Sashe 142
Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A daren wannan ranar su Hajjo suka iso. Hajjo, Abban Adawiya, Abban Abdallah, Abba Musbahu. Sai Addah data takura akan sai tazo taga jikin Aymah ɗin. Duk da kuwa ance baza'azo da matan gidan da yara ko ɗaya ba. Su yi haƙuri har Aymah ta dawo tunda ance jikin Alhmdllh. Amma Addah ta nace, da kantama ta biyama kanta ƙuɗin jirgi. Dan ita dai a ganinta bai kamata a yanda suke da Umm ba ace batazo ta duba NU'AYMAH ba. Shaƙuwar tasu hajjo ta kalla tace a barta taje tunda tace zata biyama kanta. dan bazai yuwu a biya mataba sauran matan suga anyi son kai.
Suma sunji daɗin ganin yanda jikin Aymahn yayi ƙyau sosai. Dan da taimakon Yoohan suka samu suka shiga wajenta. Alhmdllh kuma duk ta ganesu. Harma hajjo ta tsokaneta aka cuna mata baki. Dariya duk sukayi, Yoohan ya girgiza kai yana wani ɗan munafukin murmushi, a ransa yana faɗin, ‘Ta dawo duniya yanzu zata addabi kowa. Barema ni data gama rainawa’.
Kamarko Aymah tasan mi yake rayawa. Dan tana can tana masa kallon ƙasan ido ganin yanda ya rame mata a idanu. Sai dai batai tunanin komai a ranta ba ta maida hankalinta gasu hajjo.
Bayan wucewar su hajjo Richard ya kawo abincin da zataci lokacin shan maganinta yayi da barcinta. Dan a yau ne zata fara cin abu mai nauyi bayan kullum da ake bata iya mai ruwa-ruwa kawai dan ba'a son ta tauna abu saboda jijiyiyin kanta dake tare dana haƙori.
Cikin jin daɗi Yoohan ya amsa yana faɗin, “Thanks you Rich”. Ɗan hararsa Richard yayi da faɗin, “Dama akwai godiya ne tsakanina da kai Mr X”. Murmushi kawai Yoohan yayi amma baice komaiba. Shima Richard ɗin sai ya murmusa yana binsa da kallo. Sam baya iya dogon fushi da Yoohan. Ƙauna yake masa ta gaskiya kuma ta haƙiƙa har cikin ɓargonsa. Yanajinsa a jinin jikinsa tamkar ƴan uwansa da suka fito ciki ɗaya. Kuma shi harga ALLAH bai taɓa jin zafinsa akan auran Nu'aymah da yayiba duk da kuwa ta kasance Bahaushiya kuma musulma. Sai dai salla da Yoohan ya farayi yanzu yana matuƙar damun ransa. ya rasa wane kalar tunani zaiyi akan wannan matsalar, wazai tunkara su tattauna domin haɗa hannu wajen dawo da Yoohan cikin hankalinsa?. Da yayi yunƙurin sanarma wani sai yaji rauni da fargaba ta kamashi. dan haka ya barma ransa ko sauran abokansu su Joseph ya kasa faɗamawa....
Yoohan dai tuni ya fice a office ɗin abunsa ya bar Rich da faɗawa dogon tunani. A waje yaga Solomon tsaye. Ya ɗan kafesa da kallon mamaki dan ganin yanda Solomon ɗin yay fakare kamar wanda ya tsorata da ganinsa. Bai dai ce da shi komaiba yay wucewarsa.
Nannauyan numfashi Solo ya sauke yana rumtse idanunsa da wayarsa dake cikin hannu. Yau shikam ya shiga uku, yana fatan Yoohan baiji wayarnan da yakeyi da papa ba. Gaba ɗaya sai wani tsoro na tashin hankali ya kuma baibayesa. Barin asibitin yayi jikinsa na tsuma. dama zuwansa kenan shi da Richard.
Yoohan da haka kawai yanayin Solomon yaso ɗarsa masa zargi a zuciya ya ƙarasa ɗakin da Aymah take yana wasiwasi. Kwance take akan gadon jiyyarta idanunta a lumshe. Har yanzu bawai jikin nata yayi ƙarfi baneba. Dan ko magana ma da ƙa'ida takeyinta. Kai duk ma sauran abubuwa komai zatayi da ƙa'idarsa saboda ƙwalwarta ana buƙatar ta samu isashen hutun da komai zai gama dai-daita. Dan yanzu dai su Yoohan sun tabbatar da komai Alhmdllh, sai dai zata ringa yawaita ciwon kai kafin wani tsahon lokaci da suma basusan adadiba. Sannan idanunta sun raunana zatake amfani da glass shima kafin zuwa wani lokaci. Bawai bata gani bane, tana ganin komai Alhmdllh, sai dai ba a yanda ya kamataba. Dan idan abu yayi mata nisa tana ganinsa bibbiyu ko dishi-dishi. Sannan sun tabbatar da zata rage yawan hayaniya yanzun.
