← Book details Yar Dandi Ceh Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 74 OF 225

Sashe 74

Yar Dandi Ceh Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read

A daddafe ya iya tashi sbda yin sallarh la'asar da aketa kira. Ya nufa toilet yana ganin jiri yayi alwala ya fito ya fice a gidan ya nufa masallaci duk daurewa yakeyi, ya isa masallacin akayi sallar la'asar dashi aka idar, ya dawo cikin gidan, ya koma falon ya dauki car key dinsa ya fito ya shiga motarshi jiki babu laka ya fice a gidan, direct gidan alhasan ya nufa, yasan by this time ze samesa a gida, kawai mafita yake nema na yadda ze rabu da Auren nan salin Alin ba tare da Amihh ta tsine masa ba, dan harga Allah bayajin ze iya hkri da wannan Kaddararren Auren da aka masa, shi dama macen arziki ce seya hkra Amma karuwa! "Baze yuba!'' Ya fadi yana driving motar Amma Hnklinshi na can ga tunani. Da temakon Allah da ma'aikinsa AB'ILAL ya isa da motarshi gidan Alhasan, yayi hon get man ya bude masa get din ya shigo yayi packing ya fito, jiki babu laka ya nufa hanyar falon Alhasan. ma'aikatan gidan nata gaidasa Amma be amsaba, to bema jisu ba, koma yanajinsun daman ba amsawa yakeyi ba. Shigowar Alhasan gidan kenan ya yada zango a falon sbda a gajiye yake yau Ainu, hannunshi riqe da Bottle water me sanyi, yanasha AB'ILAL ya turo kofar falon da karfi ya shigo babu ko sallahma. A razane Alhasan ya zubo masa ido sbda yadda ya turo kofar Falon ya shigo da karfi, seyaso ya razana Alhasan din. Kallo daya Alhasan ya masa ya gane babu lafia yau, an tabo zuciar mutumin, daman ya lafiar kura, balle tayi hauka. " aiko yau seta ALLAH," alhasan ya fadi a ranshi, yana me kara zubawa AB'ILAL ido se faman huci yakeyi. Karasowa AB'ILAL yayi ya zauna a kan kujerar 2ct se sauke ajiyar zucia yakeyi kmr wanda ya sha gudu ya gaji. "Wannan wace iriyar kofa ce mara kyau kasa a falon nan! Wannan ai iskanci ne! Da wulaknci, wannan kofar ta yan iska ce!�' AB'ILAL ya fadi a hasale, dagajin yadda yake mgnr alhasan yasan da matsifa cike da cikinsa. "Me kofar tayi?'' Alhasan ya tambayeshi cikin sanyin murya. "Au tambaya ma kakeyi me kofar tayi, ai dayake kasan kai makaho ne baka gani, ko kuma kai kuturu ne baka taba kofar kaji...mtws!" ya karashe mgnr yana tsuki, hadi da lafewa a kn kujerar, jaraba da tijara fal cikinsa. Alhasan be tanka masa ba, gudun kada abin ya wuce haka. "Allah ya temake ka, ya baka yawan rai M.A..." Alhasan ya fadi hkn kmr sarki da bafadensa. AB'ILAL ya masa bansa ya wani basar ji yakeyi kmr ma ya rufe Alhasan din da duka. Murmushin Alhasan ya sakar masa se wani faman karkada kafa yakeyi zallar mulki da tsantsar saurauta kawai, ke yawo a ruhinsa. "Ashe ka shigo kd..." Cewar Alhasan, dabe daddaraba, sbda ya riga ya saba, komi ze masa ze shanye. Ai kmr AB'ILAL na jira ya taso masa da cewa "dole mana gashi naxo, ja ganni kuma kana tambayata.., mtws hmm!'' Ya karashe mgnr yana jin zuciarsa kmr zata fashe. Alhasan ya bude baki yana kallon AB'ILAL wato de yau yana ganin ba alamar arzikima a tattare da mutumin. AB'ILAL yaci gaba da mgna a mugun hasale. " waini Amihh zatawa Auren dole, auren dole kmr wata mace, da wata tsinanniya wlhy bnsonta sena saketa tinda ba Tare mukazo dunia ba..." A hasale yake mgnr muryarsa me cike da tijara se tashi takeyi. Alhasam daya zuba masa ido, ya gane kn zancan nasa dukda ba a natse ya masa mgnr ba. "Aure kuma? Plx ka fahimtar dani sosai...wani irin Aure?" Alhasan ya jefowa AB'ILAL tambayar a matukar kid'eme. "Kasan kai kurma ne bakaji Ai,,to nace maka Aure wai