← Book details Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 173 OF 211

Sashe 173

Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

       Yoohan ko takan gidansu bai sake biba. ya dai saka Omar zuwa da mai saka keys ya sabunta duk keys ɗin dake a sashensa. Da yake lokacin duk ƴan gidan sun fita, su mama debora kuma na wajen Gebrail sai babu wanda yasan mi akayi. Solomon dai yaso shiga ya duba sai dai fitowar Omar yay masa katanga da hakan. Dan yana kai mai saka keys ɗin shi fitowa yay dan ya hana su Solomon ɗin kowacce damar sanin abinda ya farun. Sosai ya jima da fahimtar wanene Solomon dama. Labarin korosa da Aymah tasa akayi kuma da Yoohan ya bashi ne ya sake tabbatar masa akwai wata a ƙasa. Sai dai komai sake ɗaure kansa yakeyi shikam. Dan baiga miye dalilin aikata abu a sarƙaƙe da su papan keyiba game da Yoohan ba.

           Shiri yay tsaf domin shiga Kano. yanason daga Kano Lagos zai nufa. Yay kwana uku su juya U.S shi da Omar.
     Misalin huɗu kuwa Yoohan da Omar suka iso anguwar su Nu'aymah. Kasancewar anata hada-hadar shiga salla sai kawai suma sukai alwala suka shiga. Bayan an idar sun fito Yoohan yaketa faman jan ƙananun tsaki saboda kallon damutane suketa musu. Duk da yasan wasu a cikinsu sunriga da sun sanshi zuwa yanzun. Amma duk sanda zaizo basa iya daina binsa da kallo kamar wani baƙo. Ya rasa mi suke kallone wai? Gashi shi kuma ya mugu-mugun tsanar a sakamasa ido.
      Umar daya san dokar dai yanata murmushi. Dan ya tabbatar kallon ne ya bama Yoohan ɗin haushi. Bai dai ce komaiba har suka sami iso daga baba malam ta hanyar malam ƙarami daya fito ya gansu. Sakawa yay malam ƙarami shiga dasu cikin gida, shi kuma ya nema alfarmar ɗalibansa shima yabi bayansu. Sashen hajjo aka kaisu. Dan mutuniyar Yoohan ce yanzu sosai. Danma bajin zancen juna sukeba sai da tafinta. Amma a wannan karon hajjo ta fahimci Yoohan ya fara jin hausa kaɗan-kaɗan. Takoji daɗi, duk da harshen nasa a karye yake. Wani abunma koya faɗa bata ganewa.
      Sosai aka cika musu gaba da kayan ciye-ciye. Shi dai Omar nasa kallo ne da tayasu dariya. Dan yau ne karan farko daya shigo gidan. Anan baba malam ya samesu kuwa. Suka gaishesa da tsantsar girmamawa. yayinda shima da kulawa yake amsa musu da tambayar iyali. Da ga haka suka ɗan zauna hira. Anan hajjo kejin Omar ma abokin Yoohan ɗinne, kuma ya muslinta. Daɗi sosai ya sake kama Hajjo. Lallai tarkonsu ya kama kurciya. Dan ga nasasorin auren Yoohan da ɗiyarsu nan sun fara bayyana.
      Daga Sashen Hajjo baba malam ya shiga da su dan su gaida Umm. Yasan dai ganin Yoohan ɗin zaisa taji sanyi a ranta da raguwar kewar Nu'aymah. Aiko hasashen baba malam ɗin yayi dai-dai. Dan sosai Umm taji ɗunbin daɗi, duk da kuwa akwai ƴar kunya a tsakaninsu. Dan daga ita har shi babu wanda ya iya saka idon juna. Da yake sun iske Addah a sashen itama suka gaisheta. Ta amsa musu da kulawa tanata tambayar ɗiyarta Nu'aymah.
      Suna ɗan hira da Addah ne, wadda ta kasance duk akan Nu'aymah Afrah da Muhammad da suka dawo daga islamiyya suka shig falon da sallama. Kallonta duk su Yoohan sukayi. Itama fuska ɗauke da nuna rashin sani a garesu, dan miskilace ta gaske, ga salon aiki. ta shiga gaidasu tana ƙoƙarin wucewa ɗakin Aymah daya zama nata yanzu batare ta nuna alama tama taɓa ganin mai kama dasu ba a rayuwa. Su dai da kallo kawai suka bita. Yayinda Yoohan ya miƙama Muhammad hannu alamar yazo garesa.
       Muhammad akwai wayo, dan haka tsaf ya gane Yoohan. Hannu ya bashi sukai musabaha. Yoohan ya shafa kansa yana murmushi, yace, “Oh my dear Friend ka ƙara girma fa”. Cike da jin daɗi Muhammad ya zauna kusa da shi yace, “Thanks Uncle. Ina Aunty N ɗina?” Yay maganar yana waige-waigen neman Nu'aymah.
           Murmushi Yoohan yayi yana ɗan rungumo Muhammad ɗin jikinsa. Yayinda Omar ke bashi amsa yana dariya. “Ta maka wayo tana U.S abinta”. Da ƴar damuwa Muhammad yace, “To Uncle yaushe zatazo itama?”.
       Yoohan yace, “Soon insha ALLAH Darling. Amma karka damu idan kunyi hutu zan kaika ka ganta”.
     Daɗi sosai ya kama Muhammad, nafa ya shiga tsallen murna su Addah na masa dariya.

