Sashe 72
Yar Dandi Ceh Part 1 Complete Hausa Novel · about 11 min read
For more information 08136349646
Gumbar madara 😋
Gumbar kankana
Gumbar Alkama
Gumbar gero
Gumbar ridi
Gumbar hatsi
Gumbar gyada
Gumbar Ayah
Gumbar me rubutun mallaka.
Tsumin tabaje
Tsumin baure
Tsumin kankana
Tsumin kwakwa
Tsumin zam-zam
Tsumin rubutu
Tsumin al'ajabu
Ingantaccen maganin infection sadidan insha ALLAH.
Ingantaccen matsi, mesa dadin gaba ga me gida, da maganin gyaran nono, maganin sa kiba, da maganin rage tumbi, maganin kara hips available.
Turaren mallala E.T.C humrar mallaka...
Masu bukatar hadin *yar gatah* komi da komi za asa a ciki na NA MALLAKA dana mgnin infection 20K 30K 40k 50k 70k 80k 90k 100k iya kudinki iya yadda zakiyi shagalinki . MATA KU TASHI KUYI GYARA SABODA MASU GIDA MAGUNGUNANMU masu inganci ne Da kyau sayen na gari maida kudi gida . 08136349646.pls karki dauki lmbata ki dameni in baki shiryaba plx.
08/01/2022 à 18:24 - SAADATU BINTU ABDULLAHI: *YAR DANDI CEH...* 🅿�21
SAADATU BINTU ABDULLAHIâœðŸ?
Tafiyar 2h ta kawoshi garin kaduna daga garin kano. Ko Packing me kyau beyi ba ya fito daga motar hannunshi riqe da car key dinsa da wayoyinsa. ma'aikatan gidan na ganinsa suka zubo a gushe suka karaso suka tsugunna suka fara kwaso gaisuwa, ko amsawa beyi ba, infect ma ko kallo basu isheshi ba, direct ya nufa hnyar shiga falon Amihh cikin isa, izza kasaita, zallar mulki. Dan ustaz ya bisa da ido yace "Wato ainifin shi wannan balarabe ne kou? Na'am shi balarabe ne...daga kasar saudi arebia.." Ya bawa kanshi amsa. silele me wankin mota dake kusa da dan ustaz din ya amshe da
"kai malam ustazu kaseeran isknci kabeeran, wannan dan masu gidanne, raba kanka!" dan Ustaz ya zaro ido yana tand'ar baki yace ''na'am, wato ainifin shi din kurma ne kou? Naga an gaisheshi be amsa ba...'' Silele yayi yar dariya yace "tab! Yanaji kar in fada maka Miskili ne na karshe...ai wannan da kake ganinsa ni banma taba ganin murmushinsa ba, tinda nake tare dasu 5yrs kenan ynzu, be murmushi ko kadan, kullum rannan nashi a hade, kmr an aiko masa da saqon mutsibah..." Dan ustaz ya zaro ido waje, yace "wato ainifin shi din haka yake!?" Silele yace "Ai yama fi hakan...ba sauki a lamarinsa..." Dan ustaz ya tande baki, hadi da hadiye miyau yace "Latagadab! Wato ainifin shikenan..." Cewar Dan Ustaz daya canza akalar mgnr dama silele natsiha kan ya dena gulma, bayan an gama shafa masa gulmar kenan, ko cikin su , dashi da silele wazewa wani wa'azi oho, dan wuta ne yakeyi da kafiri, aiko nan silele ya masa tas tas dole yaja bakinsa yayi shiru daga wa'azin nasa.