Ƙamshinsa da taji ya yawaita a ɗakinne ya sakata buɗe idanunta a hankali. A kansa ta zubasu, sai dai batai masa kallon sakan uku ba ta janye. Ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke. ya matsa gaban gadon sosai ya zauna, kama hannunta yay cikin nashi. Cikin magana ƙasa-ƙasa da ko kana a ɗakin bajinsu zakai ba yace,
“How are you feeling?”.
Hannunta da ke a cikin nasa taɗan motsa, idanunta a lumshe, cikin magana a hankali fiyema da tasa tace, “Alhamdulillah”.
“Masha ALLAH”. ya faɗa da harshensa karyayye.
Batare da yace mata komaiba ya kamata zai tayar. Buɗe idanun tayi sosai. A rashin sanin ita yake kallo suka faɗa a cikin nashi. Saurin kauda kanta tayi tana motsa baki kaɗan. Duk da ba magana taiba yasan tsiwarce ta motso, sai dai yanzu kam babu bakin yi yanda ya kamata. Filo ya saka mata ta jingina yanda zataji daɗi. Ya zauna a kusa da ƙafafunta dake a miƙe. Gaba ɗaya jitai ta gama takurewa a wajen. Ga ƙamshinsa yayi bala'in adabawa numfashinta. Shi dai da baisan tanayi ba, ya san dai tunda ta kasance jinin masoyinsa baba malam bazai taɓa gajiyawa wajen jinyarta ba tamkar yanda yasan iyayenta zasu kula da ita. takeaway ɗin ya buɗe yana fuskantarta. Duk da ya fahimci kallonsa takeyi sai bai nuna ya ganiba. Batare da ya kalleta ba yace, “Yau zaki fara cin abinci mai nauyi. Insha ALLAH yanda jikinki keyin ƙyau zamu samu sallama da wuri. Amma sai kin daure kin ringa cin abinci ko yaya ne. Dan yanzu zakiji ɗanɗanon sa sam baya miki wani daɗi. Sai a hankali ne ɗanɗanon harshenki zai warware”.
Fuska kawai taɗan yamutsa. Dan harga ALLAH kam abincin ma ganinsa kawai da takeyi yanzu amai yake neman sakata, sai dai kuma itama tana buƙatar ganin an sallameta ta bar asibitin nan da duk take jinta a takure.
Bai damu da rashin yin maganar tata ba. Ya ɗiba abincin a spoon ya nufi bakinta da shi. Har zata kauda kanta yay saurin faɗin, “No, Please!”. Daurewa tai ta buɗe bakin idanunta a rumtse. Ya zuba mata tausayinta na ƙara ratsasa. taja kusan minti biyu tana juya abincin a baki sannan ta haɗiyeshi da ƙyar. Sake ɗiba yayi ya bata. Nanma dai sai da ta ɓata lokaci. Da ƙyar ya samu taɗanci, sai dai sunja lokaci mai tsaho ana ƙaƙa nakayi, dan harda hawayenta shaɓe-shaɓe a fuska. Da ga ƙarshe dai ganin ta ɗanci ya haƙura ya barta. Tissue yasa ya goge mata bakinta da hawayen datayi. Yana ƙoƙarin tashi ta riƙo hannunsa. Kallonta yay kawai sai dai baice komaiba.
A mamakinsa sai yaga ta ɗauki cokalin daya bata abincin ta ɗibo ta nufo bakinsa. ba ƙaramin harbawa zuciyar Yoohan yayiba. Duk da ba abincine daya cika damuwa da shi ba haka ya buɗe bakin kawai yana kallonta. Zuba masa tayi kuwa batare da ta yarda sun haɗa ido ba. Ta ƙara ɗebowa tana magana a hankali. “Ka rame da yawa. da alama kaima baka da lafiyar kuma bakacin abinci. Amma gashi ni kazo ka tsareni sai da naci. To kaima tsareka zanyi sai kaci”.