      Sai bayan isha'i su Yoohan suka bar gidan da kayan Nu'aymah ghana must go guda. Baba malam baicema Yoohan komaiba game da wayar da sukayi da papa. ya da masa nasiha cikin hikima shi da Omar ɗin akan muhimmanci iyaye. Ta hakane Yoohan ya ɗan tsargi akwai abinda ya faru kenan. Amma sai shima baice komaiba.
        Ƙarfe goma na dare suka wuce Lagos. Inda zasu kwana uku yay aikin daya kawosa 9ja ɗin.

★★★

       Tunda suka shigo lagos Yoohan bai samu kansa ba. Aiki yake tuƙuru tamkar yanda ya saba hidima ga al'umma. Ya ɗanyi wasu ziyarce-ziyarce dake ransa. Batare daya sake bi takan su papa ba suka wuce U.S shi da Umar.

  *_U.S_*

        Kasancewar su Nu'aymah sunsan da dawowar mazajen nasu a ranar da safe Juliet ta maida Nu'aymah gidanta. Yaɗanyi ƙura kaɗan kuwa saboda rashin mutane. Dan haka Juliet ta taimaka mata suka gyara duk da Aymah na hanata. To itama dai ƙarfin haline dan a jigace take komai. Bayan sun kammala Juliet tai mata sallama ta koma nata gidan.
      Cike da ƙarfin hali Aymah taima Yoohan girki. Da ƙyar kuwa ta kammala tai wanka. Batare da tabi takan wani kwalliya ba tai shiri cikin Bomshort jeans bleu da pink top kawai tazo falo ta kwanta a ƙasan tiles kamar yanda takeyi a yanzun. Duk da kuwa da farko taci alwashin masa kwalliyar tarba amma hakan ya gagareta. Cike da rashin jin daɗin jiki kuwa barci yay awon gaba da ita a wajen. Ga zazzaɓi mai zafi daya fara saukar mata na yamma.
        A ƙagare Yoohan yake da son ganinta. Hakan yasa yaƙi yarda su hau cab ɗaya shi da Omar. Duk da kuwa kusan anguwa ɗaya suke. Sai ma an fara sauke Omar ɗin a gida kafin a ƙaraso nasu.
        Tsabar zumuɗi a barandar gidan yabar kayan da yazo dasu ya shige ciki. Sassanyan ƙamshin daya doki masa hancine ya sakashi lumshe idanu. Kafin ya buɗesu a hankali kan Aymah dake kwance a ƙasan tiles barcin wahala yay gaba da ita. Kallonta yake da matsanancin shauƙi da kewa. Ya taka a hankali zuwa inda take. Tsugunnawa yay a gabanta ya ɗaura tattausan hannunsa saman fuskarta dake shining na masu ciki ya shafa yana sauke ajiyar zuciya. Ko motsi batayiba kuwa. Sai ma numfashi da take saukewa a hankali. Zamewa yay ya zauna. ganin baya ganinta da ƙyau sai kawai ya kwanta shima ya ɗora kansa saman filon datake kwance yana kallonta da ƙyau. Sai dai kwanciyar tasu ta kasance tamkar kai da ƙafa bawai a jere ba. Hakan yasa goshinsa na saitin haɓarta ne. Itama nata goshin na saitin tasa haɓar. Yanda take busa masa numfashinne shima yana busa mata nasa ya sakashi sauke ajiyar zuciya idonsa ƙyam akan ɗan bakin tsiwarta. Matsar da kansa yayi a hankali ya daidaita bakinsu. Tare da ɗora hannunsa ya ringumo kanta jikinsa ya fara kissing nata cike da zalama da kewa.
       Cikin barci Nu'aymah taji salon da duk duniya na mutum ɗaya ne a gareta. Batare data buɗe idanuntaba cikin kasala itama takai hannu bisa kansa ta ringumosa tana mai bashi haɗin kai yanda tasan yana buƙata. Sunfi minti shida a haka sannan ya barta yana sauke numfashi da sauri-sauri. Dan harga ALLAH harya hau network.
      Shanyayun idanunta ta buɗe a hankali tana kallonsa. Dan har yanzu yana akan filon bai tashi ba. Murmushi yay mata mai sanyi, ya maida hannunsa akan fuskarta suna kallon juna cikin ido.
    “Welcome my boo”.
Tai maganar a hankali kamar mai tsoron ajisu.
     Lumshe idanunsa yayi ya sake buɗewa a kanta. Cikin ɗan sake matsar da kansa jikin fuskarta yace, “Sweet girl mike damunki?”.
     Maimakon ta bashi amsa sai hawaye shar. Saurin tashi yayi zaune har jikinsa na rawa..........✍

