← Book details Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 92 OF 211

Sashe 92

Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

         Duk da a yanda aka buɗe ƙofar Yoohan baiko motsaba balle yabar abinda yakeyi. Sai Solomon ne ya miƙe zumbur yay magana cikin daka tsawa. Cikin harshen nasara yace, “Kai wanene zaka shigo nan babu neman izini?”.
      Wani banzan kallo Abdallah yayma Solo, sai kuma ya maida idonsa ga Yoohan da har yanzu bai ɗago ya kallesu ba, baima nuna alamar yasan da shigowar tasu office ɗin ba. Hakan sai ya sake fusata Yah Ab, shima a tsawace yace, “Tsaya matsayinka na bodyguard yaro, dan ubangidanka ne dai-dai da ni”.
      Solomon zaiyi magana Yoohan da har yanzu ɗin bai ɗago ba ya ɗaga masa hannu alamar kar yace komai. Shirun kuwa Solo yayi ransa na masa ƙuna da takaicin rashin sauran ƴan uwansa.
        Cike da ƙasaita Yoohan ya ɗago fuskarsa da ada p-cap ta rufe kusan rabi saboda kansa da ke a duƙe. Manyan idanunsa ya sauke akan Abdallah, sai kuma ya maida kansu Mahmood da ke tsaitsaye suma. Batare da yayi magana ba yay musu nuni da wajen zama cike da basar da yanayin da ya ga fuskokinsu.
      Abdallah ne yaja tsaki da ƙarasawa gaban table ɗin Yoohan ɗin, cike da kaushin murya yace, “Ba zaman shan ac da kallon syringe ya kawomu ba, munzo arresting naka ne”.
     Ɗan jim Yoohan yayi kamar bazaiyi magana ba, sai kuma ya motsa laɓɓansa a hankali yace, “For......?”. A takaice cike da rainin wayo
        A hasale Yah Abdallah ya jefa masa farar envelope ɗin hannunsa.
      Da farko Yoohan baiyi niyar dubawa ba, sai dai ganin tsantsar kamannin Abdallah da su baba malam ya sakashi ɗaukar Envelope ɗin, hotunan ciki ya fiddo. A karon farko ƙirjinsa ya ɗan buga saboda cin karo da abinda baiyi tsammanin gani ba. Da kafin ya musulinta ne akazo masa da wannan hoton da yake kissing ɗin Nu'aymah bazai nuna ya damuba, amma a yanzu yana matuƙar sake ƙyamatar wannan ɗabi'ar, idan kuma ya tuna ya aikata akan kuskure yana jin matuƙar takai ci. Kallon na biyu da na ukun yay su ma, amma duk da haka sai ya dake, ya sake tsuke fuska fiye da yanda suka sameta yana jifan Abdallah da yake masa kallon tsana da ƙyama shima da kallo wulaƙanci.
     Kafin wani a cikinsu ya samu damar cewa wani abu Dr Aysha ta shigo office ɗin ita da Dr Mubarak, dan sunyi knocking har sau biyu basuji ya amsa ba. A zatonsu ko yayi busy ne shiyyasa suka shigo kawai tunda sunsan babu wani mara lafiya da zai duba bayan Nu'aymah kamar yanda ya sanar musu tunkan yazo.
      Da mamaki suke bin su Abdallah da kallon tsoro, sai kuma suka kalli Dr Yoohan ɗin shima. Ganin yanda ya tsuke fuska ya sakasu kasa masa tambayar dake a bakunansu, sai Dr Mubarak ne ya kalli Solomon da ya gama tsumewa da baƙin ciki. “Solomon mike faruwa anan ne?”.
       Solomon zai basu amsa Yoohan ya katsesa da faɗin, “Mi kuke buƙata?”. Shiru Solo yayi dan ya fahimci Yoohan ɗin baya buƙatar ya faɗa. Suma jin hakasai duk suka sake maida kallonsu garesa, cike da ƙarfin hali Dr Aysha tace, “Dama mahaifin yarinyar ne ya zo, shine nace a shigo da shi?”.
      Kansa kawai ya gyaɗa mata, sannan ya maida dubansa ga su Abdallah “Zaku iya fita ga ƙofa ko”. Ya faɗa cike da tsantsar rainin hankali. Abdallah zaiyi magana Mahmood ya matso da sauri yana nunama Yoohan I'd card ɗinsa. Hakan yayi dai-dai da shigowar Baba malam office ɗin bisa jagorancin Dr Aysha.
        Mahmood da ya fara faɗin, “Muɗin jami'ai ne daga hukumar s......” ya kasa ƙarasawa saboda tozali da baba malam. Yoohan ma mamakin ganin baba malam ɗinne ya sakashi sakin hotunan hannunsa saman desk ɗin.
