Sashe 81
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suna zaune Ahamad ya shigo ya ganta yana cewa "yau wa nake gani kamar Antina"
Da murmushi sosai ta ce "Nice me zan Samu?"
Ya mi'ka mata 'datar da yake ci, aikuwa ta karba ta hau ci, hakan kawai sai da Mk ya ji haushi dan me zata ci ragowan yawun Ahamad?
Ta mi'ka masa mukallin mota tana cewa "daure ka debowa 'danka kayan dubiya da mamarsa Zainab ta kawo masa".
Da azama ya karba, ya dinga shigo da kayayyaki har Hajiya ta ce " wanne irin hidima kuka yi haka Sa'a? Sai kace wadda zai bude shago?".
Ran Mk ya baci saboda yadda yaga uban kayayyakin ciye ciye masu tsada sai kawaia zuciyarsa ta kisima masa Bazawarinta ne ya yi wannan siyayyar.
Ya dinga huci karshe ya fice bai ko sake kallon kayan ba, da kyar ya ce da Zainab ta gaida gida.
Jawad ya warware ya koma zuwa School amma rashin son zuwa gidan Farida na sake ruruwa a ransa kullum da kuka yake isa gidan, sannan har yaje ya dawo sai ta 'kure da ya yi mata magana har zane shi Mk ya yi amma bai canja ba.
Kan dole Mk ya samo masa makarantar kwana ba tare da ya yi shawara da kowa ba, da kyar aka samo makarantar saboda anci karfin zangon karatu na biyu.
Sai da komai ya kammala na makaranta ya fa'dawa Hajiya dan kar ta hana, Kan dole ya dauki Jawad ya kai shi makarantar gwamnatin tarayya ta Kiyawa, a kokarinsa na nisanta shi da masu hure masa kunne da masu son cusa masa muguwar dabi'a.
A dai dai wannan lokacin aka dawo da Mijin Sumayya aiki Kano, da Karin girma sosai.
Tuni dama sunyi gininsu a gandun albasa layin kwankwaso, da farin ciki Suka tattaro Suka dawo kano cikin gidansu na alfarma.
Zainab ta haihu ta sami Musa sunan uban mijinta ne, Sa'adah ce ta yi masa inkiya da Walid.
Farida ce dai shiru har yanzu da suke cikin shekaru uku da aure, Mk na iyakacin kokarinsa wurin kwantar mata da hankali ya na tabbatar mata zai cigaba da sonta ko bata haihu ba.
Amma deep inside his heart ba abin da yake so irin yaga an masa haihuwa, ya matsu ya samarwa Jawad gishirin duniya.
Watan Mk uku da dawowa Jami'ar ta yi bikin karrama shi, tare da bashi mukamin Dr! Sannan ya zama shine H.O.D na English department. Wanda shine mafi karancin shekarun da ya taba zama Head of Department.
A wannan lokacin kuma mahaifin Farida ya bashi dan'kareren guda a Rijiyar Zaki, a matsayin kyautar karramawarsa ya taya shi murnar kammala karatunsa. Gida ne mai kyau, mai dauke da bangare biyu, matu'ka da gaske gidan Flat ne amma ya tsaru kwarai da gaske.
Har Jawad ya shekara Sa'adah bata ta'ba zuwa masa ziyara ranar visiting din ba adalilin tana gujewa haduwarta da Mukhtar. Sai dai Sumaayya da Inna su je, haka Farida da Mk da Hajiya duk suna zuwa.
Sai visiting din karshe wadda suka hadu da Mk har zuwa ranar da Mahmoud ya je gurinta da neman sulhu da irin bijirewar da Innah ta yi akan maganarta da Mk.
*'karshen labarin abin da ya faru a Rayuwar Sa'adah da take fatan matan da suke cikin waccan rayuwar da ta yi a baya su hankalta kafin komai ya kubuce musu*.
*Surayya Dee*
✍️
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
NA
*SURAYYA DAHIRU*.
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
*_Doka mai lamba ta 68 ta nuna cewa satar fasaha babban laifi ne da yake dai satar Dukiya._*
_*A guji taba wannan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba.*_
*Assalama Alaikum*!
*Tsokaci*
*Ina jinjina da godiya ga dimbin masu bibiyar wannan labari na *HALIN YAU* ina kuma jin dadin yadda kuke sharhi akan labarin, Allah Ya bar zumunci*.
