Sashe 168
Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Washe gari ƙarfe goma na safe Omar (Rich) ya iso hotel ɗin daga birnin Lagos. Ya iske Yoohan ɗin cikin shirin suit royal blue da sukai masa masifar ƙyau. Musamman yanzu da yay wani ɗan ɓul-ɓul dashi saboda madarar angwanci data hudashi. Rungume juna sukai cike da so da ƙyauna da begen juna. Kai kace basa waya kullum. Bayan sun gama ƴar chapter ɗinsu da suka iya suka fito gwanin sha'awa zuwa motar Omar ɗin. Omar ne ya jasu zuwa headquarter ƴan sanda na jami'an tsaron sirri suna ƴar hirarsu.
Sai da suka gama shan tambayoyi da uban bincike kafin su sami damar shiga da taimakon abokin Yoohan ɗin da aka sanarma zuwansu daga baya.
Da ƴar dariya Dawood yake kallon Yoohan daya ciskule fuska saboda haushi binciken da akaita musu yana faɗin. “Yi haƙuri bokan turai, wlhy banyi tunanin zakuzo a yau bane da nazo na tsaya a gate ɗin na jira isowarku ai. Tunda aka ɗora mana adalin shigaba a hukumarnan tamu tsaro ya ƙara tsauri dan sam bashi da wasa”.
Dariya shima Omar yayi yana taɓe baki. Yace, “Kai Dawood manta da lamarinsa kewar matarsa ke ɗawainiya da shi badan wannan binciken yake fushi ba”.
Hararsu Yoohan yayi su duka amma baice komaiba. Da haka suka ƙarasa can sama inda office ɗin oga kwata-kwata na hukumar DSS yake. Duk da Dawood yay masa bayani akan zuwan su Yoohan ɗin sai da suka jira shi ya fara shiga office ɗin sannan ya fito yay musu iso.
Ƙyaƙyƙyawan dattijo ne da a shekaru a ƙalla zai iya kaiwa 64 Zaune a kan kujerar office ɗin hankalinsa gaba ɗaya akan Computer ɗin dake saman desk ɗinsa. Batare da ya ɗago ba ya amsa musu sallamarsu cike da nutsatstsiyar muryarsa mai tarin kamala da dattako.
Sosai kwarjininsa ya cika zukatan su Yoohan duk da bai ɗago sunga fuskar tasa ba da ƙyau. Da hannu yaɗan nuna musu kujerun yana faɗin, “Bismillanku”.
Kusan a tare Omar da Yoohan suka sauke ajiyar zuciya da duban Dawood dake ƙame a tsaye. Kai shima ya jinjina musu alamar su zauna ɗin. Zaman sukayi tare da haɗa baki wajen faɗin, “Good morning sir”.
Cikin ɗan fesar da iska Boss *_Jawaad Abdul-aziz Yusif tafida_* ya ɗago gaba ɗayansa fuska babu walwala kamar ko yaushe yace, “Good Morning”. yay maganar da miƙa musu hannunsa alamun suyi musabuha.
Omar ne ya fara miƙo masa hannun suka gaisa, kafin ya miƙama Yoohan da shima zuciyarsa ke wani bugawa da harbawa da sauri-sauri. sai dai cike da dauriya ya faɗaɗa fuskarsa da murmushin ƙarfin hali.
Da ga shi har Boss Jay zukatansu suka buga da ƙarfi. Hannun Yoohan ya dinga rawa dan yama kasa ƙarasawa da shi inda na Jay dake ƙoƙarin zare glass ɗin idonsa yake.
Hakan yayi dai-dai da shigowar wata kamilalliyar mace da shekarunta zai kai kimanin 53 cikin office da sallama, hannun ta riƙe da takardu. Sanye take cikin doguwar rigar jallabiya baƙa. Shigar tata ta ƙara fidda kamalarta da mutuncinta ga mai kallonta.