Amihh tamin jiyannan, auren ma da karuwah..." Ya karashe mgnr yana me jin zuciarsa kmr zata fashe, sbda takaici da zallar baqar kiyayyar yarinyar. Alhasan duk yabi ya shiga dimauta shi kalmar karuwancin bata damesa ba, sbda yasan kowacce mace a gun AB'ILAL karuwa ce koda ma me mutumci ce. Ajiyar zucia ya sauke fuska dauke da mamaki hadi da damuwa yace "Aure? To da Hameedah ko?" a fusace ab'ilal ya amshe da cewa "inda ace mani ita ce da sauki, wannan fa karuwa ce na ce maka, ta gama gantalewarta a titi kuma wai Amihh ta rasa wadda zata hadani da ita se ita, kai wlhy ko za ayi menena sena saki yarinyarnan!'' Ya karshe mgnr Kmr zeyi kuka, ya dafe knsa dake masa azababben ciwo kamar ze tarwatse. Alhasan daya zuba masa ido yaji tausansa ya ratsa masa zucia, tabbas yasan yana cikin wani hali irin wanda be taba ganinshi a makamancinsa ba se yau. "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un!" Ita ce kalmar data fito daga bakin alhasan ya kara sauke ajiyar zucia kana daga bisani yace "To ita ma yarinyar yar kano ce kou?'' AB'ILAL da idanuwansa sukayi jajawur bemason mgnar dande beda yadda zeyi ne mafita kawai yake nema koda da tsiya ne yace "yar kd ce,.. ni bnsanma ta yaya Amihh ta sameta ba ta mannamin, wlhy frnd duk dunia yarinyarnan nafi tsana, nifa daza a bani dama da zan iya kashe yarinyarna...ita kuma Amihh dagani sonta takeyi, tinda tana ikirarin tsinemin a kan yarinyar...hmm!" Ya karashe mgnr da mugun zafin zucia har fuskarshi na huci. Alhasan ya zaro ido jin mgnr kisa a bakin AB'ILAL tabbas yasan abun babba ne. Cikin sanyin murya hadi da kwantar da hnkli Alhasan ya fara mgna "Dan ya frnd kadena mgnr kisa,..tinda bakasonta kiyayyar har tayi zafi haka kawai ka sawwaqe mata..." AB'ILAL ya furzar da wata iska daga bakinsa me dauke da huci kai kace jarumin namijin zaki ne, ya fara mgna da muryarsa data fara dishewa dan bacin rai, yaci gaba da mgna rai bb ddh "Amihh tace inna saketa seta tsinemin albarka...na rasa ya zanyi..wlhy banason yarinyarnan, ni dama wata ce se in hkra amma bazan iya hkrin zaman Aure da wannan yarinyarba, wlhy sede ko Amihh ce ta aurota kawai amma ni bani ta Auro mawa itaba..." Alhasan yayi shiru yayi kasaqe yana sauraron kalaman AB'ILAL nan da nan ya fara jin zafi dukda kuwa sanyin AC dake falon. "wannan shi ake cewa an gudu ba a tsiraba... To yar qawar Amihh ce ko yaya ne?" AB'ILAL ya masa bnza a wannan karon se aikin cusa hannunshi yakeyi a cikin sumar kansa. Kwantar da murya Alhasan yayi kana ya fara masa mgna. "Plx aboki ka rinka daukar abu a sannu se yazo maka a sannu, in zaka karanta lamarinnan kaddara ce, kaga munsa Amihh ta dawo kd daga kano sbda Kada ta maka Aure, se gashi ashe a nan din zata maka Auren...dan ALLAH ka dauka da sanyi plx..." Ya karashe mgnr da sigar rarrashi. A hasale gogan ya kara Amshewa da "Ta yaya zan dauka da sanyi ? Karuwa ce fa, da mutuncina ka auramin mazinaciyya, me yafi wannan zafi dan ALLAH?'' AB'ILAL ya fadi cikin zafin rai, kai dajin yadda yake mgnr kasan abin na cinsa inside. "A ina ka tabbatar da ita karuwa ce plx? Ba kyau fa plx kabi a hnkli..." Alhasan ya fadi da sanyin murya shi knshi jikinsa yayi sanyi, sbda yadda yaga ikon ALLAH a zahiri. "Karuwa ce mana, in ba karuwa bace mecece, yama za ayi kace wai ta ina na tabbatar da ita karuwa ce, to kazafi na mata se kabi mata haqqinka tinda uwarku daya ubanku daya..." AB'ILAL ya fadi a matukar hasale kai kace ze tashi ne ya rufe Alhasan da duka, sbda tsabar tijara. Alhasan yayi shiru na wasu yan mintoci kawai dan yasan halin kayansa. After 