Sashe 97
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ai kuwa ta fito cikin kuka ta ce "Baffah shata mini layi da Maman Khalifa, ta takura ni, ta matsa mini, saboda ta san duk abin da ta yi mini Inna ba zata ce ta yi laifi ba".
Ya murmusa ya ce "Uwata an taba shiga tsakanin hanta da jini ne, inace da dukkan uku hade mini kai kuka yi.
Yanzu kuma sai kice na shata miki kayi da ita? Ni bana haka, ya kalli Sumayya ya ce ke kuma ki ri'ke girmanki ai dai yanzu kin wuce kisa ta kuka irin haka".
Murmushi sosai Sumayya ta yi, cikin sanyin muryarta ta ce "Baffa daga na ce bai kamata ta je dubiya da kwalliyar da ta yi bane shikenan fa laifin nawa, kuma gani na yi tunda ba zance zata je ba, dubiya ne ai sai ta rage zumudi".
Dariya ta kwace wa Baffah ya shige dakinsa. Ba tare da ya yi magana ba.
Yayin da Sa'adah ta cigaba da kuka sosai, har Zainab ta gaji ta shigo gidan a fusace.
Ganin kukan da take yi, ya tayar mata da hankali ta yi zaton ko Mk ya amsa Kiran mahallicinsa ne.
Amma da ta ji ba'asin kukan sai itama ta hau dariya har tana fadin "Yo dama Ni nasan ba wani bata sonsa, idan akwai abin da na gasgata a duniyata, to kuwa son da take yiwa Uncle na cikin su".
Ai kuwa ta mi'ke a fusace ta ce "Wallahi Zainab har yau din nan ina jin karfi a tare da ni, ya ishe ki".
Zainab ta watsa mata harara ta ce "Da shekarun nan naki, da ilimin lauyancin na ki, da Jawad duk basu sa kin ji cewar kin girma ba? Amma kuwa dai kin ji kunya, kuma na gasgata Anty Sumayya lallai murnar zaki komawa muradin zuciyarki yasa ki wannan fallin, gara ma ki 'dore da kyawawan dabi'un da Kika dauka a shekaru bakwai din nan domin dai kin san yanzu ke Uwargidace kina da amarya mai tsananin wayo da kissa".
Ba'kin cikin maganar Zainab ya sake sawa ta fashe da sabon kuka tana fa'din " Asibitin ma ba zani ba".
Baffah ya fito ya dubi Zainab ya ce "Ni na fi ku fahimtar Iyah tuni Mutari ya fita a ranta, biyayya kawai zata mini, zuwa duba shi ma ai dole na yi mata, ta kuma yarda zata mini biyayya, dan haka ku daina cewa tana sonsa, ko dan shi ta yi kwalliya domin kuwa dukkan mu shaida ne akan Iyah dangin Dawisu ce".
Jin hakan ya sa ta yi shiru.
Yayin da Zainab ta ce "To Baffa ka fa'da mata a biyayyar da zata yi maka ta hada har da sanin ta girma, kar ta koma ta zama ta bizaro a gidan Uncle domin yanzu ba ita ka'dai bace, tana da kishiya mai fi'ilin tsiya".
Baffah ya murmusa ya ce "ke kam Zainab sai a gaishe ki, dukkan mace ai da inda take da tasiri, Ni kuwa na san ko mata uku ne da Mutari ban jin Iyah zata kasa samun kansa, ai duk wannan shagwabar da take yi na gata ne".
Daga haka ya fice ya na fadin "lallai ki fito ku je dubiyar nan Iyah, kinga ba lalle Zainab ta sake samun sukunin fitowa a gobe ba".
Ta fito cikin bakar doguwar riga mai kyau. Tana rataye da Yar karamar jaka, kafarta sanye da flat din talkalmi wadda mahadin jakar ne, powder ce kawai a fuskarta.
Zainab ta mike ta na cewa "Inna sai mun dawo".
Har suka isa asibitin Sa'adah bata ce kala ba, duk da Zainab na janta da hira.
A wajen asibitin Zainab ta samu jikin bishiya ta yi fakin. Suka fito suka taka ciki da kafafuwansu.
Da Abbas suka fara yin tozali, yana zaman jiran Farida ta fito ya mayar da ita gida, dan haka ya mike ya musu jagora har dakin da Mk yake kwance.
A zaune suka taradda shi, Farida tana tsaye a gabansa hanunta na dama ri'ke da hannunsa, yayin da hannun na hagu ri'ke da kwandon zuba abinci, alamun tafiya zata yi.