Da sallahma ya shigo falon, idanuwansa suka sauka a kan hilwah da salwah dake zaune a falon sunata hira suna murmushi, murmushin da bekai ciki ba, dukkaninsu da abinda ke ransu, sallamar tasa tasasu kallon bakin kofar, duk suka zuba masa ido, gaban hilwah ya yanke ya fadi ganin wannan guy din, a kallo daya ta ganesa, fuskarsa bazata taba goguwaba a ruhinta da zuciarta, wani irin mummunan bugu zuciarta tayi, still kwayar idonta na Kansa, yayin da shima kwayar idonshi ke kanta, ya gaza daukewa, nan ya daskare yana hasko guraren daya ganta, surarta da siffarta bazasu gushe a garesa ba, tunawa yayi da inda ya fara ganinta hotel ne, daga nan se gidan karuwai, again yanzu kuma, gata a gidansu a tsakiyar falonsu.. "Me takeyi a gidannan?'' Ya tambayi knsa yayin da yakejin muguwar tsanarta a tsakiyar zuciyarsa, kallon tsana yake jifanta dashi, gaza jurewa tayi da irin kallon da yake mata me wiyar fassaruwa ta dauke kwayar idonta daga garesa tana me jin zuciarta na tsananta bugu. Shi knshi zuciar tasa bugawa takeyi da karfi da karfi, tsantsar tsagwaron kiyayyarta na yawaita ga zuciarsa, ze iya cewa tinda uwar sa ta haifesa be taba tsanar wani ba kmr yadda ya tsani yarinyar nan. Salwah ta bisu da ido, tana me nazartarsu, musammanma yah AB'ILAL din, wanda kullum fuskarshi bb haske babu ni'ima kai kace mutuwa aka masa a kullum, ko murmushi ba yayi. "Sannu da zuwa yah AB'ILAL..."salwah ta fadi cikin ladabi. Hade rai ya karayi fuskarnan tayi duhu kar kaso ka bincika kasan ranshi, dukda yaji me salwah tace Amma bata isa ya ansa mata b, ko ince bata kai matsayin daze amsa mataba, kawai zallar mulki ne. har lokacin kwayar idonshi na kan Hilwah wadda knta ke kasa ji takeyi tamkar tayi me! zuciarta bata mata ddh sam sam , se bugawa takeyi da sauri da sauri tasan saboda shine zuciarta ke bugawa, 'meya kawoshi gidan?" Ta tambayi zuciarta... se ko zuciar tata ta bata amsa da ''maybe gidansu ne tinda ga salwah na ce mata yayah.." Hanta da jinin jikinta suka kada, nan da nan ta shiga wani sabon yanayin.... dai-dai Amihh ta fito daga bedroom dinta, tana mgna. "Hilwah kinci abinci?'' Ita ce kalmar data fito daga bakinta, daman hkn ne ya fito da ita daga dakin, danta tambaya ko hilwah taci abinci. Idanuwanta suka sauka a kan AB'ILAL dake tsaye, wanda ya zubawa Amihhn ido.... Kallo daya Amihh ta masa taga yayi wata irin muguwar rama, abun ya taba mata zucia Amma seta dake ta dannewa ranta dukda tanason sanin meye silar ramar tasa. "Ka iso kenan..." Cewar Amihh, da idonshi ke knta. Ba tare daya amsa mata tambayartaba ya nuna hilwah da yatsa yana fadin "Amihh me wannan takeyi a nan?" Amihh tabi inda ya nuna da yatsa, salwah ma ta bishi da kallo, hilwah knta na kasa tayi shiru tasan da ita yake mgnr guiwowinta sukayi mata sanyi. "Bansa niba..." Ita ce kalmar data fito daga bakin Amihh cikin tsare gida. Tambayar tasa ta bata Amihh tabbacin ya taba ganin hilwah ne a wani gurin maybe. AB'ILAL yaja bakinshi yayi shiru, sbda amsar da Amihh ta basa. Juyawa Amihh tayi ta koma dakinta, yabiyo bayanta yana sake waiwayon Hilwah, zuciarshi ta kasa dena bugawa, daya ganta ji yy kmr yaje ya shaqeta ko ya samu ta fita daga rayuwarsa. Suna shigowa dakin amihh ta karasa ta zauna gefen bed dinta. AB'ILAL kam gaza zama yayi. "Amihh meya kawo yarinyar nan cikin gidannan?'' AB'ILAL ya kara jefowa Amihh Tambayar a tsaye ya gaza zama ma, sbda dmwa. Ido Amihh ta bishi dashi, se yanzu take hango tsantsar tsanar hilwah a kn fuskarsa, a dazu ma ta hango amma ta gaza fassarawa , se ynzu ne ta iya fassarawa. Hade rai Amihh tayi tace "tuhumata kakeyi?'' AB'ILAL ya dafe kai cike da kosawa yasan meya kawo hilwah gidan. "Ba tukumarki nakeyi ba Amihh.....ina tambayarki ne plx...in yarinyarnan ce ta kawota gidannan wlhy sena kusan karyata a gidanna, yau sede a fita da ita da Ambulance...." Ya karashe mgnr a matukar hasale. "Ni uwarka ni ce na kawota gidan seka karyani, kasa a fitar dani da Ambulance din.. karamin mara tarbiya!" Amihh tayi mgnr cikin tsiwa. AB'ILAL ya zubawa Amihh ido kana yace "why amihh? Karuw...." Saurin katseshi Amihh tayi tana me jin mamakin ta yaya yasan ita din karuwa ce? Nan ta kara tabattr da cewa AB'ILAL yasan Hilwah.
