← Book details Yar Dandi Ceh Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 38 OF 225

Sashe 38

Yar Dandi Ceh Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read

🅿�12
Dukkaninsu babu wanda zuciyarshi bata dukan uku uku musammanma Hilwah data kasa dago kwayar idonta ta kalleshi, nan take jinin dake jikinta ya daskare ya dena motsi ta kasance kmr mutum mutumi. A bangaren AB'ILAL kam zubawa hilwah ido yayi baya ko kyaftawa a zahirin gaskia ya hango wadansu irin qualities a tattare da ita, to amma daga yanayin shigarta yanada tabbacin ba macen arziki bace, kwata kwata babu alamar kamala a tattare da ita, nan take yaga duk qualities dinta sun rushe a idanuwansa, sun tashi a banxa. "YAR DANDI CEH...." Zuciyarshi ta bashi wannan batun me mugun zafi, wata irin tsanarta me tsanani tayi wankan tsarki tayiwa zuciyarshi dirar mikiya, nan da nan yaji kmr ya kasheta sbda tsabar tsananin kiyayyarta, mace har mace amma dagani yar dandi ce, wato karuwa ce. Nan da nan zuciyarshi ta bashi kila ma ynzu hk daga gun iskanci take Idanuwanshi suka riked'e suka chabza launi, nam take ya antayowa hilwah kallon tsana, se ynzu yake nadamar zuwanshi hotel din sbda ganin MUMMUNAR halittar ta me kyan dan maciji da yayi. Haka kawai ta tsinci knta dason ta dago kwayar idonta ta bashi hkrin bangajeshin datayi sbda tanada tabbacin ita ce me lefi kasancewar bata hayyacinta tasan ita ce ta bangajeshi sbda ba kallon gabanta takeyi ba hasalima kanta na kasa. Dago kwayar idanuwanta tayi ta sauke a knsa nan suka hada ido cikin ido, a lokaci kankani ta gano wani irin kallo yake mata me wuyar fassaruwa, AB'ILAL kam seda ya lumshe kwayar idonshi a duniya ba a tabayin macen data kalleshi ba ya dauke kwayar idonshi ba se a knta , tabbas akwai WATA a kasa. "Am....am....am... Ve...ry...sor..ry..." hilwah ta fadi cikin tsananin kid'imewa yayinda muryarya ke assarfa tana tsarkewa sbda tsabar tsantsagwaron kyaun guy din kasancewar ta dan kallaceshi amma ta hango wani irin kyau nasa na musamman me tada hankalin ya mace me lafia da kuzari. Tinda ya dauke kwayar idonshi a cikin nata be kara bari sun hada ido ba, sbda kwayar idonta nada wani irin sihirtaccen sehirin da besan na meye ba shide yasan da suka hada ido seda duk jinin dake jikinsa ya tashi, ita kanta burarshi seda tayi wani irin mugun amsawa this is the first time da burar shi ta amsa a sanadiyar yaga d'iya mace. Lallai yanada tabbacin beda sa'arh, y fadi hkn a ranshi yana karewa jikin hilwah kallo yna me bakin cikin yau farkon farajin feeling dinshi a kan yar DANDI ceh, shi yasa yakeda tabbacin beda sa'arh a rayuwarshi, dayasan hk ne da be rako Alhasan ba, tin ynzu ya fara nadamar rakiyar da yayi ma Alhasan. Hk kawai jikinta taji ya mata sanyi saboda BOYEYYEN AL'AMARIn data karanto a cikin kwayar idonshi nan da nan taji zuciarta ta kara tsananta bugu, maida kwayar idonta kasa tayi tana kallon wayarshi data fadi kasa ta mace sanadiyar faduwar da tayi, se hand bag dinta data fadi a hannunta, so takeyi ta tsugunna ta dauko masa wayarshi ta bashi maybe ko shine silar dayasa ya jefeta da BOYEYYEN kallo me cike da lamari masu wiyar fassaruwa tabbas kanta yayi nauyi baze iya dauka ba, sam bazata iya fassara kallon daya jefeta dashi ba a matsayin ko na menene. Sunkuyawa tayi jiki babu laka da niyar ta dauko wayarshi data fadi kasa ta bashi kuma ta bashi hkri, kawai AB'ILAL yayi saurin sunkuyawa da niyar ya dauki wayarshi daidai itama ta kai hannu ya kai hannu babban yatsanshi na hannun dama da babban yatsanta na hannun dama sukayi hanzarin kaiwa junansu wani irin wawan kiss seda duk jikinsu ya amsa, kowannensu jikinshi ya dauki vibrating musammanma hilwah, seda wani azababben ruwa me muguwar azababben dadih ya zubo daga kasan ramin tsuliyarta. Da sauri AB'ILAL ya janye yatsanshi ya dauki wayar shi zuciarshi cike da