*Bayan haka zan so na yi dan tsokaci game da wata sa'dara a cikin labarin, a shafin baya da na saki. Watau daidai wajen da MK ya tare da Farida a hotel din Tahir na yini daya. Wasu daga cikin masu kokarin bibiyar littafin kullum, sun yi sharhi akan cewa don me MK ba zai bari har sai sun tafi UK ba kamar yadda aka tsara? Me yasa bai yi hakurin ya nuna zumudinsa wanda hakan tamkar cin fuska da tozarci ne ga Sa'adah?*
*To abin da nake son na ja hankalin masu bibiyar labarin shi ne, a dabi'a ta namiji wannan ba komai ba ne. Idan har namiji na bukatar abu idonsa rufewa yake ya manta da komai, musamman ma bukatar kwanciyar aure. Abin a halittar maza yake, don haka shi MK bai yi haka da nufin muzantawa ga Sa'adah ba ko kuma jin cewa Farida ta fita. Sai dan a fahimci kaso casa'in da tara da digo Tara na mazan Yau haka suke, domin zasu iya kwanciya da macen da bama sonta suke ba, kawai dan su biya bukatar su ne sabanin da yaje wahalar gaske mace ta sallamawa wadda bata so kanta Akan tana so sai alatilas.*
*Watakila tsawon lokacin da ya dauka ne yasa shi gaza hakurin jurewa har sai sun tafi UK din*.
*Ina fatan masoya Iyah za su fahimci MK kuma su yi masa uzuri.*
*Wasalam*.
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
91-92.
*Barkan mu da Dawowa*
*Asalin labarin*.
Kwana Sa'a ta yi tana juyi, Abu goma da ashirin sun cakude mata, na farko idan ta ce bata son Mk ta yi karya, duk yadda take jin haushin sa, da jin bacin rai akan lamarinsa, bai hana ta ji wani irin murna da farin-cikin dawowarsa ba. na biyu kuma bata jin a karan kanta zata saurare shi har sai ya janye kalamansa, sannan kishin auren Farida da ya yi yana matu'kar kassara tunaninta, yana gushe dukkan farin cikin da take ciki, haka nan yana sanya mata jin haushinsa marar misaltuwa, sannan ya sababa mata jarumtar da zata iya yin fito na fito da shi. Sai kuma fargabar yadda Inna ta zafafa lamarin ta da shi.
Haka gari ya waye ta tashi da idanuwanta a kumbure ga ciwon kai tabbacin babu isasshen barci a tare da ita.
Tana tsakar gida tana brush ta dinga jiyo sautin wayarta, bata wani damu ba tana raya koma waye ya sake kira.
Maimakon ta shiga dakinta, dakin Innarta ta shige ta sameta ta idar da sallar walaha.
Ta sake gaisheta tunda sun riga sun gaisa tun asuba.
Ta zuba mata ido ta ce "Iyah wani Mafarki na yi da ya tayar mini da hankali, amma zan bishi da sadaka da kuma addu'a domin ba abin da sadaka bata wanke shi, kema ki tsananta addu'a ki kuma fita harkar Muutar tun baku sake jefa mana ba'kin cikin da ya zarta wadda muka shiga a baya ba".
A sanyaye Sa'adah ta ce "wani abin kika gani ne marar Da'di Innah?"
Da sauri Inna ta ce "ai idan akace marar da'di da sauki, abin da na gani muninsa ya zarce hankali, abin a nemi tsari ne, ba a kanmu kawai ba, akan kowanne musulmi ma, Malamin islamiyarmu ya ce ba kyu fa'dar Mafarki marar kyau domin duk yadda aka fassara maka shi haka zai zo maka, dan haka zan kame bakina , na bishi da istigifari da sadaka, ina sake jan kunnenki ki sake nesanta kan ki da Muutar".
A tsorace Sa'a ta ce "To Inna zan kiyaye in sha Allah, ashana zaki bani, ta kicin din na jefata a ruwa ban lura ba".
Ta karba ta fita, tana Kissimmee kissimmen mafarkin Inna da dukkan alama ita da Mk ya shafa.
Haka ta yini sukuku har yamma, Innar ma haka take ba kuzari adalilin mafarkin da ya mata tsaye a zuci, domin ta san da wahalar gaske ta yi Mafarki amma idan ta yi, ta kuma tashi da abin a kanta ma'ana bata manta ba, to kuwa lah shakka sai abin ya faru ko da ba kwabo da kwabo ba. Amma kaso sittin sai ya zama reality.