Akan mijin nata ta fara sauke idanunta da mamakin yanayin data gansa. Sai kuma ta maida dubanta ga abinda yakema kallon ruɗani da tsoro. Baya tayi da sauri har takardun hannunta na watsewa a ƙasa. Saurin sunkuyawa Dawood da ke binsu da kallon mamaki yayi yana tattare takardun da faɗin, “Am sorry maa”.
Bilkisu bata iya cewa komaiba sai takawa da tai da sauri inda Jay yake. Zatai magana yay saurin damƙe hannunta alamar shi ya dawo cikin hankalinsa. Girgiza mata kai yayi alamar kartace komai. Sai ma wayancewa yayi da faɗin, “Wai nikam da gaske likitan da naso gani ruwa a jallo shekara ɗaya data shuɗe ne amma hakan ya gagareni a gabana?”.
Duk da Yoohan yaji sam a ransa ba wannan batun bane jefa adalin ma'aikacin cikin ruɗanin ganisa sai shima ya sauke ajiyar zuciyar da sam bata samun nutsuwa bace. Cike da ladabi ya jinjina kansa yana murmushin ƙarfin hali. Dan wani masifar kwarjini da Jay ya masa. Yace, “I'm very sorry sir. Nasan ni mai laifine sosai a gareka”.
“No no no son. Inama mutane irinka uziri sosai ni a rayuwa. Dan haka manta kawai da wancan batun, tuni an kauda matsalarma”. Jay ya faɗa yana maida glasess ɗinsa akan ido.
Cike da jin daɗi Yoohan yace, “Thanks you Uncle”. Sai kuma ya ɗan kalli Bilkisu da alamu suka nuna har yanzu tana a cikin ruɗani ita dai yace, “Good morning maa”.
Da wani irin sanyi tace, “Good morning dear”. Shima Omar (Rich) da al'ajabi ya cika gaisheta yayi. Ta amsa masa da kulawa shima tana duban Jay da har yanzu idanunsa akan Yoohan suke. Kauda kansa yayi ya ɗan dubeta saboda taɓa masa kafaɗa da tayi. Murmushin ƙarfin hali yay mata da nunama su Yoohan ita faɗin, “My wife. Itace naso na kawo maka a wancan lokacin muka gagara samun dama. Itama ma'aikaciyace a wannan hukumar. Amma Alhmdllh, daga baya mun fahimci babu waccan matsalar da mukai zargi”.
Cike da girmamawa Yoohan da Omar sukace masha ALLAH. ALLAH ya ƙara kiyaye gaba.
Amin suka amsa musu. Bilkisu data fahimci zamanta a wajen zai iya kawo matsala sai tai ɗanyi murmushi da ranƙwafawa saitin kunnensa tai magana. “Bara naje, su Zuhrah na jirana zamu wuce. Ga takardun nan duka na haɗo maka na case ɗin matar nan mai safarar ƙwayoyi”.
Kansa ya jinjina mata kawai yana murmushi. Yana son ɗan sumbatar matarsa babu dama. Dan haka ya kashe mata ido ɗaya cike da salon ƙwarewar manyan masoya😉😂.
Itama murtani ta maida masa da nata salon taima su Yoohan sallama ta fice. Numfashi Jay ya furzar a ɓoye. sannan ya maida duka hankalinsa gasu Yoohan da kansu ke a ƙasa. Dan gaba ɗaya zuciyar Yoohan ta gaza samun nutsuwar zama a waje ɗaya. Yadai dage yanata ambaton sunayen ALLAH kozai samu sassauci daga abinda yakeji cikin jininsa.
“Tom Doctors ina saurarenku. Dawood ya sanarmin kuna son ganina cike da magiya a garesa. Ina fatan dai lafiya ko?”.
Omar yace, “A lafiya lau sir. Wani taimako mukazo nema ne a wajenka da alfarma akan wani case”.
“Okay. Babu damuwa. Dawood zoka ɗauka dukkan bayanansu dan kar a samu kuskure ko”.