"Kul! In ka karasa se naci kutmar ubanka! In wannan kalmar ta kara fitowa daga bakinka sena ci maka mutumci.." A hasale hadi da bacin rai Amihh ta fadi hkn. AB'ILAL ya zuba mata ido kmr zeyi kuka..."je kaci abinci ka dawo muyi mgna.." Amihh ta fadi hadi da dauke knta a knshi.jiki a sanyaye ya karasa ya Zauna a kasan kafafuwanta yace "Amihh bnjin yunwa..plx muyi mgnr.." Hajiya maryam ta sauke ajiyar zucia kwayar idonta na kn AB'ILAL ta rasama ta ina zata fara mgnr dake ranta, sbda reaction din da AB'ILAL ya firgitata, hkn ya nuna mata da wata a kasa. Tabbas da Aiki a gabanta dmn ya lafiyar kura balle tayi hauka. "Amihh ina jinki.." AB'ILAL ya fadi hadi da dago kwayar idonsa ya saukewa hajiya maryam, itama shi din take kallo, tasha mur ta dake, ta hade rai dmn ita din jarumar macece. "Aure nasa aka daura maka a jiya jumma'ah..." A matukar razane AB'ILAL ya dago kwayar idonsa daya sauke kasa ya kalli Amihh cikin rashin fahimtar kan gadon zancenta yace "Wani irin aure kuma Amihh?" "Aure wanda uwarka da ubanka sukayi suka haifeka ta hanyarshi.."hajiya maryam ta bashi amsa a takaice, babu alamar shakkarshi a tattare da ita. Dafe kai AB'ILAL yayi zuciarshi na kuna, tabbas yasan mgnr amihh babu alamar wasa, nan jikinsa ya hau rawa ya fara zufa dukda sanyin AC dake dakin, wani abu yazo farkon zuciarsa ya tsaya, zallar tashin hnkli ya bayyana a tattare dashi. "Aure babu izini Amihh ? Meyasa zakimin haka plx Amihh?'' AB'ILAL ya fadi murya cikin tsananin tashin hnkli, a lokaci kankani duk yabi ya gigice. "Saboda na isa yasa na maka Aure, kuma sbda na gaji da ganinka ba Aure, kusan shekara da shekaru ina hadaka da yammatan kawayena kana cimin mutumci shiyasa a wannan karon na Zartar da hukuncin daya yimin kuma kaima dole ya maka!'' Tura hannunsa yayi cikin sumar kansa, yana me jin tsantsar takaici hadi da bakin ciki, ciki hadda zazzafar kunar zucia da raima gabaki daya, be taba tsintar knsa a bacin rai ba irin na yau, wani irin aure ne wannan se kace a zamanin da babu ilmi, AB'ILAL ya fadi a ranshi. A fili yace "Gaskia bana sonta, koma wacece, wlhy bazan zauna da ita ba..." Ya fadi babu alamar tsoro a cikin muryarsa. A matukar zafafe Amihh ta amshe da "Seka zauna da ita dan ubanka, zanga cikin nida kai waya dauki cikin wani yayi nakudarshi dan dangin ubanka!, duk wani iskncinka karyarshi kakeyi Wallahi a wannan karon sena nuna maka bambamcin tsakanin aya da tsakuwa...kai karamin mara daraja ne! Aure ne An daura kuma ya dauro, har abadan, ko kana shan giyar wake baka isa ka zartar da hukunci ba a kn auren nan seda izinina..." Dago red eyes dinsa yayi ya zuba mata, idanuwansa sunyi jajawur tamkar gauta, duk yabi ya gigice ya yamutse. "Plx Amihh yaza kiyimin hk plx? Wani irin Aure ne wannan ba izini? Why pls Amihh? Dan Allah meyasa kikeyi min haka ne dan ALLAH? Kwata kwata yaushe kika dawo garinnan da har zakiyimin Aure amihh?'' Ya karashe mgnr kmr ze fashe da kuka. Amihh ta kara hade girar sama da kasa tace "ko zakayi meye sede kayi, dan ubanka Aure ne An rika an daura, kuma kaida rabuwa dashi har abadan, sede ka mutu ko ita ta mutu! Tashi ka fitarmin a daki!" Idonuwan AB'ILAL suka gaza dena kallon Amihh, zuciarsa cike take da nadanar dawowarta kd a tunaninsa da bata dawo kd ba da hakan be faru ba. ashe kaddararsa ce tasashi takura mata Dole ta dawo kaduna. "Amihh to haka aka miki, auren dole...wannan Auren dole ne kkyimin , da