Sashe 9
Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Addah ta samu ciki da zuwanta gidan, amma Umm shiru kakeji. Sunyi murna sosai da cikin Addah, har ALLAH ya sauketa lafiya ta haifo ɗanta Namiji santalele. Wanda yaci suna Hashim, amma suna kiransa da malam ƙarami. Babu jimawa matar Musbahu ta haifo nata cikin itama Namiji, yaci suna Ahmad. Itama tsakaninsu babu nisa da Momyn Abdallah datai haihuwa ta biyar, itama ta haifo mace aka sake maida mata Aysha.
Sosai su Baba malam sukai farin ciki family ɗinsu ya dawo kamar da. Inda sukema Umm Addu'ar itama ALLAH ta kawo mai albarka. Haka haihuwar matan gidan ta cigaba da tafiya a jajjere. Sai da sukai haihuwa hurhuɗu kafin ALLAH ya bama Umm ciki itama. Kowa ya tayata farin ciki sosai, musamman ma Addah da ayanzu takeda yara huɗu, Ɗaya namiji Uku mata. Sai Momyn Abdallah nada huɗu, maza biyu mata biyu. Matar Abba Musbahu nada huɗu itama duk maza.
Umm ta haihu Namiji sannan su Addah duk suna fama da laulayi ƙananun ciki, sai dai kuma kwanan jaririn Uku ya koma. Sosai Umm tasha kuka, amma daga ƙarshe saita share hawayenta dan tasan ALLAHn daya bata ya karɓa ya fita sonsa. sannan ma yaran gidan babu wanda kemata shamaki da nasa, faɗi tashinsu sukeyi a sashenta kamar nata, musamman ma Abdallah da ƴaƴan Addah da inba faɗa maka akaiba bazaka taɓa sanin ba nata baneba.
Cikin amincin ALLAH bata rufa wata uku da haihuwa ba saiga wani cikin, inda shima Baba malam yay murna matuƙa fiye ma dana farko. Su Addah sun rigata haihuwa. Matar Abbah Musbahu ce ta fara haihuwar ƴarta mace da taci suna Yusrah, sai Addah ta haihu itama mace, aka saka mata Adawiya, sai Momyn Abdallah ta haihu itama dai mace, aka saka Safiyya sunan mahaifiyarta, sai dai ana mata alkunya da Amal. Bayan haihuwarsu da watanni itama Umm ta sake haifo ƴarta mace mai kama da ita. Wadda taci suna Zainab, da yake sunan hajjo ne sai ake mata alkunya da Nu'aymah.
Bayan haihuwar Nu'aymah da kusan shekara biyar Umm ta sake haihuwar yaro ɗaya namiji Muhammad, daga nan kuma shiru kakeji bata sake ko ɓatan wata ba. A lokacin Addah ta sake haihuwa uku, mata biyu da namiji ɗaya. Sai yazam tana da yara bakwai. Mata shidda maza biyu. Itama Momyn Abdallah ta ƙara biyu ƴammata tagwaye, tanada mata huɗu maza uku itama. matar Abbah Musbahu ko ɗaya ta ƙara shima namiji, tanada maza biyar mace ɗaya kenan. Daga haka haihuwar ta tsaya musu su duka babu wanda ya ƙarayi.
Rayuwar gidan tacigaba da gudana cike da birgewa da ban sha'awa, inda ALLAH keta ƙara ɗaga darajar mazajensu ta ɓangaren yaɗa da'awa da ilmantar da bayin ALLAH da taimakonsu ta hanyoyi da dama. Suma kuma ba'a barsu a bayaba wajen yima addini hidima. Ƴaƴansu sun tashi kansu a haɗe cike da tarbiyya kula. Komai tare ake musu.
Akwai shaƙuwa sosai tsakanin Abdallah da Nu'aymah, dan tunda aka haifeta ya kasa ya tsare. Komai yaci sai ya ragema Nu'aymah duk da alokacin yayi girma sosai, dan harma ya kammala firamare yana shirin shiga sakandire. Babu mai dukan Nu'aymah ya kwana lafiya a gidan. Umm ce kawai yake ma ɗan kawaici, itama zaita fushi da itane koda bazaiyi maganaba. Komai ma Abdallah na Nu'aymah ne, firarsa Nu'aymah, fushinsa sai an taɓa Nu'aymah, kukansa sai Nu'aymah na kuka.