tsanarta wadda keta kara karuwa a zuciarshi shi kyamartama yaji yanaji. Riqe inda bata riqe ba yayi a wayar domin hatta da inda ta riqe a wayar yaji ya tsaneshi gaba daya! In takaixe muku Wayarma gabaki daya yaji ya tsaneta sbda tabatan da hilwah tayi. Miqewa yayi tsaye yana me bin hilwah Dake duqe da wani mugun kallo me cike da muguwar tsantsar tsagwaron bakinkirin din tsanarta. hilwah ta dago kwayar idonta still taba duqe kawai ta zuba masa ido tabbas kallon da yake mata ba a taba mata irinshi ba tinda uwarta ta kawota doron kasar duniya , dan hk bata iya fassarashi dallah-dallah amma tabbas tanada tabbacin kallon da yake mata yana cike ne da tsantsar tsagwaron tsanarta hadi da muguwar kiyayyarta. Wani irin dogon tsuki yaja ya riqe wayar hannunshi a wulaknce ya juya fuuuuuhh! Kmr fitar iska a tayar mota, yabar gurin direct cikin hotel din ya nufa zuciya narke da tsabar bakin ciki da takaici hadi da gundumemiyar kiyayyar hilwah, ji yakeyi daya jima a gurin yana iya sumar da yar iskar. Hilwah shiru tayi ta bishi da ido a zuciyarta tana nazarin tsukin da yayi ko na menene oho, harya bace da ganinta amma bata bar kallon inda yabi ba. wani irin duka kmr gangah taji zuciarta nayi, yayin da duk jinin dake yawo a jikinta ya dauki sanyi akasin da, daya dauki mugun zafi. Gaf ilahirin vitamins A-B-C-D din dake jikinta suka sauka duka at one time kuma a lokaci kankani ta gaza tsugunnuwa kawai tayi koma ta zauna dirshen zaman yan bori a kasan hotel din Allah yaso ko ina tas tas yake kmr a yadda mace a hau bisa kai sbda tsabar tsabtar gurin. Gaf ilahirin jikinta ta sakeshi dabas a kan tantsama tantsama din duwawukanta dake zaune kasa, shiru tayi kmr me nazari ta dafe hannayenta duka biyu a kasa, still kwayar idanuwanta masu jahilin kyau suna bisa kallon hanyar da AB'ILAL yabi wato hanyar shiga hotel din, harga ALLAH ba a taba yin namijin dataji ya burgeta ba se yau, se haskako surarsa kawai takeyi a kwayar idonta tana lumsar kwayar idon nata yayinda kasanta keta tsiyaya, amma kwakwalwar kanta na riqe gam da reaction din AB'ILAL a kanta hadi da uban tsukin daya ja ba karamin tsayawa a ranta tsukin yayi ba, dan bata ankare da cewa sbda ta taba mishi waya bane ya riqe wayarshi a wulakance, ita de kawai tasan tsukin dayaja yana dauke da ma'anoni daban daban, wanda in za a Tara kaf mutanen duniya basu isa su fassarashi ba ,dole se in shine din ya fassara abinshi da kankin kanshi. "Awww!" Ta sauke ajiyar zucia hadi da fitar wani irin sound daga daddadan bakinta, taja numfashi a wahalce kai kace bura aka gama narka mata irin ta gajin nan ne iya kar gajiya.... A haka kankana ya zo ya sameta zaune zaman dirshan a kasa kmr wata zararriya ko yace tantiriyar yar bori ta gidan dandi. Fuskarshi dauke da mamaki ya tsugunna ya dauki bag dinta wadda ita ya fara cin karo da ita a hnyarshi ta karasowa inda take, kwayar idonshi na kan hilwah yayin da ita kuma kwayar idonta ke kan Hanyar nan da AB'ILAL yabi ya bace mata. Zuciya da fuskar Kankana dauke da dumbin mamaki hannunshi riqe da hand bag dinta daya tsugunna ya dauka ya karaso inda take yana kwarkwasa hadi da dafe kirji yana fadin ."yauni na shiga uku ni kankana! Mezan gani haka uwar dakina? To ni ko mugun gamo kikayi ne? Oh ni kankana na shiga ukuh! Mugunji mugun Gani ALLAH ka kiyashemu dagashi! Uwar dakina lafiya da zama a kasa? Ke ba bokaye kike bi ba ballan tana ince wani lakanin aka baki ..." Kankana ya hau jero zance fuska dauke da mamaki idonshi na kn hilwah. Seda kankana yayi mgna ta gane ya karaso gurin ajiyar zucia ta sauke a wahalce ta dawo da kwayar idonta kan kankana. "Uwar dakina ko shafar jinnu ne, muje mu tattaro limamai da manya manyan malaman anguwa,.." Cewar kankana dake mgnr cikin kwarkwasa. Jiki a sanyaye hilwah ta fara yunkurin miqewa tsaye, amma ta gaza, kankana ya miqo mata hannunshi