Da tsantsar girmamawa Dawood yace. “Okay sir”. Yay maganar da ƙame jikinsa waje guda yana buga kafarsa ƙasa. Hannu Jay yaɗan miƙar alamar amsawa. Daga haka ya ciro takarda da pen ya zauna ya fara sauraren bayanin da Omar ya farayi kasancewar Yoohan ya sanar masa komai dangane da gidan su Aymah akan abinda yaji daga gareta da wanda ya sani.
Sai da ya kai aya Jay ya sauke numfashi yana janye pen ɗin da yake gogawa saman laɓɓansa. Ya ɗan murmusa da faɗin, “Babbar magana. Ɗan jibiya family kam ba ɓoyayyan gida bane. dan ahaline na masu daraja saboda ilimin addini da harkokin kasuwancinsu. So dama akan samu irin waɗanan rikice-rikicen da ZAGON ƘASA a irin mafi yawan waɗan nan gidajen. Shi kuma zagon ƙasa Kamar wani SARAN ƁOYE ne mai cin rai da ruɗa tunanin wanda akemawa. So na tayaku murna tare da shigowarku cikin hasken musulinci. Na kumayi alƙawarin taimaka muku wajen ban kaɗo abinda kuke buƙata bisa son ƙyautatawarku ga Sheikh Soorajidden Hashim. Saboda nima malamina ne ai. Kuna ambata masa sunana zai baku labari. Har ɗaurin aurenku naje ma. tabbas kwanaki dana buƙaci zuwa wajensa muyi magana ya sanarmin zaiyi tafiya za'aima yarinyarsa aikin ƙwaƙwalwa a ƙasar ƙetare”.
Da jindaɗi a fuskokinsu suke dubansa.
Shima murmushi yayi yana zare glasess ɗinsa. ya cigaba da cewa, ”Ina ƙaunarsa sosai dan yayima rayuwata hidima mai yawa. Insha ALLAH nima bazan gajiya ba wajen bankaɗo azzalumai masu cin dunduniyarsa. Sai dai wannan aikin dolene ya kasance na sirri”. Yakai ƙarshen maganar da duban Dawood.
“Dawood! Ina buƙatar ganin Bilkisu Jawaad”.
Da sauri Dawood ya miƙe yana faɗin, “Okay sir”.
Sai da suka gama shan tambayoyi da uban bincike kafin su sami damar shiga da taimakon abokin Yoohan ɗin da aka sanarma zuwansu daga baya.
Da ƴar dariya Dawood yake kallon Yoohan daya ciskule fuska saboda haushi binciken da akaita musu yana faɗin. “Yi haƙuri bokan turai, wlhy banyi tunanin zakuzo a yau bane da nazo na tsaya a gate ɗin na jira isowarku ai. Tunda aka ɗora mana adalin shigaba a hukumarnan tamu tsaro ya ƙara tsauri dan sam bashi da wasa”.
Dariya shima Omar yayi yana taɓe baki. Yace, “Kai Dawood manta da lamarinsa kewar matarsa ke ɗawainiya da shi badan wannan binciken yake fushi ba”.
Hararsu Yoohan yayi su duka amma baice komaiba. Da haka suka ƙarasa can sama inda office ɗin oga kwata-kwata na hukumar DSS yake. Duk da Dawood yay masa bayani akan zuwan su Yoohan ɗin sai da suka jira shi ya fara shiga office ɗin sannan ya fito yay musu iso.
Ƙyaƙyƙyawan dattijo ne da a shekaru a ƙalla zai iya kaiwa 64 Zaune a kan kujerar office ɗin hankalinsa gaba ɗaya akan Computer ɗin dake saman desk ɗinsa. Batare da ya ɗago ba ya amsa musu sallamarsu cike da nutsatstsiyar muryarsa mai tarin kamala da dattako.