wadda bnsani ba, itama bata sanniba..why plx Amihh?'' Duk maganganun da yakeyi baya hayyacinsa. Amihh ta fahimci hkn, amma bata daga masa kafa ba. "Ai ynzu zakusan junan naku, aure Ai ba wasa bane..ita ce wadda ka gani a falo,..." A matukar gigice hadi da dimauta AB'ILAL ya kara kure Amihh da ido. "Ita wa kenan Amihh?'' Ya tambaya zuciarsa na masa barazanar fashewa. "Ita wadda kagani a falo da hilwah kake tambayata me takeyi a gidannan, to itace..." Amihh ta bashi amsa ko a jikinsa sam bata ma nuna nasa ta damu da reaction dinsa ba. Tsabar tashin hnkli da firgice AB'ILAL ya shiga, ya zabura ya mike tsaye yana mgna da karfin da bemasan yanayi ba duk yabi ya gigice a lokaci kankani ita knta Amihh se binshi takeyi da ido. " wannan karuwar Amihh? Kinsan wacece Wannan din Amihh? Karuwa cefa me zaman kanta a gidan karuw..." amihh ta daka masa tsawa "Ita karuwar ba a aurenta kenan? To bari kaji in gaya maka in kai baka sani ba, ..ka shiryar da karuwa ma ka Aureta lada biyu kakedashi, na daya ka shiryar da ita zuwa tafarkin Allah kuma ga ladar Aurenta da kayi cikin mutumci..ballantana ma wannan ba karuwa ba..." "Wllhy Amihh karuwa ce...a gidan karuwai fa take, ni bnsonta wlhy bna sonta, sakinta zanyi yanzu yanzunnan,...naji ko wacece ki hadani da ita mace me mutumci plx... " Yayi mgnr yana haki sbda kunar zucia. Mikewa tsaye Amihh tayi tana gyara daurin zanin jikinta ta matso daf da AB'ILAL din ta fara mgna cikin matsifa da jaraba da kafiyar kanta da yafi nasa. "Ko da dangin ubanwa kake kwana baka isa ba ka saki yarinyarnan kaji na gaya maka, zan nuna maka Ainihin wacece ni a nigeria inhar kayi kuskuren sakin yarinyarnan, Allah yasa gaf mazan duniyarnan sun santa, karshen karuwanci kenan kou? To wlhy seka zauna da ita... Kai bari in takaice maka ko a zucia ka furta kalmar saki ga yarinyarnan, kaga bama a baki ba kou? A zuciya? To wlhy ka kwana ka tashi da sanin ni da kai har abadan! Inhar ka saki yarinyarnan a zucia ma ba a fili ba, na hkra dakai a matsayin d'ana na cikina, wlhy ALLAH sede ka nemi wata uwar bade niba...har abadab!" Tinda ta fara mgnr bata dauke numfashin ba harta sauke sbda a hasale take, ajiyar zucia ta sauke hadi da numfarfashi. A matukar razane hadi da gigita da dimauta da fita hayyaci AB'ILAL ya zubawa Amihh ido, tabbas a wannan karon kalamanta sun masa tsauri, ya rasama ya zeyi da yaso yanzunnan ya laftawa yarinyar red card uku ma kuwa, Amma ina Ai be isa ba inhar yanaso ya gama da duniya lafiya.kafafuwansa suka fara neman gaza daukar gangar jikinsa ya koma ya zauna nan jasan dakin , ya dafe knsa ji yakeyi kmr ya fashe da kuka. Ficewa Amihh tayi ta bar masa dakin saboda bazata jure ganinsa a yanayin da yake ba. Ko da ta fito falon bata tadda kowa a falonba, hakan ya bata tabbacin suna dakin salwah. , direct ta nufa wani daki daya daga dakunan gidan tana shiga ta fada toilet ta dauro alwala ta fito, ta bude Waldrop din kaya na dakin, wasu sabbin hijjabs ne a jere kusan guda talatin an zubasu ne kawai sbda baki, in sunzo sunason yin Sallah, suyi sallah dashi, dukkanin dakunan gidan Akwai hijjabai. Guda daya ta dauko ta saka ta nufa dadduma ta tada sallarh nafila tana me ronon ALLAH ya sassauta lamarin sbda yayi tsauri ga AB'ILAL ya dauka da zafi ba kmr yadda hilwah ta dauka ba, Dukda ba ita ta haifeta ba Amma tayi hkri ta mata biyayyar da dan cikinta ya gaza mata, se ynzu take kara jin Hilwah a ranta....
