Babangida, yana hakaito sadda yake biyowa Akil makaranta, oh rayuwa gaibu ce, ba wadda yasan me gobe zata zo da shi.
Yana tafe yana tunin bashi da matsalar gwajin rukunin jini, tunda tuni yasan Farida A.s ce yayin da ya kasance A.A basu da matsala, kawai fargabar sa daya ciwon da ta ke faama da shi ance ana iya gadarsa kenan akwai yiyuwar ta haifa masa mai irin ciwonta.
Alatilas zai yi auren nan, ko dan ya nuna mata martanin soyayyar da ta wanzu tana masa ba gajiyawa amma a zahirin gaskiya kaso mai yawa na zuciyar sa da gangar jikinsa gaba'daya Sa'adah suke so, da ita suke son su rayu muddin rai, shi da kansa yasan hukunta kansa yake yi da rashinta.
Yana tu'ki yana ayyano cikakken dirin jikinta bata da rama kamar Farida, duk da a yanzu ta tsiyaye, amma ya yi imani da zarar ta dawo hannunsa komai da ta rasa zai dawo mata tunda zata sami nutsuwa, ga iya girkin gargajiya tamkar Innarta, ga ga gayu, kullum tamkar mai Shirin shigaa gasar kyawawa saboda kwalliya. uwa uba ta kasance mace mai lafiya, A.A ce sannan O positive duk wadda ya san darajar lafiya ya san wadda ubangiji ya hada musu wannan nau'ikan ba karamin ni'imomin ubangiji suke ciki ba.
Kalamanta na karshe ya fado masa wai idan ya sake tura mata kudi ba zai gama da uwarsa lafiya ba! Bai taba ganin inda abin arziki ya zama sharri ba sai a gurin Sa'adatu.
Ba 'karamin bata masa rai wannan kalmar ta yi ba, bayan tasan ita mai laifi ce, ya tsani kaifin harshe, umm
Kusan Wannan bacin ran da ta haddasa masa ya rage masa fargabar auren Farida da yake ji.
Washagari asabar dai dai da 17/09 aka daura auren Mukhtar Kabir Bichi, da Farida Nasir Torondi.
Daurin auren da ya samu halarta manyan mutanen na Nijer da Nigeria.
Sosai aka yi hidima ta bangaren amarya, duk yadda Farida ta so ya halarci Dinner da zata yi a harabar gidansu ha'kuri ya bata, bai je ba, yana ji a ransa tunda bai yi irin wannan sha'anin a bikin Iyah ba, to yanzu ma ba zai yi ba da yake da shekaru talatin har da tara.
Bangaren Iyah kuwa sai da aka daura auren ta gane Farida ya aura.
Duk yadda ta so yin jarumtar boye yadda auren Farida ya bugeta kasawa ta yi, ta fito daga dakinta, daidai lokacin Baffanta ya dawo daga wurin daurin auren ya ci sabon dinki tamkar yarsa yake aurar wa.
Tana tsaye tana kallonsa , sai kuma ta fara ganinsa bibbiyu, basu ankaraba suka ji tim ta zube a kasa.
Dukkansu suka kai mata dauki, tsawon lokaci ana kanta har sai da aka kira Maman Ema wata kwararriyar nurse ce har ta kai mukamin metron, ita ta dinga dawainiya da ita har ta farfado, tana fa'da musu jininta ne ya yi kasa sosai adalilin rashin samun barci da kuma damuwa da ta sanya a ranta.
Kwana biyun da suka biyo baya ba karamin tsauri suka yiwa Sa'adah da iyayenta ba, domin ba karamin wahala ta sha ba, har zabura take ta kwasa da gudu, gaba'daya ta gigice ta fita a hankalin ta, ba kuma komai ke damunta ba illah matsananciyar damuwa wato (Desperation).
Yadda take zabura da suratai ya matu'kar tada hankalin ahalinta mussaman Inna da ta ke uwa, ansan kuwa raunin uwa akan danta.
Bayan maganin asibiti har rubutu Baffa yake zama da kansa ya ke mata wadda na dangana ne da samun sukunin zuciya.