Itama kamar tasan abinda yake yi, tanama kowa ƙiwa a gidan amma banda Yah Ab, duk abinda ta samu saita rage ta ajiye masa. Tun kowa na ɗaukar lamarin nasu wasa har aka fahimci yafi ƙarfin wasan aka koma binsu da addu'a.
Nu'aymah nada shekaru tara a duniya su Baba malam suka buɗe kamfanin mangyaɗa a garin Lagos, hakan yasa dole Malam Rudwan Hashim Jibiya (Abban Abdallah) ya koma can da iyalansa dan ya dinga kula da shi. Lokacin komawar tasu kam anga tashin hankali wajen Abdallah saboda rabuwa da Nu'aymah. Da ƙyar aka yakicesa daga jikinta, danfa shi yace inhar zaije sai dai da ita, kokuma a barsa anan wajensu. Ganin yanda yay matuƙar ɗaga hankalinsa yasa Hajjo sakawa a barsa nan gida badan Momynsa tasoba. Idan anyi hutu ya ringa zuwa musu, idan kuma sunzo shikenan.
Haka yana gani iyayensa suka lula Lagos aka barsa a kano saboda Nu'aymah. Bayan tafiyarsu Abban Abdallah da shekar biyu shima Abba Musbahu daya ƙara auren mata ta biyu ya bisa tare da Ammin Ahmad, yabar amaryarsa anan gidan yana zuwa weekend, dan aiki yayma Abban Abdallah yawa acan shi kaɗai, ga harkar Addini gata kasuwanci, ga nashi kuma yanayi shima.
Gida sai ya koma daga hajjo sai Umm da Addah da Ummah amaryar Abba Musbahu. Iyalan Baba Malam dana Abba Mustapha kenan. Sai idan sun sami hutune matan kanzo da yaran nan suyi, sukuma su Abbah sai suke zuwa weekend idan matan nasu sunzo nan.
Haka rayuwar ta cigaba da tafiya, shaƙuwa na sake ƙulluwa tsakanin Nu'aymah da Abdallah, hakama tsakanin Adawiya da Nu'aymah, dan sun taso sa'anni su biyu tunda su Yusrah suna Lagos.
Komansu tare ake musu, babu maijin kansu, Hassana da Hussaina ma ake kiransu saboda shaƙuwa. A hankali Adawiya ta kwaso kayanta ta dawo ɗakin Nu'aymah dake sashensu, suka zama a ɗaki guda, makaranarsu ɗaya, ajinsu ɗaya. Kai komaima nasu ɗayane. Gefe ga soyayyar Nu'aymah da Abdallah, inda itama Adawiya son Abdallah keta mata saƙa a zuciya batare da kowa ya saniba har ita kanta. Bata tashi farga dason da take masaba sai da yay mata babbar illa a jini da zuciya, har takai bazata iya haƙura ta barma Nu'aymah ba.
Tunda Abdallah ya kai minzalin aure bayan kammala karatunsa na degree aketa fama da shi yayi aure amma yaƙi, acewarsa Nu'aymah yake so. An lallaɓashi akan ya auri wata idan Nu'aymah ta isa saiya ƙara da ita, amma sam yace bazata saɓuba, zai jirata ko shekara nawane. Abin ya bama kowa mamaki, dan lokacinma fa Nu'aymah da Adawiya suna firamare aji shidda ne. Haka kowa ya haƙura aka zuba masa ido, sai ma ya koma karatu da kasuwancinsa na kansa daya ƙirƙira, ya duƙufa wajen faɗaɗa karatunsa na addini kuma tamkar iyayensa.
A wannan shekarar Abban Abdallah ya sake komawa Abuja da zama inda canma suka buɗe reshen Company ɗinsu na mangyaɗa, sai aka bar Abba Musbahu a Lagos. Tunda suka dawo Abuja Momyn Abdallah ta fara jan yaronta jikinta sosai, a hankali ta janye ra'ayinsa ya koma Abuja da zama wajensu, inda harkokin kasuwancinsa suka fara faɗaɗa daga Nigeria zuwa ƙasar Saudia. Lokacin kuma Adawiya da Nu'aymah sun shiga sakandire.
Suna aji uku a secondary Abdallah ya koma kara faɗaɗa iliminsa na addini a ƙasar Saudia inda yake kasuwancinsa yanzu, sai yazam baya zuwa sai dai aiko da kaya Nigeria Omar da Ahmad na kulawa dasu suma suna aika masa na Nigeria can.