na dama ta riqe da temakonshi ta miqe tsaye jiki a tsanyaye kai kace cinta akayi bata kawo ruwa ba aka zare. "Uwar dakina menene?" Kankanah ya kara jefo mata tambaya ganin yadda duk tabi ta susuce kmr hawan jinnu. Ba tare da hilwah ta bashi amsar tambayar da yayi mata ba tace da kyar "Bu de min mota plx .." Yadda tayi mgnr kawai ya tabbatrwa da kankana akwai wani abu daya faru da ita, domin kuwa a muryarta kai kace mara lafiya ce. Ba tare daya bata lokaci ba ya dauko car key din daya jefa a hand bag dinsa ya bude motar, kana ya bude mata mazaunin gaba kujerar me zaman banza ta karasa ta shiga tana cije kasan lefe har zuwa lokacin zuciyarta na tsananta bugu, kankana na kokarin maida murfin motar ya rufe ya tsinkayi muryarta tana mgna cikin sanyi. "Bag dina na nan kasa ka dauko min plx .." Kankana ya nuna mata bag din ba tare da yayi mgna ba danshi abin ya daure masa kai, shiru kawai tayi ta miko hannu ta amshi bag din tata ya mayar da murfin motar ya rufe da tunani tunani a zuciarshi ya zagaya mazaunin dreva ya bude ya shiga. "Ka kunna min AC pls..." Ta fadi still cikin sanyin murya kai kace ba muryarta bace. Ba bata lokaci kankana ya tada motar, ya kunna AC din motar ya kureta lamba daya ce babu a zuwanta karshe, ajiyar zuciar hilwah ta sauke ta danna wasu numbers a gefen kujerar data ke zaune, nan kujerar ta kwanta tayi bending a kan kujerar tana sauke ajiyar zucia sanyin AC na ratsata, kankana de ya zuba mata ido, yayin da nata kwayar idon ke a lumshe ya tada motar suka fice a hotel din. Ba tare da yayi ma Amal sallama ba daga cewa yana zuwa bari yaje yaga uwar dakinshi ina tayi kasancewar car key na hannunshi, shine yazo ya tarar da wannan baqon yanayin. Tinda suka hau titi yana ankare da ita se sauke ajiyar zuciya kawai takeyi idanuwanta na lumshe. "Uwar dakina wai meya faru ne?" Kankanah ya kara tambayarta cikin damuwa. Shiru kawai ta masa saboda bata da bakin magana, abu daya kawai take iya tunawa a wannan halin shine wannan guy din, kawai tsarinsa ya mata Ainun, ta gaza fassara dalilin dayasa ya mata , ko ince ta gaza fassarar menene ma'anar ya mata har ga ranta, kuma menene silar dataji sha'awarsa ta darsur mata a xucia da gangar jiki. Kara rintse idanuwanta tayi gam tana juyi a kan kujerar datake kwance... Jefi jefi Kankana na juyowa yana satar kallonta tabbas yanason sanin menene ya haifar mata da Wannan yanayin da be taba ganinta a cikinsa ba se yau. A haka suka isa gidanta direct kankana na packing ta fita a motar jikinta a sanyaye, ya dauko bag dinta ya fito ya biyota a baya zucia fal damuwa, a falo ta yada zango ko damar isa ga bedroom dinta bata yiba, a kasan carpet ta kwanta jikinta a sanyaye ta lumshe idanuwanta tana me tunano yanayin halittar AB'ILAL me firgita manyan mata,. Kankana ya zauna kusa da kanta ya zuba mata ido ya hau jero mata tambayoyi , shiru ta masa ba tare data bashi amsa ba, ji tayi ma yana damunta sbda yana katse mata tunanin wannan guy din me kyau, shine sunan data bashi a ranta me kyau, tabbas taga maza iri iri sannan taga masu kyau iri iri amma bata taba ganin me kyaun guy dinba tinda uwarta ta kawota dunia, wato de ita tanada wani irin boyayyen kyau ne da babu me fahimtarsa se ita din da kanta... Kankana yayi juyin dunia ta gaya masa meya faru Amma ta masa bnza karshe ma daga masa hannu tayi alamar yana damunta dole yaja bakinshi yayi shiru....ta umurcesa daya kunna mata AC dake falon, ya tashi ya kunna AC din jikinsa a sanyaye ya dawo ya zauna, tace ya kawo masa cocaine ya dauko mata, ya kawo mata ta amsa jikinta na rawa ta zuba a hannunta daga nan kwance ta fara shaqarta kmr zautacciya ko ince me shirin zaucewah... Kankana ya zuba mata ido... Nan da nan ta farajin wani irin sanyi a ranta yayinda knta ya fara mata cool, nan take ta hau slow kmr tsohuwar motah...
Chapter 38 · 0% Book details