Yanda tai maganarne a sakalce ya sakashi yin murmushi. ya fahinci kuma da iya gaskiyarta take faɗin abinda ke a ranta. Hannu ya kai saman fuskarta a hankali yana faɗin, “Thanks you”. Kallo ɗaya tai masa ta janye idanunta batare datace komaiba. Sai dai taji daɗin thanks you ɗin daya ce mata. Hannu tasa akan hannunsa dake saman fuskarsa ta janye, dan yanda yake mata a kumatu jitake tsigar jikinta na tashi. Murmushi ya kumayi yana cigaba da amsar abincin. itako taƙi yarda su haɗa idanu sam, sai danna masa abinci takeyi.
A wannan yanayin Dr LiLiya shigo ya samesu. Da tsokana yake cewa, “Irin wannan soyayya haka bazasu bari a warke ba?”.
Sosai Aymah ta waro idanu akan baturen likitan. Sai dai kuma batai magana ba. Ta ɗan harari Yoohan dake murmushi. Sai kuma ta ajiye spoon ɗin ta kwanta abunta da juya musu baya. Ƙaramar dariya Yoohan yayi har haƙoransa na bayyana sosai. Ƙasa-ƙasa ya cema Dr Liam “Kaga ka jamin an bar bani”.
Dr Liam dariyar shima yayi yana haɗe hannaye waje guda alamar Sorry.
Ita dai Aymah bata sake kulasuba. Da za'a bata magani ma ƙin yarda tayi ta kalli kowa a cikinsu. Tana sha kuwa ko mintuna goma cikakku batayi ba barci mai nauyi yay awon gaba da ita. Sassanyar ajiyar zuciya Yoohan ya sauke. Ya kama hannunta data bashi abinci ya sumbata yana wani lumshe idanu. Daga haka suka fito suka bar mata ɗakin shi da Dr Liam
____________★★
Yau kwanakin su Hajjo biyu da zuwa. gobe idan ALLAH ya kaimu kuma zasu koma harda su baba malam ma. Sunzo sun duba Aymah da jikinta keta ƙara warwarewa Alhmdllh. Sai dai batason cin abinci sai Yoohan yata lallashi da dabara. A hakanma bata yarda taci ita kaɗai. sai dai idan ya ɗeba spoon ɗaya ya bata itama sai ta ɗiba ta bashi. Ita a ganinta wayo takeyi dansu cinye tare ya rage mata aiki. shiko hakan ba ƙaramin shauƙi yake sakashi a ciki ba, da jinsa on top. Ta kai ko ruwan addu'arta ya bata tasha itama shima sai ta rage ta bashi ya sha. Dan harga ALLAH ramar da taga yayi kuma na damunta a cikin rai. Ta tabbatar koda rashin lafiya yayi to harda damuwar halin da take a ciki. Dan ta fahimci shi mutum ne mai tausayi sosai dama.
Suma sunji daɗin ganin yanda jikin Aymahn yayi ƙyau sosai. Dan da taimakon Yoohan suka samu suka shiga wajenta. Alhmdllh kuma duk ta ganesu. Harma hajjo ta tsokaneta aka cuna mata baki. Dariya duk sukayi, Yoohan ya girgiza kai yana wani ɗan munafukin murmushi, a ransa yana faɗin, ‘Ta dawo duniya yanzu zata addabi kowa. Barema ni data gama rainawa’.
Kamarko Aymah tasan mi yake rayawa. Dan tana can tana masa kallon ƙasan ido ganin yanda ya rame mata a idanu. Sai dai batai tunanin komai a ranta ba ta maida hankalinta gasu hajjo.
Bayan wucewar su hajjo Richard ya kawo abincin da zataci lokacin shan maganinta yayi da barcinta. Dan a yau ne zata fara cin abu mai nauyi bayan kullum da ake bata iya mai ruwa-ruwa kawai dan ba'a son ta tauna abu saboda jijiyiyin kanta dake tare dana haƙori.
Cikin jin daɗi Yoohan ya amsa yana faɗin, “Thanks you Rich”. Ɗan hararsa Richard yayi da faɗin, “Dama akwai godiya ne tsakanina da kai Mr X”. Murmushi kawai Yoohan yayi amma baice komaiba. Shima Richard ɗin sai ya murmusa yana binsa da kallo. Sam baya iya dogon fushi da Yoohan. Ƙauna yake masa ta gaskiya kuma ta haƙiƙa har cikin ɓargonsa. Yanajinsa a jinin jikinsa tamkar ƴan uwansa da suka fito ciki ɗaya. Kuma shi harga ALLAH bai taɓa jin zafinsa akan auran Nu'aymah da yayiba duk da kuwa ta kasance Bahaushiya kuma musulma. Sai dai salla da Yoohan ya farayi yanzu yana matuƙar damun ransa. ya rasa wane kalar tunani zaiyi akan wannan matsalar, wazai tunkara su tattauna domin haɗa hannu wajen dawo da Yoohan cikin hankalinsa?. Da yayi yunƙurin sanarma wani sai yaji rauni da fargaba ta kamashi. dan haka ya barma ransa ko sauran abokansu su Joseph ya kasa faɗamawa....