ZAFAFA BIYAR 2021

Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

          Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗

        Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗

        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗

         Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋

    Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.*_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.

No. 69

______________

INA MASOYA MA’ABOTA SON ‘KAAWATA KITCHENS DINSU DAMA DECORATION NA GIDAJEN SU? TOH KU MATSO, DOMIN NESA TAZO KUSA..._

_KAYA NE INGATTATU DA AKE KAWO MUKU SU TUN DAGA KASAR 🇩🇪 GERMANY..! KOWA YASAN GERMANY AKWAI KAYA MASU INGANCI, SEKA SHEKARA DA SHEKARU KANA AMFANI DA KAYAYYAKIN SU BASA LALACEWA. ANYI SU CIKIN TSANTSAR INGANCI DA KUMA RAHUSA... WADANNAN KAYA *MAAB LUXURY HOME* DAKE GERMANY TA KAWO MANA SU NIGERIA. RIGIJI GABJI FA KENAN.. BABU RUWAN KU DA WANI PRE-ORDER KO SHIPPING FEE, KAYAN *MAAB LUXURY HOME* SUNA NAN A KASAR MU NIGERIA, SAI DAI KAWAI KU HANZARTA KU GARZAYA KU BIYA KUDI KU KARBA..._

_MAAB LUXURY HOME, MAAB LUXURY HOME, MAAB LUXURY HOME..._

_SUNE A KAN SAHUN GABA INDE WAJEN SIYAN KAYAN KITCHEN NE DA NA KAWATA GIDA, WATO A TURANCE KITCHEN UTENSIL’s& HOME DECOR..._

_INA UWARGIDA? AMARYA? YAMMATA DAKE SHIRIN SHIGA DAGA CIKI? ZAWARA MASU SHIGA DAGA CIKI? IYAYE MASU NEMAN INDA ZASU SAYAWA ‘YAYAN SU KAYAN GIDA? YAYYE MAZA, MIJIN MATAR SA😉? SAURAYI DAKE SON BURGE BUDURWAR SA WAJEN GWANGWAJE KYAUTA? TOH *MAAB LUXURY HOME* TA TANADAR MUKU DUKKANIN ABUBUWAN AMFANI NA KITCHEN, DANA KAWATA GIDA, YAITA WALWALI YANA HASKAKAWA.._

_AKWAI KAYAN KITCHEN MAI KAWATA KITCHEN, WANDA ZAI SA KISHIYA KWAFA, YASA DANGIN MIJI SU FARA HABA HABA DAKE, DUK INDA AKA SHIGO CIKIN GIDAN KI ASAN EH TABBAS KEMA KINA AMFANI DA KAYAN *MAAB LUXURY HOME*, KAYAN KAWAATA GIDAJE MASU HASKA KO’INA NA GIDAN KI, KAGA GIDA A NIGERIA AMMA TAMKAR A NAHIYAR ‘KETARE.._
Chapter 173 · 0% Book details