Nu'aymah yarinyace ƙyaƙyƙyawa fara masha ALLAH, dan tana kama da mahaifiyarta sosai, yarinyace mai shegen wayo ga rashin tsoro ga tsiwa. Tsula tsiyarsu suke ita da Adawiya fiye da zato, kullum cikin jan faɗa suke a makaranta daga boko har islamiyya. Duk da rashin jinsu yarane masu kaifin basira da hazaƙa musamman ma Nu'aymah, tana da matuƙar ƙoƙari, dan tun tana aji biyu na secondary tayi saukar Qur'ani, bayan tayi da shekara ɗaya itama Adawiya tayi. Bayan duk sunyi sauka suka juya hadda, tare da karatun sauran littatafai kuma.
Hazaƙar Nu'aymah a makaranta yasa suna aji biyar wani malami ya bada shawarar a barta kawai ta zana ssce a wannan shekarar, koba komai zata kammala jami'a da ƙarancin shekaru. Baba malam ya amshi wannan shawarar, musamman daya duba maganar auren Nu'aymah da Abdallah da kowa ke jira, ya yanke shawarar tana zana ssce za'ayi auren sai taje ta cigaba da karatunta a ɗakin mijinta kawai. amma saiya sa suyi ssce ɗin tare da Adawiya. Wannan shine ya sakasu gama makaranta a wannan shekarar. Adawiya dasu Amal nada shekaru sha bakwai cif, Nu'aymah kuwa bata cikaba har yanzu, tana sha shida da wasu watanni dan su Adawiya sun girmeta...............✍
ZAFAFA BIYAR 2021
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
*_Typing📲_*
*_SARAN ƁOYE!!_*
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
Free page😋
_Daga yau free pages sun ƙare masoya. Ku garzayo domin samun waɗanan littatafai guda biyar akan farashi mai sauƙi. Dan girman ALLAH kibi ta hanyar data dace ki mallaki naki😅, karki zama cikin masoya masu mana SARAN ƁOYE akan kasuwancinmu😢🙏, muna alfahari daku aduk inda kuke. Muna godiya kuma da ƙaunar da kuke nuna mana irin trillions ɗin nan. Idan nace ku na dabanne ina nufin na daban har cikin raina😘😘🤝🏻_.
*_Masu buƙatar mu saka musu tallar kayan sana'arsu zasu iya zuwa suyi magana damu domin tayasu tallata hajojinsu a yanar gizo😘🤝🏻_*.
No. 5
Sosai su Baba malam sukai farin ciki family ɗinsu ya dawo kamar da. Inda sukema Umm Addu'ar itama ALLAH ta kawo mai albarka. Haka haihuwar matan gidan ta cigaba da tafiya a jajjere. Sai da sukai haihuwa hurhuɗu kafin ALLAH ya bama Umm ciki itama. Kowa ya tayata farin ciki sosai, musamman ma Addah da ayanzu takeda yara huɗu, Ɗaya namiji Uku mata. Sai Momyn Abdallah nada huɗu, maza biyu mata biyu. Matar Abba Musbahu nada huɗu itama duk maza.
Umm ta haihu Namiji sannan su Addah duk suna fama da laulayi ƙananun ciki, sai dai kuma kwanan jaririn Uku ya koma. Sosai Umm tasha kuka, amma daga ƙarshe saita share hawayenta dan tasan ALLAHn daya bata ya karɓa ya fita sonsa. sannan ma yaran gidan babu wanda kemata shamaki da nasa, faɗi tashinsu sukeyi a sashenta kamar nata, musamman ma Abdallah da ƴaƴan Addah da inba faɗa maka akaiba bazaka taɓa sanin ba nata baneba.
Cikin amincin ALLAH bata rufa wata uku da haihuwa ba saiga wani cikin, inda shima Baba malam yay murna matuƙa fiye ma dana farko. Su Addah sun rigata haihuwa. Matar Abbah Musbahu ce ta fara haihuwar ƴarta mace da taci suna Yusrah, sai Addah ta haihu itama mace, aka saka mata Adawiya, sai Momyn Abdallah ta haihu itama dai mace, aka saka Safiyya sunan mahaifiyarta, sai dai ana mata alkunya da Amal. Bayan haihuwarsu da watanni itama Umm ta sake haifo ƴarta mace mai kama da ita. Wadda taci suna Zainab, da yake sunan hajjo ne sai ake mata alkunya da Nu'aymah.