Sosai kwarjininsa ya cika zukatan su Yoohan duk da bai ɗago sunga fuskar tasa ba da ƙyau. Da hannu yaɗan nuna musu kujerun yana faɗin, “Bismillanku”.
Kusan a tare Omar da Yoohan suka sauke ajiyar zuciya da duban Dawood dake ƙame a tsaye. Kai shima ya jinjina musu alamar su zauna ɗin. Zaman sukayi tare da haɗa baki wajen faɗin, “Good morning sir”.
Cikin ɗan fesar da iska Boss *_Jawaad Abdul-aziz Yusif tafida_* ya ɗago gaba ɗayansa fuska babu walwala kamar ko yaushe yace, “Good Morning”. yay maganar da miƙa musu hannunsa alamun suyi musabuha.
Omar ne ya fara miƙo masa hannun suka gaisa, kafin ya miƙama Yoohan da shima zuciyarsa ke wani bugawa da harbawa da sauri-sauri. sai dai cike da dauriya ya faɗaɗa fuskarsa da murmushin ƙarfin hali.
Da ga shi har Boss Jay zukatansu suka buga da ƙarfi. Hannun Yoohan ya dinga rawa dan yama kasa ƙarasawa da shi inda na Jay dake ƙoƙarin zare glass ɗin idonsa yake.
Hakan yayi dai-dai da shigowar wata kamilalliyar mace da shekarunta zai kai kimanin 53 cikin office da sallama, hannun ta riƙe da takardu. Sanye take cikin doguwar rigar jallabiya baƙa. Shigar tata ta ƙara fidda kamalarta da mutuncinta ga mai kallonta.
Akan mijin nata ta fara sauke idanunta da mamakin yanayin data gansa. Sai kuma ta maida dubanta ga abinda yakema kallon ruɗani da tsoro. Baya tayi da sauri har takardun hannunta na watsewa a ƙasa. Saurin sunkuyawa Dawood da ke binsu da kallon mamaki yayi yana tattare takardun da faɗin, “Am sorry maa”.
Bilkisu bata iya cewa komaiba sai takawa da tai da sauri inda Jay yake. Zatai magana yay saurin damƙe hannunta alamar shi ya dawo cikin hankalinsa. Girgiza mata kai yayi alamar kartace komai. Sai ma wayancewa yayi da faɗin, “Wai nikam da gaske likitan da naso gani ruwa a jallo shekara ɗaya data shuɗe ne amma hakan ya gagareni a gabana?”.
Duk da Yoohan yaji sam a ransa ba wannan batun bane jefa adalin ma'aikacin cikin ruɗanin ganisa sai shima ya sauke ajiyar zuciyar da sam bata samun nutsuwa bace. Cike da ladabi ya jinjina kansa yana murmushin ƙarfin hali. Dan wani masifar kwarjini da Jay ya masa. Yace, “I'm very sorry sir. Nasan ni mai laifine sosai a gareka”.
“No no no son. Inama mutane irinka uziri sosai ni a rayuwa. Dan haka manta kawai da wancan batun, tuni an kauda matsalarma”. Jay ya faɗa yana maida glasess ɗinsa akan ido.
Cike da jin daɗi Yoohan yace, “Thanks you Uncle”. Sai kuma ya ɗan kalli Bilkisu da alamu suka nuna har yanzu tana a cikin ruɗani ita dai yace, “Good morning maa”.
Da wani irin sanyi tace, “Good morning dear”. Shima Omar (Rich) da al'ajabi ya cika gaisheta yayi. Ta amsa masa da kulawa shima tana duban Jay da har yanzu idanunsa akan Yoohan suke. Kauda kansa yayi ya ɗan dubeta saboda taɓa masa kafaɗa da tayi. Murmushin ƙarfin hali yay mata da nunama su Yoohan ita faɗin, “My wife. Itace naso na kawo maka a wancan lokacin muka gagara samun dama. Itama ma'aikaciyace a wannan hukumar. Amma Alhmdllh, daga baya mun fahimci babu waccan matsalar da mukai zargi”.