Gumbar madara 😋
Gumbar kankana
Gumbar Alkama
Gumbar gero
Gumbar ridi
Gumbar hatsi
Gumbar gyada
Gumbar Ayah
Gumbar me rubutun mallaka.
Tsumin tabaje
Tsumin baure
Tsumin kankana
Tsumin kwakwa
Tsumin zam-zam
Tsumin rubutu
Tsumin al'ajabu
Ingantaccen maganin infection sadidan insha ALLAH.
Ingantaccen matsi, mesa dadin gaba ga me gida, da maganin gyaran nono, maganin sa kiba, da maganin rage tumbi, maganin kara hips available.
Turaren mallala E.T.C humrar mallaka...
Masu bukatar hadin *yar gatah* komi da komi za asa a ciki na NA MALLAKA dana mgnin infection 20K 30K 40k 50k 70k 80k 90k 100k iya kudinki iya yadda zakiyi shagalinki . MATA KU TASHI KUYI GYARA SABODA MASU GIDA MAGUNGUNANMU masu inganci ne Da kyau sayen na gari maida kudi gida . 08136349646.pls karki dauki lmbata ki dameni in baki shiryaba plx.
08/01/2022 à 18:24 - SAADATU BINTU ABDULLAHI: *YAR DANDI CEH...* 🅿�21
SAADATU BINTU ABDULLAHIâœðŸ?
Tafiyar 2h ta kawoshi garin kaduna daga garin kano. Ko Packing me kyau beyi ba ya fito daga motar hannunshi riqe da car key dinsa da wayoyinsa. ma'aikatan gidan na ganinsa suka zubo a gushe suka karaso suka tsugunna suka fara kwaso gaisuwa, ko amsawa beyi ba, infect ma ko kallo basu isheshi ba, direct ya nufa hnyar shiga falon Amihh cikin isa, izza kasaita, zallar mulki. Dan ustaz ya bisa da ido yace "Wato ainifin shi wannan balarabe ne kou? Na'am shi balarabe ne...daga kasar saudi arebia.." Ya bawa kanshi amsa. silele me wankin mota dake kusa da dan ustaz din ya amshe da
"kai malam ustazu kaseeran isknci kabeeran, wannan dan masu gidanne, raba kanka!" dan Ustaz ya zaro ido yana tand'ar baki yace ''na'am, wato ainifin shi din kurma ne kou? Naga an gaisheshi be amsa ba...'' Silele yayi yar dariya yace "tab! Yanaji kar in fada maka Miskili ne na karshe...ai wannan da kake ganinsa ni banma taba ganin murmushinsa ba, tinda nake tare dasu 5yrs kenan ynzu, be murmushi ko kadan, kullum rannan nashi a hade, kmr an aiko masa da saqon mutsibah..." Dan ustaz ya zaro ido waje, yace "wato ainifin shi din haka yake!?" Silele yace "Ai yama fi hakan...ba sauki a lamarinsa..." Dan ustaz ya tande baki, hadi da hadiye miyau yace "Latagadab! Wato ainifin shikenan..." Cewar Dan Ustaz daya canza akalar mgnr dama silele natsiha kan ya dena gulma, bayan an gama shafa masa gulmar kenan, ko cikin su , dashi da silele wazewa wani wa'azi oho, dan wuta ne yakeyi da kafiri, aiko nan silele ya masa tas tas dole yaja bakinsa yayi shiru daga wa'azin nasa.