Yoohan dai tuni ya fice a office ɗin abunsa ya bar Rich da faɗawa dogon tunani. A waje yaga Solomon tsaye. Ya ɗan kafesa da kallon mamaki dan ganin yanda Solomon ɗin yay fakare kamar wanda ya tsorata da ganinsa. Bai dai ce da shi komaiba yay wucewarsa.
Nannauyan numfashi Solo ya sauke yana rumtse idanunsa da wayarsa dake cikin hannu. Yau shikam ya shiga uku, yana fatan Yoohan baiji wayarnan da yakeyi da papa ba. Gaba ɗaya sai wani tsoro na tashin hankali ya kuma baibayesa. Barin asibitin yayi jikinsa na tsuma. dama zuwansa kenan shi da Richard.
Yoohan da haka kawai yanayin Solomon yaso ɗarsa masa zargi a zuciya ya ƙarasa ɗakin da Aymah take yana wasiwasi. Kwance take akan gadon jiyyarta idanunta a lumshe. Har yanzu bawai jikin nata yayi ƙarfi baneba. Dan ko magana ma da ƙa'ida takeyinta. Kai duk ma sauran abubuwa komai zatayi da ƙa'idarsa saboda ƙwalwarta ana buƙatar ta samu isashen hutun da komai zai gama dai-daita. Dan yanzu dai su Yoohan sun tabbatar da komai Alhmdllh, sai dai zata ringa yawaita ciwon kai kafin wani tsahon lokaci da suma basusan adadiba. Sannan idanunta sun raunana zatake amfani da glass shima kafin zuwa wani lokaci. Bawai bata gani bane, tana ganin komai Alhmdllh, sai dai ba a yanda ya kamataba. Dan idan abu yayi mata nisa tana ganinsa bibbiyu ko dishi-dishi. Sannan sun tabbatar da zata rage yawan hayaniya yanzun.
Ƙamshinsa da taji ya yawaita a ɗakinne ya sakata buɗe idanunta a hankali. A kansa ta zubasu, sai dai batai masa kallon sakan uku ba ta janye. Ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke. ya matsa gaban gadon sosai ya zauna, kama hannunta yay cikin nashi. Cikin magana ƙasa-ƙasa da ko kana a ɗakin bajinsu zakai ba yace,
“How are you feeling?”.
Hannunta da ke a cikin nasa taɗan motsa, idanunta a lumshe, cikin magana a hankali fiyema da tasa tace, “Alhamdulillah”.
“Masha ALLAH”. ya faɗa da harshensa karyayye.
Batare da yace mata komaiba ya kamata zai tayar. Buɗe idanun tayi sosai. A rashin sanin ita yake kallo suka faɗa a cikin nashi. Saurin kauda kanta tayi tana motsa baki kaɗan. Duk da ba magana taiba yasan tsiwarce ta motso, sai dai yanzu kam babu bakin yi yanda ya kamata. Filo ya saka mata ta jingina yanda zataji daɗi. Ya zauna a kusa da ƙafafunta dake a miƙe. Gaba ɗaya jitai ta gama takurewa a wajen. Ga ƙamshinsa yayi bala'in adabawa numfashinta. Shi dai da baisan tanayi ba, ya san dai tunda ta kasance jinin masoyinsa baba malam bazai taɓa gajiyawa wajen jinyarta ba tamkar yanda yasan iyayenta zasu kula da ita. takeaway ɗin ya buɗe yana fuskantarta. Duk da ya fahimci kallonsa takeyi sai bai nuna ya ganiba. Batare da ya kalleta ba yace, “Yau zaki fara cin abinci mai nauyi. Insha ALLAH yanda jikinki keyin ƙyau zamu samu sallama da wuri. Amma sai kin daure kin ringa cin abinci ko yaya ne. Dan yanzu zakiji ɗanɗanon sa sam baya miki wani daɗi. Sai a hankali ne ɗanɗanon harshenki zai warware”.
Fuska kawai taɗan yamutsa. Dan harga ALLAH kam abincin ma ganinsa kawai da takeyi yanzu amai yake neman sakata, sai dai kuma itama tana buƙatar ganin an sallameta ta bar asibitin nan da duk take jinta a takure.