Bayan haihuwar Nu'aymah da kusan shekara biyar Umm ta sake haihuwar yaro ɗaya namiji Muhammad, daga nan kuma shiru kakeji bata sake ko ɓatan wata ba. A lokacin Addah ta sake haihuwa uku, mata biyu da namiji ɗaya. Sai yazam tana da yara bakwai. Mata shidda maza biyu. Itama Momyn Abdallah ta ƙara biyu ƴammata tagwaye, tanada mata huɗu maza uku itama. matar Abbah Musbahu ko ɗaya ta ƙara shima namiji, tanada maza biyar mace ɗaya kenan. Daga haka haihuwar ta tsaya musu su duka babu wanda ya ƙarayi.
Rayuwar gidan tacigaba da gudana cike da birgewa da ban sha'awa, inda ALLAH keta ƙara ɗaga darajar mazajensu ta ɓangaren yaɗa da'awa da ilmantar da bayin ALLAH da taimakonsu ta hanyoyi da dama. Suma kuma ba'a barsu a bayaba wajen yima addini hidima. Ƴaƴansu sun tashi kansu a haɗe cike da tarbiyya kula. Komai tare ake musu.
Akwai shaƙuwa sosai tsakanin Abdallah da Nu'aymah, dan tunda aka haifeta ya kasa ya tsare. Komai yaci sai ya ragema Nu'aymah duk da alokacin yayi girma sosai, dan harma ya kammala firamare yana shirin shiga sakandire. Babu mai dukan Nu'aymah ya kwana lafiya a gidan. Umm ce kawai yake ma ɗan kawaici, itama zaita fushi da itane koda bazaiyi maganaba. Komai ma Abdallah na Nu'aymah ne, firarsa Nu'aymah, fushinsa sai an taɓa Nu'aymah, kukansa sai Nu'aymah na kuka.
Itama kamar tasan abinda yake yi, tanama kowa ƙiwa a gidan amma banda Yah Ab, duk abinda ta samu saita rage ta ajiye masa. Tun kowa na ɗaukar lamarin nasu wasa har aka fahimci yafi ƙarfin wasan aka koma binsu da addu'a.
Nu'aymah nada shekaru tara a duniya su Baba malam suka buɗe kamfanin mangyaɗa a garin Lagos, hakan yasa dole Malam Rudwan Hashim Jibiya (Abban Abdallah) ya koma can da iyalansa dan ya dinga kula da shi. Lokacin komawar tasu kam anga tashin hankali wajen Abdallah saboda rabuwa da Nu'aymah. Da ƙyar aka yakicesa daga jikinta, danfa shi yace inhar zaije sai dai da ita, kokuma a barsa anan wajensu. Ganin yanda yay matuƙar ɗaga hankalinsa yasa Hajjo sakawa a barsa nan gida badan Momynsa tasoba. Idan anyi hutu ya ringa zuwa musu, idan kuma sunzo shikenan.
Haka yana gani iyayensa suka lula Lagos aka barsa a kano saboda Nu'aymah. Bayan tafiyarsu Abban Abdallah da shekar biyu shima Abba Musbahu daya ƙara auren mata ta biyu ya bisa tare da Ammin Ahmad, yabar amaryarsa anan gidan yana zuwa weekend, dan aiki yayma Abban Abdallah yawa acan shi kaɗai, ga harkar Addini gata kasuwanci, ga nashi kuma yanayi shima.
Gida sai ya koma daga hajjo sai Umm da Addah da Ummah amaryar Abba Musbahu. Iyalan Baba Malam dana Abba Mustapha kenan. Sai idan sun sami hutune matan kanzo da yaran nan suyi, sukuma su Abbah sai suke zuwa weekend idan matan nasu sunzo nan.
Haka rayuwar ta cigaba da tafiya, shaƙuwa na sake ƙulluwa tsakanin Nu'aymah da Abdallah, hakama tsakanin Adawiya da Nu'aymah, dan sun taso sa'anni su biyu tunda su Yusrah suna Lagos.
Komansu tare ake musu, babu maijin kansu, Hassana da Hussaina ma ake kiransu saboda shaƙuwa. A hankali Adawiya ta kwaso kayanta ta dawo ɗakin Nu'aymah dake sashensu, suka zama a ɗaki guda, makaranarsu ɗaya, ajinsu ɗaya. Kai komaima nasu ɗayane. Gefe ga soyayyar Nu'aymah da Abdallah, inda itama Adawiya son Abdallah keta mata saƙa a zuciya batare da kowa ya saniba har ita kanta. Bata tashi farga dason da take masaba sai da yay mata babbar illa a jini da zuciya, har takai bazata iya haƙura ta barma Nu'aymah ba.