Mafarki ta yi wai Muutar na ta bin Sa'a da gudu, suna ta tseren, so yake ya kamota amma tana ta zille masa ga wani abu Abu a nade a hannunsa, sun ci gudu, har Sa'a ta gajiya ta zube a kasa tana haki ya karaso, da gudu ya jefa mata abin da yake ta faman kankame shi, tamkar 'kwai.
Da kuka Sa'adah ta bude ashe jariri ne, maimakon ta ga Sa'adah ta mayar masa da abinsa, sai kawai ta ga ta hau shayar da shi, cikin zafin nama ta nufi Sa'a, tana zuwa tasa hannu da nufin fisge yaron sai kawai ji ta yi an tureta da wani irin karfin da ya zarta na bil'adama, ta sake yun'kurin sake kwace yaron, aka sake turata cikin wani irin rami. Da wata irin murya ta ji ance "Zaki iya mutuwa akan wannan yaron, domin 'dansu ne, ke ce shamakin zuwansa duniya, to kuwa zai zo, idan baki yi Sa'a bama a dakinki zasu yi cikin su haifar miki shi a matsayin shege".
Da kyar Inna ta fito a cikin ramin nan bayan ta kukkuje kafafuwanta, dai dai lokacin Kuma ta farka adalilin Kiran assalatu da ta ji Anayi a masallaci.
Ta tashi duk jikinta a jike tsabar fargaba da rudu, ta mike a hankali tana neman tsari da samun shege a cikin zuri'arta.
Yammaci sosai kafin Sa'a ta shirya ta fito da Shirin tafiya gidan Sumayya.
A tsakar gidan ta sami Inna, ta ce "Inna zan tafi".
Ta daga ido ta kalleta ta ce "Ince sai wani satin kike da zama a kotu?"
"A a Gobe ne Innah".
"To ki gaishe da Yayar ta ki, sannan ki fa'da mata lalle ta sake taya mu da addu'a".
Har Sa'adah ta kusa kaiwa zaure Inna ta dawo da ita, ta zaunar da ita ta fa'da mata komai na mafarkin da ta yi, ta rufe da cewa "Dan haka ki nisanci Muutar.
Kunya ta kama Sa'adah amma ta daure ta ce "in Sha Allah hakan ba zata faru ba ubangiji ba zai kunyata ku ba Inna".
Da murmushi sosai ta ce "Nice me zan Samu?"
Ya mi'ka mata 'datar da yake ci, aikuwa ta karba ta hau ci, hakan kawai sai da Mk ya ji haushi dan me zata ci ragowan yawun Ahamad?
Ta mi'ka masa mukallin mota tana cewa "daure ka debowa 'danka kayan dubiya da mamarsa Zainab ta kawo masa".
Da azama ya karba, ya dinga shigo da kayayyaki har Hajiya ta ce " wanne irin hidima kuka yi haka Sa'a? Sai kace wadda zai bude shago?".
Ran Mk ya baci saboda yadda yaga uban kayayyakin ciye ciye masu tsada sai kawaia zuciyarsa ta kisima masa Bazawarinta ne ya yi wannan siyayyar.
Ya dinga huci karshe ya fice bai ko sake kallon kayan ba, da kyar ya ce da Zainab ta gaida gida.
Jawad ya warware ya koma zuwa School amma rashin son zuwa gidan Farida na sake ruruwa a ransa kullum da kuka yake isa gidan, sannan har yaje ya dawo sai ta 'kure da ya yi mata magana har zane shi Mk ya yi amma bai canja ba.
Kan dole Mk ya samo masa makarantar kwana ba tare da ya yi shawara da kowa ba, da kyar aka samo makarantar saboda anci karfin zangon karatu na biyu.
Sai da komai ya kammala na makaranta ya fa'dawa Hajiya dan kar ta hana, Kan dole ya dauki Jawad ya kai shi makarantar gwamnatin tarayya ta Kiyawa, a kokarinsa na nisanta shi da masu hure masa kunne da masu son cusa masa muguwar dabi'a.
A dai dai wannan lokacin aka dawo da Mijin Sumayya aiki Kano, da Karin girma sosai.
Tuni dama sunyi gininsu a gandun albasa layin kwankwaso, da farin ciki Suka tattaro Suka dawo kano cikin gidansu na alfarma.
Zainab ta haihu ta sami Musa sunan uban mijinta ne, Sa'adah ce ta yi masa inkiya da Walid.