Zuciyar Sa'a ta buga da tsananin gaske, ta zabura, zata koma da baya, Zainab da Abbas kawai suka lura da hakan, Dan haka cikin hikima Zaynab ta ru'ko hannun ta da karfin gaske, kan dole suka karasa shiga sosai.
Zainab suka gaisa da Farida ta tambayi mai jiki, sannan ta gaida Mk da ya yi mutuwar zaune, saboda yadda ya ji wani abu da bai san menene ba ya dirar masa, gashi dama fama yake da rashin karfin jiki.
Surayya Dee
✍️✍️.
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
*NA*
*SURAYYA DAHIRU*.
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*
*GAISUWAR GIRMA GA*
*HAJ SALIHA A.A. ZARIA.*
*MARUBUCIYAR BEGE*
*ALLAH YA KARA MIKI LAFIYA DA NISAN KWANA MAI ALBARKA*.
104-106.
Farida na ri'ke da hannun Mk, ta kalli Sa'a da murmushi ta ce "Maraba da Gogel, karaso kusa mana".
Takaici a zuciyar Sa'adah tamkar ta rushe da kuka, ta ki sakar masa hannu dan ta nuna mata itace matarsa. Sannan dan ta tabbatar mata ita bakuwa ce yanzu a wurin Mk, shine take mata iso a gabansa?
Ta daure ta hadiye damuwarta ta yi kamar bata ga hannuwansu a sarke ba, ta cewa Farida "Sannun ki".
Daga inda take tsaye ta kalli Mk ta ce "ya ya jikin?"
Daga haka ta tsuke bakinta, tana karanta duk addu'ar da ta zo bakinta, tabbas Mk ne ya wula'kanta ta saboda ya nunawa Farida ita ba wata tsiyar ba ce. Shiyasa ya ki zame hannunsa da yake cikin nata.
Amma ai ya yi da yar halak.
A hankali Mk yake kallonta ta kasan ido, yana nazartar yadda take kokawa da fishin da ya ke yun'kuro mata.
Cikin hikima ya zare hannunsa a hannun Farida, gumi sai yanko masa yake yi.
Da sauri Farida ta 'kara karfin A.C da gudun fanka, saboda zufar da taga na karyo masa wadda kawai ta fargaba ce. A ransa ya dinga nazarin anya zai iya jarumtar ri'ke mata biyu kuwa? Saboda yadda ya dinga zullimin kasancewarsa a gabansu a lokaci 'daya.
Mk na wanna tsinkayen ya ga Farida ta ajiye kwandon hannunta tabbacin ta fasa tafiyar kenan.
Wato duk ha'kurin mace ta iya shu'umanci indai akan kishi ne?
Yau ya gasgata hakan domin ko kaffara ba zai yi ba, idan ya yi rantsuwar saboda Sa'adah ta 'ki tafiyar.
Dan haka ya yi kicin kicin da fuska, ita kuma sai kokarin yi masa fifta take yi.
Yayin da Sa'adah da Zainab suke ganin ikon ubangiji na yadda Farida ta kankane komai, Zainab da Mk ne suke mamakinta. Yayin da Iyah ta san dama Farida zata yi abin da ya fi haka.
Abbas ne ya leko daga bakin kofar ya ce "Farida ina ta faman jiran ki, so nake na yi maza na kai ki na dawo, kafin su tafi kar abar shi ba kowa, Hajiya ta tafi tun dazu, zan biya na dauko su Anty Amina Kuma".
Ai kuwa ta ce "je ka dauko su kawai, idan Akil ko Ahamad sun zo, sai je su dauko mini motata, ko kuma na fita na hau adaidaita sahu".
Abbas ya yi sakare yana mamakinta a ransa tare da cewa "Ah adole ita ba zata basu damar ganawa ba, duk da dai bata nuna bacin rai ko damuwa ba.
Sai a lokacin Mk ya ce" amma kin san ban son Ahamad yana hawa motar ki saboda ba ya tuki da nutsuwa, Akil kuma yana shago sai dare ya fara jah yake zuwa".
Ta marairaice ta ce "Ba damuwa sai na hau adaidaita sahu".
"A a bana so kin sani, bana so".
Ya sake sassautawa "ya ce ki je ya kai ki, ana idar da Sallar isha ki rufe gidan, sannan ki taimake ni ki sha maganin ki please".