Cike da girmamawa Yoohan da Omar sukace masha ALLAH. ALLAH ya ƙara kiyaye gaba.
Amin suka amsa musu. Bilkisu data fahimci zamanta a wajen zai iya kawo matsala sai tai ɗanyi murmushi da ranƙwafawa saitin kunnensa tai magana. “Bara naje, su Zuhrah na jirana zamu wuce. Ga takardun nan duka na haɗo maka na case ɗin matar nan mai safarar ƙwayoyi”.
Kansa ya jinjina mata kawai yana murmushi. Yana son ɗan sumbatar matarsa babu dama. Dan haka ya kashe mata ido ɗaya cike da salon ƙwarewar manyan masoya😉😂.
Itama murtani ta maida masa da nata salon taima su Yoohan sallama ta fice. Numfashi Jay ya furzar a ɓoye. sannan ya maida duka hankalinsa gasu Yoohan da kansu ke a ƙasa. Dan gaba ɗaya zuciyar Yoohan ta gaza samun nutsuwar zama a waje ɗaya. Yadai dage yanata ambaton sunayen ALLAH kozai samu sassauci daga abinda yakeji cikin jininsa.
“Tom Doctors ina saurarenku. Dawood ya sanarmin kuna son ganina cike da magiya a garesa. Ina fatan dai lafiya ko?”.
Omar yace, “A lafiya lau sir. Wani taimako mukazo nema ne a wajenka da alfarma akan wani case”.
“Okay. Babu damuwa. Dawood zoka ɗauka dukkan bayanansu dan kar a samu kuskure ko”.
Da tsantsar girmamawa Dawood yace. “Okay sir”. Yay maganar da ƙame jikinsa waje guda yana buga kafarsa ƙasa. Hannu Jay yaɗan miƙar alamar amsawa. Daga haka ya ciro takarda da pen ya zauna ya fara sauraren bayanin da Omar ya farayi kasancewar Yoohan ya sanar masa komai dangane da gidan su Aymah akan abinda yaji daga gareta da wanda ya sani.
Sai da ya kai aya Jay ya sauke numfashi yana janye pen ɗin da yake gogawa saman laɓɓansa. Ya ɗan murmusa da faɗin, “Babbar magana. Ɗan jibiya family kam ba ɓoyayyan gida bane. dan ahaline na masu daraja saboda ilimin addini da harkokin kasuwancinsu. So dama akan samu irin waɗanan rikice-rikicen da ZAGON ƘASA a irin mafi yawan waɗan nan gidajen. Shi kuma zagon ƙasa Kamar wani SARAN ƁOYE ne mai cin rai da ruɗa tunanin wanda akemawa. So na tayaku murna tare da shigowarku cikin hasken musulinci. Na kumayi alƙawarin taimaka muku wajen ban kaɗo abinda kuke buƙata bisa son ƙyautatawarku ga Sheikh Soorajidden Hashim. Saboda nima malamina ne ai. Kuna ambata masa sunana zai baku labari. Har ɗaurin aurenku naje ma. tabbas kwanaki dana buƙaci zuwa wajensa muyi magana ya sanarmin zaiyi tafiya za'aima yarinyarsa aikin ƙwaƙwalwa a ƙasar ƙetare”.
Da jindaɗi a fuskokinsu suke dubansa.
Shima murmushi yayi yana zare glasess ɗinsa. ya cigaba da cewa, ”Ina ƙaunarsa sosai dan yayima rayuwata hidima mai yawa. Insha ALLAH nima bazan gajiya ba wajen bankaɗo azzalumai masu cin dunduniyarsa. Sai dai wannan aikin dolene ya kasance na sirri”. Yakai ƙarshen maganar da duban Dawood.
“Dawood! Ina buƙatar ganin Bilkisu Jawaad”.
Da sauri Dawood ya miƙe yana faɗin, “Okay sir”.