Farida ce dai shiru har yanzu da suke cikin shekaru uku da aure, Mk na iyakacin kokarinsa wurin kwantar mata da hankali ya na tabbatar mata zai cigaba da sonta ko bata haihu ba.
Amma deep inside his heart ba abin da yake so irin yaga an masa haihuwa, ya matsu ya samarwa Jawad gishirin duniya.
Watan Mk uku da dawowa Jami'ar ta yi bikin karrama shi, tare da bashi mukamin Dr! Sannan ya zama shine H.O.D na English department. Wanda shine mafi karancin shekarun da ya taba zama Head of Department.
A wannan lokacin kuma mahaifin Farida ya bashi dan'kareren guda a Rijiyar Zaki, a matsayin kyautar karramawarsa ya taya shi murnar kammala karatunsa. Gida ne mai kyau, mai dauke da bangare biyu, matu'ka da gaske gidan Flat ne amma ya tsaru kwarai da gaske.
Har Jawad ya shekara Sa'adah bata ta'ba zuwa masa ziyara ranar visiting din ba adalilin tana gujewa haduwarta da Mukhtar. Sai dai Sumaayya da Inna su je, haka Farida da Mk da Hajiya duk suna zuwa.
Sai visiting din karshe wadda suka hadu da Mk har zuwa ranar da Mahmoud ya je gurinta da neman sulhu da irin bijirewar da Innah ta yi akan maganarta da Mk.
*'karshen labarin abin da ya faru a Rayuwar Sa'adah da take fatan matan da suke cikin waccan rayuwar da ta yi a baya su hankalta kafin komai ya kubuce musu*.
*Surayya Dee*
✍️
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
NA
*SURAYYA DAHIRU*.
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
*_Doka mai lamba ta 68 ta nuna cewa satar fasaha babban laifi ne da yake dai satar Dukiya._*
_*A guji taba wannan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba.*_
*Assalama Alaikum*!
*Tsokaci*
*Ina jinjina da godiya ga dimbin masu bibiyar wannan labari na *HALIN YAU* ina kuma jin dadin yadda kuke sharhi akan labarin, Allah Ya bar zumunci*.
*Bayan haka zan so na yi dan tsokaci game da wata sa'dara a cikin labarin, a shafin baya da na saki. Watau daidai wajen da MK ya tare da Farida a hotel din Tahir na yini daya. Wasu daga cikin masu kokarin bibiyar littafin kullum, sun yi sharhi akan cewa don me MK ba zai bari har sai sun tafi UK ba kamar yadda aka tsara? Me yasa bai yi hakurin ya nuna zumudinsa wanda hakan tamkar cin fuska da tozarci ne ga Sa'adah?*
*To abin da nake son na ja hankalin masu bibiyar labarin shi ne, a dabi'a ta namiji wannan ba komai ba ne. Idan har namiji na bukatar abu idonsa rufewa yake ya manta da komai, musamman ma bukatar kwanciyar aure. Abin a halittar maza yake, don haka shi MK bai yi haka da nufin muzantawa ga Sa'adah ba ko kuma jin cewa Farida ta fita. Sai dan a fahimci kaso casa'in da tara da digo Tara na mazan Yau haka suke, domin zasu iya kwanciya da macen da bama sonta suke ba, kawai dan su biya bukatar su ne sabanin da yaje wahalar gaske mace ta sallamawa wadda bata so kanta Akan tana so sai alatilas.*
*Watakila tsawon lokacin da ya dauka ne yasa shi gaza hakurin jurewa har sai sun tafi UK din*.
*Ina fatan masoya Iyah za su fahimci MK kuma su yi masa uzuri.*
*Wasalam*.
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
91-92.
*Barkan mu da Dawowa*
*Asalin labarin*.
Kwana Sa'a ta yi tana juyi, Abu goma da ashirin sun cakude mata, na farko idan ta ce bata son Mk ta yi karya, duk yadda take jin haushin sa, da jin bacin rai akan lamarinsa, bai hana ta ji wani irin murna da farin-cikin dawowarsa ba. na biyu kuma bata jin a karan kanta zata saurare shi har sai ya janye kalamansa, sannan kishin auren Farida da ya yi yana matu'kar kassara tunaninta, yana gushe dukkan farin cikin da take ciki, haka nan yana sanya mata jin haushinsa marar misaltuwa, sannan ya sababa mata jarumtar da zata iya yin fito na fito da shi. Sai kuma fargabar yadda Inna ta zafafa lamarin ta da shi.