Ya fa'da cikin sigar rarrashi da kulawa.
Amma ta yi mirisisi ta ki tafiya, lamarin da ya sake dagula lissafin Sa'adah, wai yau a gabanta wata macen take nunawa ta fita son Mk, ta fita kusa da shi.
A gabanta shima ya ke nunawa wata macen tattali da kulawa? Wannan shine duniya rawar yanmata.
Shirun da Farida ta yi ya tabbatarwa da Mk bata amince bane, ya kalleta a tausashe ya ce "Ban son ki wuce lokacin shan maganin ki ne, gobe idan zaki taho, ki taho da shi, sai ki yi ta zamanki, amma yanzu taimake ni ki je ki kular mini da lafiyar ki".
Nan ma ta yi shiru, Mk ya ce "shikenan ai, tunda so kike mu kwanta gaba'daya".
Dakin ya yi shiru na mintina uku, Zainab na mamakin irin wannan al'amarin, ta kasa cewa komai duk da bakinta cike
yake da tarin maganganu, da suke bu'katar fashin ba'ki.
Irin kallon da Farida take yiwa Mk da idanuwanta masu maiko ya sa
nan da nan zuciyar Sa'a ta hauro, ta kalli Abbas dake bakin kofa yana tsayawur jiran Farida, amma ganin Sa'adah yasa ta fasa tafiyar dan kar ta samu damar 'dagawa mijinta hankali 😀
Ta ce "Uncle Abbas"
"Na'am Anty Sa'adahtu".
"Tafiya zan yi, kuma akwai sakon da zan fa'da masa, zo ka ri'ke mini shi zuwa waje na mintina kadan".
Da sauri Abbas ya shigo yana cewa "daga nan ma na zagaya da shi, dazun nan likita ya gama ce mini kwanciyar ta yi yawa, ya dinga yin atisaye ko a cikin dakin nan ne".
Ya isa jikin gadon ya mikawa Mk hannun, ya dago shi.
Ya sunkuya ya janyo masa takalma a a kasan gadon ya saka sannan ya mikar da shi, suka fita a hankali.
Zainab ta dinga jin wani irin farin-cikin iyakar da Sa'a ta nunawa Farida.
Sun Jima da fita sannan Sa'adah ta dauki handbag dinta zata bisu, Farida ta ce "Gogel ko zaki fitar masa da kujera, jikin nasa ba kwari har yanzu".
Ya murmusa ya ce "Uwata an taba shiga tsakanin hanta da jini ne, inace da dukkan uku hade mini kai kuka yi.
Yanzu kuma sai kice na shata miki kayi da ita? Ni bana haka, ya kalli Sumayya ya ce ke kuma ki ri'ke girmanki ai dai yanzu kin wuce kisa ta kuka irin haka".
Murmushi sosai Sumayya ta yi, cikin sanyin muryarta ta ce "Baffa daga na ce bai kamata ta je dubiya da kwalliyar da ta yi bane shikenan fa laifin nawa, kuma gani na yi tunda ba zance zata je ba, dubiya ne ai sai ta rage zumudi".
Dariya ta kwace wa Baffah ya shige dakinsa. Ba tare da ya yi magana ba.
Yayin da Sa'adah ta cigaba da kuka sosai, har Zainab ta gaji ta shigo gidan a fusace.
Ganin kukan da take yi, ya tayar mata da hankali ta yi zaton ko Mk ya amsa Kiran mahallicinsa ne.
Amma da ta ji ba'asin kukan sai itama ta hau dariya har tana fadin "Yo dama Ni nasan ba wani bata sonsa, idan akwai abin da na gasgata a duniyata, to kuwa son da take yiwa Uncle na cikin su".
Ai kuwa ta mi'ke a fusace ta ce "Wallahi Zainab har yau din nan ina jin karfi a tare da ni, ya ishe ki".
Zainab ta watsa mata harara ta ce "Da shekarun nan naki, da ilimin lauyancin na ki, da Jawad duk basu sa kin ji cewar kin girma ba? Amma kuwa dai kin ji kunya, kuma na gasgata Anty Sumayya lallai murnar zaki komawa muradin zuciyarki yasa ki wannan fallin, gara ma ki 'dore da kyawawan dabi'un da Kika dauka a shekaru bakwai din nan domin dai kin san yanzu ke Uwargidace kina da amarya mai tsananin wayo da kissa".
Ba'kin cikin maganar Zainab ya sake sawa ta fashe da sabon kuka tana fa'din " Asibitin ma ba zani ba".