Bai damu da rashin yin maganar tata ba. Ya ɗiba abincin a spoon ya nufi bakinta da shi. Har zata kauda kanta yay saurin faɗin, “No, Please!”. Daurewa tai ta buɗe bakin idanunta a rumtse. Ya zuba mata tausayinta na ƙara ratsasa. taja kusan minti biyu tana juya abincin a baki sannan ta haɗiyeshi da ƙyar. Sake ɗiba yayi ya bata. Nanma dai sai da ta ɓata lokaci. Da ƙyar ya samu taɗanci, sai dai sunja lokaci mai tsaho ana ƙaƙa nakayi, dan harda hawayenta shaɓe-shaɓe a fuska. Da ga ƙarshe dai ganin ta ɗanci ya haƙura ya barta. Tissue yasa ya goge mata bakinta da hawayen datayi. Yana ƙoƙarin tashi ta riƙo hannunsa. Kallonta yay kawai sai dai baice komaiba.
A mamakinsa sai yaga ta ɗauki cokalin daya bata abincin ta ɗibo ta nufo bakinsa. ba ƙaramin harbawa zuciyar Yoohan yayiba. Duk da ba abincine daya cika damuwa da shi ba haka ya buɗe bakin kawai yana kallonta. Zuba masa tayi kuwa batare da ta yarda sun haɗa ido ba. Ta ƙara ɗebowa tana magana a hankali. “Ka rame da yawa. da alama kaima baka da lafiyar kuma bakacin abinci. Amma gashi ni kazo ka tsareni sai da naci. To kaima tsareka zanyi sai kaci”.
Yanda tai maganarne a sakalce ya sakashi yin murmushi. ya fahinci kuma da iya gaskiyarta take faɗin abinda ke a ranta. Hannu ya kai saman fuskarta a hankali yana faɗin, “Thanks you”. Kallo ɗaya tai masa ta janye idanunta batare datace komaiba. Sai dai taji daɗin thanks you ɗin daya ce mata. Hannu tasa akan hannunsa dake saman fuskarsa ta janye, dan yanda yake mata a kumatu jitake tsigar jikinta na tashi. Murmushi ya kumayi yana cigaba da amsar abincin. itako taƙi yarda su haɗa idanu sam, sai danna masa abinci takeyi.
A wannan yanayin Dr LiLiya shigo ya samesu. Da tsokana yake cewa, “Irin wannan soyayya haka bazasu bari a warke ba?”.
Sosai Aymah ta waro idanu akan baturen likitan. Sai dai kuma batai magana ba. Ta ɗan harari Yoohan dake murmushi. Sai kuma ta ajiye spoon ɗin ta kwanta abunta da juya musu baya. Ƙaramar dariya Yoohan yayi har haƙoransa na bayyana sosai. Ƙasa-ƙasa ya cema Dr Liam “Kaga ka jamin an bar bani”.
Dr Liam dariyar shima yayi yana haɗe hannaye waje guda alamar Sorry.
Ita dai Aymah bata sake kulasuba. Da za'a bata magani ma ƙin yarda tayi ta kalli kowa a cikinsu. Tana sha kuwa ko mintuna goma cikakku batayi ba barci mai nauyi yay awon gaba da ita. Sassanyar ajiyar zuciya Yoohan ya sauke. Ya kama hannunta data bashi abinci ya sumbata yana wani lumshe idanu. Daga haka suka fito suka bar mata ɗakin shi da Dr Liam
____________★★
Yau kwanakin su Hajjo biyu da zuwa. gobe idan ALLAH ya kaimu kuma zasu koma harda su baba malam ma. Sunzo sun duba Aymah da jikinta keta ƙara warwarewa Alhmdllh. Sai dai batason cin abinci sai Yoohan yata lallashi da dabara. A hakanma bata yarda taci ita kaɗai. sai dai idan ya ɗeba spoon ɗaya ya bata itama sai ta ɗiba ta bashi. Ita a ganinta wayo takeyi dansu cinye tare ya rage mata aiki. shiko hakan ba ƙaramin shauƙi yake sakashi a ciki ba, da jinsa on top. Ta kai ko ruwan addu'arta ya bata tasha itama shima sai ta rage ta bashi ya sha. Dan harga ALLAH ramar da taga yayi kuma na damunta a cikin rai. Ta tabbatar koda rashin lafiya yayi to harda damuwar halin da take a ciki. Dan ta fahimci shi mutum ne mai tausayi sosai dama.