Haka gari ya waye ta tashi da idanuwanta a kumbure ga ciwon kai tabbacin babu isasshen barci a tare da ita.
Tana tsakar gida tana brush ta dinga jiyo sautin wayarta, bata wani damu ba tana raya koma waye ya sake kira.
Maimakon ta shiga dakinta, dakin Innarta ta shige ta sameta ta idar da sallar walaha.
Ta sake gaisheta tunda sun riga sun gaisa tun asuba.
Ta zuba mata ido ta ce "Iyah wani Mafarki na yi da ya tayar mini da hankali, amma zan bishi da sadaka da kuma addu'a domin ba abin da sadaka bata wanke shi, kema ki tsananta addu'a ki kuma fita harkar Muutar tun baku sake jefa mana ba'kin cikin da ya zarta wadda muka shiga a baya ba".
A sanyaye Sa'adah ta ce "wani abin kika gani ne marar Da'di Innah?"
Da sauri Inna ta ce "ai idan akace marar da'di da sauki, abin da na gani muninsa ya zarce hankali, abin a nemi tsari ne, ba a kanmu kawai ba, akan kowanne musulmi ma, Malamin islamiyarmu ya ce ba kyu fa'dar Mafarki marar kyau domin duk yadda aka fassara maka shi haka zai zo maka, dan haka zan kame bakina , na bishi da istigifari da sadaka, ina sake jan kunnenki ki sake nesanta kan ki da Muutar".
A tsorace Sa'a ta ce "To Inna zan kiyaye in sha Allah, ashana zaki bani, ta kicin din na jefata a ruwa ban lura ba".
Ta karba ta fita, tana Kissimmee kissimmen mafarkin Inna da dukkan alama ita da Mk ya shafa.
Haka ta yini sukuku har yamma, Innar ma haka take ba kuzari adalilin mafarkin da ya mata tsaye a zuci, domin ta san da wahalar gaske ta yi Mafarki amma idan ta yi, ta kuma tashi da abin a kanta ma'ana bata manta ba, to kuwa lah shakka sai abin ya faru ko da ba kwabo da kwabo ba. Amma kaso sittin sai ya zama reality.
Mafarki ta yi wai Muutar na ta bin Sa'a da gudu, suna ta tseren, so yake ya kamota amma tana ta zille masa ga wani abu Abu a nade a hannunsa, sun ci gudu, har Sa'a ta gajiya ta zube a kasa tana haki ya karaso, da gudu ya jefa mata abin da yake ta faman kankame shi, tamkar 'kwai.
Da kuka Sa'adah ta bude ashe jariri ne, maimakon ta ga Sa'adah ta mayar masa da abinsa, sai kawai ta ga ta hau shayar da shi, cikin zafin nama ta nufi Sa'a, tana zuwa tasa hannu da nufin fisge yaron sai kawai ji ta yi an tureta da wani irin karfin da ya zarta na bil'adama, ta sake yun'kurin sake kwace yaron, aka sake turata cikin wani irin rami. Da wata irin murya ta ji ance "Zaki iya mutuwa akan wannan yaron, domin 'dansu ne, ke ce shamakin zuwansa duniya, to kuwa zai zo, idan baki yi Sa'a bama a dakinki zasu yi cikin su haifar miki shi a matsayin shege".
Da kyar Inna ta fito a cikin ramin nan bayan ta kukkuje kafafuwanta, dai dai lokacin Kuma ta farka adalilin Kiran assalatu da ta ji Anayi a masallaci.
Ta tashi duk jikinta a jike tsabar fargaba da rudu, ta mike a hankali tana neman tsari da samun shege a cikin zuri'arta.
Yammaci sosai kafin Sa'a ta shirya ta fito da Shirin tafiya gidan Sumayya.
A tsakar gidan ta sami Inna, ta ce "Inna zan tafi".
Ta daga ido ta kalleta ta ce "Ince sai wani satin kike da zama a kotu?"
"A a Gobe ne Innah".
"To ki gaishe da Yayar ta ki, sannan ki fa'da mata lalle ta sake taya mu da addu'a".
Har Sa'adah ta kusa kaiwa zaure Inna ta dawo da ita, ta zaunar da ita ta fa'da mata komai na mafarkin da ta yi, ta rufe da cewa "Dan haka ki nisanci Muutar.
Kunya ta kama Sa'adah amma ta daure ta ce "in Sha Allah hakan ba zata faru ba ubangiji ba zai kunyata ku ba Inna".