A wannan lokacin Inna ta kudiri aniyar Mukhtar ko shine namiji tilo a duniya da ya hallata Iyah ta yi zaman aure da shi, to kuwa ita ta Haramta mata shi, wannan abin da ya yiwa Iyah ta tabbatar ya yi tsauri da yawa ya wuce laifinta, ta yi imanin 'yarta ba zata yi zina ko sata ko wani mugun kaba'irar da zai kasa yi mata afuwa ba, ta lura so yake ya susuta mata yarinya ya sa zuciyarta ta buga, tunda shi bashi da asara ya angwance da 'diyar masu kambun susa.
Asalima Inna sai take ganin tamkar so yake ya shafawa Sa'adah kashin kaji. kuma raina arzikinsu ya yi.
Kwanaki biyu suka ragewa Mk ya wuce, ya dauki Farida da hantsi suka je ta gaida Hajiyar Bichi, duk yadda Hajiya take jin dama Sa'a ya dawo da ita, ta karbi Farida da sakakkiyar fuska, yayin da Jawad ya ke ta murnar Malam ya ce zasu bishi Ingila a jirgi da wannan balabiyar Auntin. Dai dai lokacin shekarun Jawad goma.
Kunyar Farida da sanyin ta yasa Hajiya ta dan rage 'kin data ke yiwa auren na su.
A hanyar su ta komawa gida ta ga ya sauka daga kan titin da zai bi ta unguwar su, ya hau wani daban.
Bata ce kala ba, ta zuba masa ido kawai.
Bai tsaya ko ina ba sai a harabar hotel din Tahir.
Jikin Farida ya yi sanyi sosai, ta shiga cikin rudani da fargaba, amma haka ta bishi, har dakin da ya riga da ya kama a safiyar yau, domin taga a aljihunsa ya fito da mukallin daki mai lamba 008.
A dadare ta shiga ta zauna, shikuma ya juya ya fita, ba'a jima ba ya dawo da leda mai dauke da yougurt da gasasshen kifi, sai lemuka masu sanyi hadi da ruwa.
Ka'dan ta dan ta'ba adalilin matsawar da ya mata, shi kuwa da dama yunwa yake ji sosai ya ci, sannan ya shiga ya yo wanka, ya fito daure da tawul iya kugunsa.
Mk da kansa ya dinga mamakin kansa bai yi zaton zai ji sha'awar wata macen bayan Sa'a ba, bai yi zaton zai yi rawar jiki har ya kasa ha'kuri su isa Uk kafin ya tare da amaryarsa ba, amma abin mamaki jiya kwana ya yi yana juyi, rabon da ya shiga irin wannan yanayin ya manta, bai sani ba ko dan yasan bai da wadda ta halatta a gare shi ne.
Ganin abin na neman kassara shi, shiyasa ya murje kunya ya je har gidansu ya daukota da zummar zai kaita ta gaida mahaifiyarsa sannan sisters dinsa na son ganinta sosai.
Sanin mijinta ne yasa ba a nemi ba'asi ko fargabar fitar su tare ba, asalima kyakkawan shiri aka mata, domin turaren da mahaifiyarta ta dinga bin duk wata ga'ba tana shafa mata na alfarma ne, takanas ake yiwa manyan matan da suka amsa sunansu a sanin duniyar kamshi.
Sannan ta bata wani irin tsumi da tunda aka fara aurenta kullum sai ancika mata ciki da shi, akan Dole Farida ke Sha, saboda kasancewarta masaniyar magaganuwa bata yarda da Shan kowanne irin abu da sunan magani ba.
Wannan kamshin ya sake rikita Mk yana jin tamkar wani maganadisu ke jansa ga Farida, shi ka'dai yasan yaddda ya kosa su kadaice.
Duk yadda Farida ta ke da kunya ta yi iyakcin bakin kokarinta ta bashi hadin kai, duk da yadda ta ke cin kwakwa a hannunsa kasancewar ita din cikakkiyar budurwa ce ta daure ya samu nutsuwa sosai.