Da sallahma ya shigo falon, idanuwansa suka sauka a kan hilwah da salwah dake zaune a falon sunata hira suna murmushi, murmushin da bekai ciki ba, dukkaninsu da abinda ke ransu, sallamar tasa tasasu kallon bakin kofar, duk suka zuba masa ido, gaban hilwah ya yanke ya fadi ganin wannan guy din, a kallo daya ta ganesa, fuskarsa bazata taba goguwaba a ruhinta da zuciarta, wani irin mummunan bugu zuciarta tayi, still kwayar idonta na Kansa, yayin da shima kwayar idonshi ke kanta, ya gaza daukewa, nan ya daskare yana hasko guraren daya ganta, surarta da siffarta bazasu gushe a garesa ba, tunawa yayi da inda ya fara ganinta hotel ne, daga nan se gidan karuwai, again yanzu kuma, gata a gidansu a tsakiyar falonsu.. "Me takeyi a gidannan?'' Ya tambayi knsa yayin da yakejin muguwar tsanarta a tsakiyar zuciyarsa, kallon tsana yake jifanta dashi, gaza jurewa tayi da irin kallon da yake mata me wiyar fassaruwa ta dauke kwayar idonta daga garesa tana me jin zuciarta na tsananta bugu. Shi knshi zuciar tasa bugawa takeyi da karfi da karfi, tsantsar tsagwaron kiyayyarta na yawaita ga zuciarsa, ze iya cewa tinda uwar sa ta haifesa be taba tsanar wani ba kmr yadda ya tsani yarinyar nan. Salwah ta bisu da ido, tana me nazartarsu, musammanma yah AB'ILAL din, wanda kullum fuskarshi bb haske babu ni'ima kai kace mutuwa aka masa a kullum, ko murmushi ba yayi. "Sannu da zuwa yah AB'ILAL..."salwah ta fadi cikin ladabi. Hade rai ya karayi fuskarnan tayi duhu kar kaso ka bincika kasan ranshi, dukda yaji me salwah tace Amma bata isa ya ansa mata b, ko ince bata kai matsayin daze amsa mataba, kawai zallar mulki ne. har lokacin kwayar idonshi na kan Hilwah wadda knta ke kasa ji takeyi tamkar tayi me! zuciarta bata mata ddh sam sam , se bugawa takeyi da sauri da sauri tasan saboda shine zuciarta ke bugawa, 'meya kawoshi gidan?" Ta tambayi zuciarta... se ko zuciar tata ta bata amsa da ''maybe gidansu ne tinda ga salwah na ce mata yayah.." Hanta da jinin jikinta suka kada, nan da nan ta shiga wani sabon yanayin.... dai-dai Amihh ta fito daga bedroom dinta, tana mgna. "Hilwah kinci abinci?'' Ita ce kalmar data fito daga bakinta, daman hkn ne ya fito da ita daga dakin, danta tambaya ko hilwah taci abinci. Idanuwanta suka sauka a kan AB'ILAL dake tsaye, wanda ya zubawa Amihhn ido.... Kallo daya Amihh ta masa taga yayi wata irin muguwar rama, abun ya taba mata zucia Amma seta dake ta dannewa ranta dukda tanason sanin meye silar ramar tasa. "Ka iso kenan..." Cewar Amihh, da idonshi ke knta. Ba tare daya amsa mata tambayartaba ya nuna hilwah da yatsa yana fadin "Amihh me wannan takeyi a nan?" Amihh tabi inda ya nuna da yatsa, salwah ma ta bishi da kallo, hilwah knta na kasa tayi shiru tasan da ita yake mgnr guiwowinta sukayi mata sanyi. "Bansa niba..." Ita ce kalmar data fito daga bakin Amihh cikin tsare gida. Tambayar tasa ta bata Amihh tabbacin ya taba ganin hilwah ne a wani gurin maybe. AB'ILAL yaja bakinshi yayi shiru, sbda amsar da Amihh ta basa. Juyawa Amihh tayi ta koma dakinta, yabiyo bayanta yana sake waiwayon Hilwah, zuciarshi ta kasa dena bugawa, daya ganta ji yy kmr yaje ya shaqeta ko ya samu ta fita daga rayuwarsa. Suna shigowa dakin amihh ta karasa ta zauna gefen bed dinta. AB'ILAL kam gaza zama yayi. "Amihh meya kawo yarinyar nan cikin gidannan?'' AB'ILAL ya kara jefowa Amihh Tambayar a tsaye ya gaza zama ma, sbda dmwa. Ido Amihh ta bishi dashi, se yanzu take hango tsantsar tsanar hilwah a kn fuskarsa, a dazu ma ta hango amma ta gaza fassarawa , se ynzu ne ta iya fassarawa. Hade rai Amihh tayi tace "tuhumata kakeyi?'' AB'ILAL ya dafe kai cike da kosawa yasan meya kawo hilwah gidan. "Ba tukumarki nakeyi ba Amihh.....ina tambayarki ne plx...in yarinyarnan ce ta kawota gidannan wlhy sena kusan karyata a gidanna, yau sede a fita da ita da Ambulance...." Ya karashe mgnr a matukar hasale. "Ni uwarka ni ce na kawota gidan seka karyani, kasa a fitar dani da Ambulance din.. karamin mara tarbiya!" Amihh tayi mgnr cikin tsiwa. AB'ILAL ya zubawa Amihh ido kana yace "why amihh? Karuw...." Saurin katseshi Amihh tayi tana me jin mamakin ta yaya yasan ita din karuwa ce? Nan ta kara tabattr da cewa AB'ILAL yasan Hilwah.