5mt Alhasan yaci gaba da mgna "Ba haka nake nufi ba frnd, ynzu de shikenan kayi hkri... " "nifa sakin yarinyarnan zanyi Alhasan wlhy ALLAH bazan zauna da ita ba, dan ina iya mata lahanin dazan dauwama a gidan yari.." AB'ILAL ke mgnr cikin zafi da zuciarsa da babu sassauci ko a murya kasan babu sauki a lamarinsa. Alhasan ya zuba masa ido, ya kula duk natsihar daya masa ma a wannan halin da yake ciki da wuya yajisa saurarensanma baya tunanin yanayi, ya kula ko hkri ya basa ma se ya kwaso wani bala'in ya kara laftowa, be daddaraba ya ci gaba da masa mgna da laushin murya. ''Dan Allah frnd kada kayi kuskuren sakin yarinyarnan, tinda kasan halin Amihh, kamar yadda ka fadi tace inka saki yarinyarnan tsine maka zatayi, wlhy tsinemakan zatayi, plx mubi a hankali a rabu salin Alin, duk ci gaban da kake ganin muna samu a dunia sbda munabin Allah ne kuma munbin iyayenmu, dan ALLAH kabi a hnkli ka gama da Amihh lafia fushin iyayenmu a kn mu beda dadih frnd babbar matsifa ce, 9month ba 9days bane, kayi hakuri plx dan Allah..." Ajiyar zucia AB'ILAL ya sauke yana me jin dan sassuci a zuciarsa sbda kalaman Alhasan sun d'an shigeshi kadan ko ince wasu sun shigeshi. "Bani ruwa..." Ita ce kalmar data fito daga bakin AB'ILAL uban yan mulki se huci kawai yakeyi kmr wanda yaci gindi ya kawo ya sauka yana hutawa, kafin ya daura daga inda ya tsaya (wannan ba hucin cin gindi bane hucin jaraba ne da zallar matsifa😂) mikewa alhasan yayi ba bata lokaci ya nuda frij din dake falon, ya dauko bottle water me sanyi normal one, ya dawo inda AB'ILAL yake , ya bude ruwan ya bar murfin a kai kana ya mikawa AB'ILAL din. Ya dago kwayar idonsa da knsa dake masa nauyi ya zubawa ruwan da alhasan ke miko masa ido, seda ya dauki 5mnt yana kallon ruwan, shi kuma alhasan na tsaye beda yadda zeyi. AB'ILAL ya amshi ruwan Alhasan ya koma ya zauna kujerar dake facing AB'ILAL din ya zuba masa ido, se kallon bottle water din dake hannunsa kawai yakeyi. Yakai baki da niyar yasha, ya tuno yadda yaga yarinyar a falon uwarsa, kawai ya fasa shan ruwan dukda uwar kishin ruwan da yakeji, yayi wata irin jifa da bottle water din, ya isa ga tamfatsetsen TV dake falon ya dakeshi kana ya dawo ya fadi kasan falon ya fara zuba... Alhasan ya zuba masa ido, be taba ganin mutum me muguwar zuciaba irin ta AB'ILAL ba. kwata kwata babu sauki a lamarinsa, baqar zucia gareshi me bakin tsiya, hadi da farar matsifa, duk duniya alhasan be taba ganin tijararre me wuyar kai ba kmr AB'ILAL. Tinda ya wurgar da bottle water din ya koma ya kwanta a kn kujerar yana hadiyar mugun yawu, me mugun zafi xuciarshi se harbawa takeyi kmr ze zauce. "Plx ka rinka cewa innalillahi wa'inna ilaihirraju'un!'' Cewar Alhasan da kwayar idonshi ke kn AB'ILAL har zuwa lokacin, shifa alhasan tsoronshi Allah, tsoronci kada baqar zuciar AB'ILAL ta buga ya shiga uku ya bani ya lalace, a garin kaduna. Ajiyar zuciar kawai AB'ILAL keta faman saukewa time to time, se faman zufa kawai yakeyi, yayi amfani da abinda Alhasan yace masa, se aikin maimaitawa innalillahi wa'inna ilaihirraju'un yakeyi a zuciarsa... Alhasan ya masa kuri da ido, shima a tasa zuciar se masa fatan sassauci yakeyi, a gaskia da ace Amihh tayi shawara dashi da bata yima wannan me baqar zuciarba Aure ba, shi ba kowa ma yake tausayamawa ba, bace wadda aka hadata aure da AB'ILAL din, yasan ta shiga uku ta bani ta lalace, tabbas zeci ubanta la'ada waje..." Alhasan ya fadi a ranshi yana me ci gaba da ma abokinnasa adduarh ALLAH ya sassauta masa baqar zuciarsa.
Chapter 74 · 0% Book details