Baffah ya fito ya dubi Zainab ya ce "Ni na fi ku fahimtar Iyah tuni Mutari ya fita a ranta, biyayya kawai zata mini, zuwa duba shi ma ai dole na yi mata, ta kuma yarda zata mini biyayya, dan haka ku daina cewa tana sonsa, ko dan shi ta yi kwalliya domin kuwa dukkan mu shaida ne akan Iyah dangin Dawisu ce".
Jin hakan ya sa ta yi shiru.
Yayin da Zainab ta ce "To Baffa ka fa'da mata a biyayyar da zata yi maka ta hada har da sanin ta girma, kar ta koma ta zama ta bizaro a gidan Uncle domin yanzu ba ita ka'dai bace, tana da kishiya mai fi'ilin tsiya".
Baffah ya murmusa ya ce "ke kam Zainab sai a gaishe ki, dukkan mace ai da inda take da tasiri, Ni kuwa na san ko mata uku ne da Mutari ban jin Iyah zata kasa samun kansa, ai duk wannan shagwabar da take yi na gata ne".
Daga haka ya fice ya na fadin "lallai ki fito ku je dubiyar nan Iyah, kinga ba lalle Zainab ta sake samun sukunin fitowa a gobe ba".
Ta fito cikin bakar doguwar riga mai kyau. Tana rataye da Yar karamar jaka, kafarta sanye da flat din talkalmi wadda mahadin jakar ne, powder ce kawai a fuskarta.
Zainab ta mike ta na cewa "Inna sai mun dawo".
Har suka isa asibitin Sa'adah bata ce kala ba, duk da Zainab na janta da hira.
A wajen asibitin Zainab ta samu jikin bishiya ta yi fakin. Suka fito suka taka ciki da kafafuwansu.
Da Abbas suka fara yin tozali, yana zaman jiran Farida ta fito ya mayar da ita gida, dan haka ya mike ya musu jagora har dakin da Mk yake kwance.
A zaune suka taradda shi, Farida tana tsaye a gabansa hanunta na dama ri'ke da hannunsa, yayin da hannun na hagu ri'ke da kwandon zuba abinci, alamun tafiya zata yi.
Zuciyar Sa'a ta buga da tsananin gaske, ta zabura, zata koma da baya, Zainab da Abbas kawai suka lura da hakan, Dan haka cikin hikima Zaynab ta ru'ko hannun ta da karfin gaske, kan dole suka karasa shiga sosai.
Zainab suka gaisa da Farida ta tambayi mai jiki, sannan ta gaida Mk da ya yi mutuwar zaune, saboda yadda ya ji wani abu da bai san menene ba ya dirar masa, gashi dama fama yake da rashin karfin jiki.
Surayya Dee
✍️✍️.
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
*NA*
*SURAYYA DAHIRU*.
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*
*GAISUWAR GIRMA GA*
*HAJ SALIHA A.A. ZARIA.*
*MARUBUCIYAR BEGE*
*ALLAH YA KARA MIKI LAFIYA DA NISAN KWANA MAI ALBARKA*.
104-106.
Farida na ri'ke da hannun Mk, ta kalli Sa'a da murmushi ta ce "Maraba da Gogel, karaso kusa mana".
Takaici a zuciyar Sa'adah tamkar ta rushe da kuka, ta ki sakar masa hannu dan ta nuna mata itace matarsa. Sannan dan ta tabbatar mata ita bakuwa ce yanzu a wurin Mk, shine take mata iso a gabansa?
Ta daure ta hadiye damuwarta ta yi kamar bata ga hannuwansu a sarke ba, ta cewa Farida "Sannun ki".
Daga inda take tsaye ta kalli Mk ta ce "ya ya jikin?"
Daga haka ta tsuke bakinta, tana karanta duk addu'ar da ta zo bakinta, tabbas Mk ne ya wula'kanta ta saboda ya nunawa Farida ita ba wata tsiyar ba ce. Shiyasa ya ki zame hannunsa da yake cikin nata.
Amma ai ya yi da yar halak.
A hankali Mk yake kallonta ta kasan ido, yana nazartar yadda take kokawa da fishin da ya ke yun'kuro mata.
Cikin hikima ya zare hannunsa a hannun Farida, gumi sai yanko masa yake yi.