"Kul! In ka karasa se naci kutmar ubanka! In wannan kalmar ta kara fitowa daga bakinka sena ci maka mutumci.." A hasale hadi da bacin rai Amihh ta fadi hkn. AB'ILAL ya zuba mata ido kmr zeyi kuka..."je kaci abinci ka dawo muyi mgna.." Amihh ta fadi hadi da dauke knta a knshi.jiki a sanyaye ya karasa ya Zauna a kasan kafafuwanta yace "Amihh bnjin yunwa..plx muyi mgnr.." Hajiya maryam ta sauke ajiyar zucia kwayar idonta na kn AB'ILAL ta rasama ta ina zata fara mgnr dake ranta, sbda reaction din da AB'ILAL ya firgitata, hkn ya nuna mata da wata a kasa. Tabbas da Aiki a gabanta dmn ya lafiyar kura balle tayi hauka. "Amihh ina jinki.." AB'ILAL ya fadi hadi da dago kwayar idonsa ya saukewa hajiya maryam, itama shi din take kallo, tasha mur ta dake, ta hade rai dmn ita din jarumar macece. "Aure nasa aka daura maka a jiya jumma'ah..." A matukar razane AB'ILAL ya dago kwayar idonsa daya sauke kasa ya kalli Amihh cikin rashin fahimtar kan gadon zancenta yace "Wani irin aure kuma Amihh?" "Aure wanda uwarka da ubanka sukayi suka haifeka ta hanyarshi.."hajiya maryam ta bashi amsa a takaice, babu alamar shakkarshi a tattare da ita. Dafe kai AB'ILAL yayi zuciarshi na kuna, tabbas yasan mgnr amihh babu alamar wasa, nan jikinsa ya hau rawa ya fara zufa dukda sanyin AC dake dakin, wani abu yazo farkon zuciarsa ya tsaya, zallar tashin hnkli ya bayyana a tattare dashi. "Aure babu izini Amihh ? Meyasa zakimin haka plx Amihh?'' AB'ILAL ya fadi murya cikin tsananin tashin hnkli, a lokaci kankani duk yabi ya gigice. "Saboda na isa yasa na maka Aure, kuma sbda na gaji da ganinka ba Aure, kusan shekara da shekaru ina hadaka da yammatan kawayena kana cimin mutumci shiyasa a wannan karon na Zartar da hukuncin daya yimin kuma kaima dole ya maka!'' Tura hannunsa yayi cikin sumar kansa, yana me jin tsantsar takaici hadi da bakin ciki, ciki hadda zazzafar kunar zucia da raima gabaki daya, be taba tsintar knsa a bacin rai ba irin na yau, wani irin aure ne wannan se kace a zamanin da babu ilmi, AB'ILAL ya fadi a ranshi. A fili yace "Gaskia bana sonta, koma wacece, wlhy bazan zauna da ita ba..." Ya fadi babu alamar tsoro a cikin muryarsa. A matukar zafafe Amihh ta amshe da "Seka zauna da ita dan ubanka, zanga cikin nida kai waya dauki cikin wani yayi nakudarshi dan dangin ubanka!, duk wani iskncinka karyarshi kakeyi Wallahi a wannan karon sena nuna maka bambamcin tsakanin aya da tsakuwa...kai karamin mara daraja ne! Aure ne An daura kuma ya dauro, har abadan, ko kana shan giyar wake baka isa ka zartar da hukunci ba a kn auren nan seda izinina..." Dago red eyes dinsa yayi ya zuba mata, idanuwansa sunyi jajawur tamkar gauta, duk yabi ya gigice ya yamutse. "Plx Amihh yaza kiyimin hk plx? Wani irin Aure ne wannan ba izini? Why pls Amihh? Dan Allah meyasa kikeyi min haka ne dan ALLAH? Kwata kwata yaushe kika dawo garinnan da har zakiyimin Aure amihh?'' Ya karashe mgnr kmr ze fashe da kuka. Amihh ta kara hade girar sama da kasa tace "ko zakayi meye sede kayi, dan ubanka Aure ne An rika an daura, kuma kaida rabuwa dashi har abadan, sede ka mutu ko ita ta mutu! Tashi ka fitarmin a daki!" Idonuwan AB'ILAL suka gaza dena kallon Amihh, zuciarsa cike take da nadanar dawowarta kd a tunaninsa da bata dawo kd ba da hakan be faru ba. ashe kaddararsa ce tasashi takura mata Dole ta dawo kaduna. "Amihh to haka aka miki, auren dole...wannan Auren dole ne kkyimin , da