Tunda Abdallah ya kai minzalin aure bayan kammala karatunsa na degree aketa fama da shi yayi aure amma yaƙi, acewarsa Nu'aymah yake so. An lallaɓashi akan ya auri wata idan Nu'aymah ta isa saiya ƙara da ita, amma sam yace bazata saɓuba, zai jirata ko shekara nawane. Abin ya bama kowa mamaki, dan lokacinma fa Nu'aymah da Adawiya suna firamare aji shidda ne. Haka kowa ya haƙura aka zuba masa ido, sai ma ya koma karatu da kasuwancinsa na kansa daya ƙirƙira, ya duƙufa wajen faɗaɗa karatunsa na addini kuma tamkar iyayensa.
A wannan shekarar Abban Abdallah ya sake komawa Abuja da zama inda canma suka buɗe reshen Company ɗinsu na mangyaɗa, sai aka bar Abba Musbahu a Lagos. Tunda suka dawo Abuja Momyn Abdallah ta fara jan yaronta jikinta sosai, a hankali ta janye ra'ayinsa ya koma Abuja da zama wajensu, inda harkokin kasuwancinsa suka fara faɗaɗa daga Nigeria zuwa ƙasar Saudia. Lokacin kuma Adawiya da Nu'aymah sun shiga sakandire.
Suna aji uku a secondary Abdallah ya koma kara faɗaɗa iliminsa na addini a ƙasar Saudia inda yake kasuwancinsa yanzu, sai yazam baya zuwa sai dai aiko da kaya Nigeria Omar da Ahmad na kulawa dasu suma suna aika masa na Nigeria can.
Nu'aymah yarinyace ƙyaƙyƙyawa fara masha ALLAH, dan tana kama da mahaifiyarta sosai, yarinyace mai shegen wayo ga rashin tsoro ga tsiwa. Tsula tsiyarsu suke ita da Adawiya fiye da zato, kullum cikin jan faɗa suke a makaranta daga boko har islamiyya. Duk da rashin jinsu yarane masu kaifin basira da hazaƙa musamman ma Nu'aymah, tana da matuƙar ƙoƙari, dan tun tana aji biyu na secondary tayi saukar Qur'ani, bayan tayi da shekara ɗaya itama Adawiya tayi. Bayan duk sunyi sauka suka juya hadda, tare da karatun sauran littatafai kuma.
Hazaƙar Nu'aymah a makaranta yasa suna aji biyar wani malami ya bada shawarar a barta kawai ta zana ssce a wannan shekarar, koba komai zata kammala jami'a da ƙarancin shekaru. Baba malam ya amshi wannan shawarar, musamman daya duba maganar auren Nu'aymah da Abdallah da kowa ke jira, ya yanke shawarar tana zana ssce za'ayi auren sai taje ta cigaba da karatunta a ɗakin mijinta kawai. amma saiya sa suyi ssce ɗin tare da Adawiya. Wannan shine ya sakasu gama makaranta a wannan shekarar. Adawiya dasu Amal nada shekaru sha bakwai cif, Nu'aymah kuwa bata cikaba har yanzu, tana sha shida da wasu watanni dan su Adawiya sun girmeta...............✍
ZAFAFA BIYAR 2021
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
*_Typing📲_*
*_SARAN ƁOYE!!_*
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
Free page😋
_Daga yau free pages sun ƙare masoya. Ku garzayo domin samun waɗanan littatafai guda biyar akan farashi mai sauƙi. Dan girman ALLAH kibi ta hanyar data dace ki mallaki naki😅, karki zama cikin masoya masu mana SARAN ƁOYE akan kasuwancinmu😢🙏, muna alfahari daku aduk inda kuke. Muna godiya kuma da ƙaunar da kuke nuna mana irin trillions ɗin nan. Idan nace ku na dabanne ina nufin na daban har cikin raina😘😘🤝🏻_.
*_Masu buƙatar mu saka musu tallar kayan sana'arsu zasu iya zuwa suyi magana damu domin tayasu tallata hajojinsu a yanar gizo😘🤝🏻_*.
No. 5