         Baba malam kuma da duk ke binsu da kallon mamaki ya sauke idanunsa kan Yoohan a ƙarshe. Takawa yay a hankali zuwa gaban tebirin, ya kai hannu ya ɗiba hotunan dan tun daga inda yake yana hango komai na cikinsu. Ɗauka yay ya sakasu cikin envelope ɗin. Kafin ya samu damar faɗin wani abu saboda nauyi da bakinsa yay masa Abdallah yace, “Abba munafukin nan ashe likita ne anan, dan hak.......”
       Baba malam yay saurin girgiza masa kai, mamakinsa na sake bayyana sosai da ganin Yoohan ɗin wai matsayin likita. Koda wasa bai taɓa kawo hakan a ransaba shikam, hasalima ya ɗauka Yoohan ɗan kasuwa ne kawai.
        Yoohan dai ya gaza yin magana, kallon baba malam ɗin kawai ya ke ko ƙyafta ido bayayi. Baba malam ya ajiye envelope ɗin yana duban su Mahmood. “Zaku iya tafiya abinku mun gode”. Kamar Abdallah zaiyi magana sai kuma yayi shiru, sai ma alamar su Mahmood suje ɗin kawai yay musu da kai. Batare da Mahmood yace komaiba ya nunama yaransa hanyar fita suka fice badan ransu yaso hakanba.
         Bayan fitar tasu babu wanda ya iya sake yin magana a office ɗin har tsahon kusan mintuna biyu, sai Abdallah ne keta antayama Yoohan harara, Solomon kuma na hararsu gaba ɗayansu. Dan duk haushi suke bashi.   
       Cikin ƙarfin hali Yoohan ya duba Dr Aysha da Solomon. Murya a sarƙe yace, “Kuje zan neme ku”. Babu wanda yay musu a cikinsu suka nufi hanyar fita kowanne da abinda yake kissimawa a cikin zuciyarsa.
         “Dama kai likita ne Yahya?”.
  Kai Yoohan ya jinjina ma baba malam da yay tambayar, yace, “Eh Uncle”.
    Murmushi baba malam yayi a karo na farko, yace, “Masha ALLAH, ALLAH ya sanya albarka, yay riƙo da hannunka wajen aikata alkairi ga al'umar MANZON ALLAH ”.
     Cike da jin daɗi Yoohan ya amsa da “Amin” kansa a ƙasa dan ya kasa kallon baba malam ɗin, harga ALLAH kwarjini yake masa matuƙa, musamman ma yanzu da yaga hotunan nan duk da bai tabbatar da alaƙar dake tsakanin baba malam ɗin da yarinyar da har yanzu shi ko sunanta ma bai saniba.
          Cike da takaici Abdallah yace, “Abba mutum nan fa shineya lalata rayuwar Nu'aymah, ta yaya zamu cigaba da fiskantarsa kamar munajin tsoronsa?”.
        Da turanci Abdallah yay maganar, dan haka Yoohan yaji komai, ya kuma fahimci komai. Sai dai kafin yace wani abu baba malam ya kalli Abdallah fuskarsa na nuna ɓacin rai, sai dai kuma baice komai ba. Yanzun ma shiru Abdallah yay badan yaso hakanba, sai dai yanda yake sauke huci zai tabbatar maka cewar zuciyar ƴan mazan a wuya take.
       Fuuu ya fice a fusace da ga office ɗin. Da ga baba malam har Yoohan duk binsa sukai da kallo............✍

______________________
ZAFAFA BIYAR 2021
_______________________

Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

          Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗

        Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗

        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗

         Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋

    Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
[5/27, 2:14 PM] +234 806 269 3623: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.

No. 38

.............Duk yanda su Abdallah sukaso a tuhumi Yoohan tun a asibiti game da zancen Nu'aymah baba malam ya hana, hakama su Abba basu bada goyon baya ba.
      Zuwa yanzu dai Yoohan ya fahimci alaƙar baba malam da patient ɗinsa. Ya kuma gane Nu'aymah. Sai dai taka maimai abinda bai gama fahimta ba shine hotunan da Abdallah ya kawo masa da tsantsar ɓacin ran da yake ganni tattare da samarin gidan su baba malam ɗin gaba ɗaya harsu malam ƙarami da ya fara sabo da su. 
Chapter 92 · 0% Book details