wadda bnsani ba, itama bata sanniba..why plx Amihh?'' Duk maganganun da yakeyi baya hayyacinsa. Amihh ta fahimci hkn, amma bata daga masa kafa ba. "Ai ynzu zakusan junan naku, aure Ai ba wasa bane..ita ce wadda ka gani a falo,..." A matukar gigice hadi da dimauta AB'ILAL ya kara kure Amihh da ido. "Ita wa kenan Amihh?'' Ya tambaya zuciarsa na masa barazanar fashewa. "Ita wadda kagani a falo da hilwah kake tambayata me takeyi a gidannan, to itace..." Amihh ta bashi amsa ko a jikinsa sam bata ma nuna nasa ta damu da reaction dinsa ba. Tsabar tashin hnkli da firgice AB'ILAL ya shiga, ya zabura ya mike tsaye yana mgna da karfin da bemasan yanayi ba duk yabi ya gigice a lokaci kankani ita knta Amihh se binshi takeyi da ido. " wannan karuwar Amihh? Kinsan wacece Wannan din Amihh? Karuwa cefa me zaman kanta a gidan karuw..." amihh ta daka masa tsawa "Ita karuwar ba a aurenta kenan? To bari kaji in gaya maka in kai baka sani ba, ..ka shiryar da karuwa ma ka Aureta lada biyu kakedashi, na daya ka shiryar da ita zuwa tafarkin Allah kuma ga ladar Aurenta da kayi cikin mutumci..ballantana ma wannan ba karuwa ba..." "Wllhy Amihh karuwa ce...a gidan karuwai fa take, ni bnsonta wlhy bna sonta, sakinta zanyi yanzu yanzunnan,...naji ko wacece ki hadani da ita mace me mutumci plx... " Yayi mgnr yana haki sbda kunar zucia. Mikewa tsaye Amihh tayi tana gyara daurin zanin jikinta ta matso daf da AB'ILAL din ta fara mgna cikin matsifa da jaraba da kafiyar kanta da yafi nasa. "Ko da dangin ubanwa kake kwana baka isa ba ka saki yarinyarnan kaji na gaya maka, zan nuna maka Ainihin wacece ni a nigeria inhar kayi kuskuren sakin yarinyarnan, Allah yasa gaf mazan duniyarnan sun santa, karshen karuwanci kenan kou? To wlhy seka zauna da ita... Kai bari in takaice maka ko a zucia ka furta kalmar saki ga yarinyarnan, kaga bama a baki ba kou? A zuciya? To wlhy ka kwana ka tashi da sanin ni da kai har abadan! Inhar ka saki yarinyarnan a zucia ma ba a fili ba, na hkra dakai a matsayin d'ana na cikina, wlhy ALLAH sede ka nemi wata uwar bade niba...har abadab!" Tinda ta fara mgnr bata dauke numfashin ba harta sauke sbda a hasale take, ajiyar zucia ta sauke hadi da numfarfashi. A matukar razane hadi da gigita da dimauta da fita hayyaci AB'ILAL ya zubawa Amihh ido, tabbas a wannan karon kalamanta sun masa tsauri, ya rasama ya zeyi da yaso yanzunnan ya laftawa yarinyar red card uku ma kuwa, Amma ina Ai be isa ba inhar yanaso ya gama da duniya lafiya.kafafuwansa suka fara neman gaza daukar gangar jikinsa ya koma ya zauna nan jasan dakin , ya dafe knsa ji yakeyi kmr ya fashe da kuka. Ficewa Amihh tayi ta bar masa dakin saboda bazata jure ganinsa a yanayin da yake ba. Ko da ta fito falon bata tadda kowa a falonba, hakan ya bata tabbacin suna dakin salwah. , direct ta nufa wani daki daya daga dakunan gidan tana shiga ta fada toilet ta dauro alwala ta fito, ta bude Waldrop din kaya na dakin, wasu sabbin hijjabs ne a jere kusan guda talatin an zubasu ne kawai sbda baki, in sunzo sunason yin Sallah, suyi sallah dashi, dukkanin dakunan gidan Akwai hijjabai. Guda daya ta dauko ta saka ta nufa dadduma ta tada sallarh nafila tana me ronon ALLAH ya sassauta lamarin sbda yayi tsauri ga AB'ILAL ya dauka da zafi ba kmr yadda hilwah ta dauka ba, Dukda ba ita ta haifeta ba Amma tayi hkri ta mata biyayyar da dan cikinta ya gaza mata, se ynzu take kara jin Hilwah a ranta....