Da sauri Farida ta 'kara karfin A.C da gudun fanka, saboda zufar da taga na karyo masa wadda kawai ta fargaba ce. A ransa ya dinga nazarin anya zai iya jarumtar ri'ke mata biyu kuwa? Saboda yadda ya dinga zullimin kasancewarsa a gabansu a lokaci 'daya.
Mk na wanna tsinkayen ya ga Farida ta ajiye kwandon hannunta tabbacin ta fasa tafiyar kenan.
Wato duk ha'kurin mace ta iya shu'umanci indai akan kishi ne?
Yau ya gasgata hakan domin ko kaffara ba zai yi ba, idan ya yi rantsuwar saboda Sa'adah ta 'ki tafiyar.
Dan haka ya yi kicin kicin da fuska, ita kuma sai kokarin yi masa fifta take yi.
Yayin da Sa'adah da Zainab suke ganin ikon ubangiji na yadda Farida ta kankane komai, Zainab da Mk ne suke mamakinta. Yayin da Iyah ta san dama Farida zata yi abin da ya fi haka.
Abbas ne ya leko daga bakin kofar ya ce "Farida ina ta faman jiran ki, so nake na yi maza na kai ki na dawo, kafin su tafi kar abar shi ba kowa, Hajiya ta tafi tun dazu, zan biya na dauko su Anty Amina Kuma".
Ai kuwa ta ce "je ka dauko su kawai, idan Akil ko Ahamad sun zo, sai je su dauko mini motata, ko kuma na fita na hau adaidaita sahu".
Abbas ya yi sakare yana mamakinta a ransa tare da cewa "Ah adole ita ba zata basu damar ganawa ba, duk da dai bata nuna bacin rai ko damuwa ba.
Sai a lokacin Mk ya ce" amma kin san ban son Ahamad yana hawa motar ki saboda ba ya tuki da nutsuwa, Akil kuma yana shago sai dare ya fara jah yake zuwa".
Ta marairaice ta ce "Ba damuwa sai na hau adaidaita sahu".
"A a bana so kin sani, bana so".
Ya sake sassautawa "ya ce ki je ya kai ki, ana idar da Sallar isha ki rufe gidan, sannan ki taimake ni ki sha maganin ki please".
Ya fa'da cikin sigar rarrashi da kulawa.
Amma ta yi mirisisi ta ki tafiya, lamarin da ya sake dagula lissafin Sa'adah, wai yau a gabanta wata macen take nunawa ta fita son Mk, ta fita kusa da shi.
A gabanta shima ya ke nunawa wata macen tattali da kulawa? Wannan shine duniya rawar yanmata.
Shirun da Farida ta yi ya tabbatarwa da Mk bata amince bane, ya kalleta a tausashe ya ce "Ban son ki wuce lokacin shan maganin ki ne, gobe idan zaki taho, ki taho da shi, sai ki yi ta zamanki, amma yanzu taimake ni ki je ki kular mini da lafiyar ki".
Nan ma ta yi shiru, Mk ya ce "shikenan ai, tunda so kike mu kwanta gaba'daya".
Dakin ya yi shiru na mintina uku, Zainab na mamakin irin wannan al'amarin, ta kasa cewa komai duk da bakinta cike
yake da tarin maganganu, da suke bu'katar fashin ba'ki.
Irin kallon da Farida take yiwa Mk da idanuwanta masu maiko ya sa
nan da nan zuciyar Sa'a ta hauro, ta kalli Abbas dake bakin kofa yana tsayawur jiran Farida, amma ganin Sa'adah yasa ta fasa tafiyar dan kar ta samu damar 'dagawa mijinta hankali 😀
Ta ce "Uncle Abbas"
"Na'am Anty Sa'adahtu".
"Tafiya zan yi, kuma akwai sakon da zan fa'da masa, zo ka ri'ke mini shi zuwa waje na mintina kadan".
Da sauri Abbas ya shigo yana cewa "daga nan ma na zagaya da shi, dazun nan likita ya gama ce mini kwanciyar ta yi yawa, ya dinga yin atisaye ko a cikin dakin nan ne".
Ya isa jikin gadon ya mikawa Mk hannun, ya dago shi.
Ya sunkuya ya janyo masa takalma a a kasan gadon ya saka sannan ya mikar da shi, suka fita a hankali.
Zainab ta dinga jin wani irin farin-cikin iyakar da Sa'a ta nunawa Farida.
Sun Jima da fita sannan Sa'adah ta dauki handbag dinta zata bisu, Farida ta ce "Gogel ko zaki fitar masa da kujera, jikin nasa ba kwari har yanzu".