Sashe 148
Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Sosai Nu'aymah tasha barcinta. Bata farka ba sai bayan a wanni uku da fitar Yoohan kamar yanda ya ambata. Taji daɗin barcin sosai. ta miƙe tanata faman ɓata fuska irin ta wanda ya tashi a barci. Wanka tayo da ruwa mai ɗumi. Ta buɗe Wadrobe zata ciri kaya tajita gam. mamaki ya kamata da takaici ganin rufewa yayi. ƙunƙuni ta fara tana faɗin, ‘Gaskiya wannan mai jajayen kunnuwan yama rainani. Nasan maganinsa ai ALLAH kuwa. Sai yasan yayi da ƴar Umm da baba malam’. Ta ƙare maganar tana huci kai kace wani uban laifi akai mata. Har ta nufi gado da fushi sai kuma ta dawo da baya. Ɗayan murfin Wadrobe ɗin ta buɗe. A mamakinta sai taci karo da akwatin nasu anan. Shi ta buɗe tana ƙwafa da faɗin, ‘Na rantse akan kayanka zan huce takaicina. Dan sakasu zanyi naita birgima a ƙasan ɗakin nan har sai sunsan niɗin Zainabu ce jikar Zainabu Abu hajjaju Hajjo matar malam Hashim ɗan jibiy.......’ ta kasa ƙarasawa sabida cin karo da wata leda da tayi a gefen akwatin. Ɗauka tayi ta buɗe ledar tare da zazzago kayan ciki. ‘Ikon ALLAH sai kallo. shiko wannan bawa mi yake nufi dani dazai ajiyemin waɗannan kayan kamar ɗiyar tsuntsuwar sama jannati? Shin wai nufinsa ni jikar ɗan jibiya ce zansa wannan a tsokani shari'ar komi?, dama shiyyasa yaƙi ɗakkomin kaya sai wani jallabiya guda biyu dan tsabar ya maidani doll’. Tai maganar tana ɗaga wandon da bazai wuce rabin cinyarta ba. Ajiyesa tai ta cigaba da ɗaga sauran ma. Duk da bawani na fidda tsiraici bane sun bata haushi. Dan ba saba saka irin waɗanan ƙananun kayan tayiba a gida. Wani lokacin ko wando da riga ta saka sai Umm ta korata ta ɗora after dress a sama inhar zata fita daga sashensu. Mansa ta ɗauka ta shafa tanata cika baki da iska. Sosai takema man shafawar matsar mugunta. Wai shima sai yaji a jikinsa tunda ya saya mata waɗanan fingalallun kayan kamar wata ƴar tsana. To wlhy tunda ya raina mata jiki saita ta narkar abinci ta zama ƙatuwa kafin subar ƙasar nan. Sai tama aljihunsa ɗibar karan mahaukaciya (Danƙari. To kaji Yoohan talautaka za'ai a ƙasar Austria🤣).
Haka tasa kayan tana mita. ta ringa zazzagama jikinta turarensa wai shine target ɗin farko da zata fara. A gaban ƙaton mirror ɗakin taje ta tsaya tana kallon kanta. Ta wani riƙe ƙugu tana faɗin, ‘Woow na kumafa haɗu’ tai maganar tana jujjuyawa. ‘Yauwa nama tuna. Bara nayi yanda naga matar jiya tayi’ ta faɗa tana tattare ƙasan farar top ɗin tata ta ɗaure a gefe. Hakanne ya bama ɗingilis ɗin wandon nata kalar blue na jeans damar fitowa sosai. ‘Tab, wlhy su Umm an haifo baturiya ba'a saniba. Hummm inama zan haɗu da hajjo yanzun. Nunawafa zanyi bamma santa ba, dan saina gama folata irin nifa bamma san African ɗinnanba sannan’. Ita kanta abun sai ya bata da dariya. Ta ƙyalƙyale kuwa da ita kamar dai har yanzun kan da motsi😂.
Haka taita shirmenta ita kaɗai harta gaji ta bari taje ta gyara gadon da kanta. A wajen gyaranne taci karo da note ɗinsa. Koda ta gama karantawa saita murmusa. Wayar daya ajiye ɗin ta ɗauka ta nufi ƙofar da taga sun fita jiya ta danna yanda taga yayi da zai rufe. a take kuwa labulen ya zuge. Ta sake dannawa ƙofar glass ɗin itana ta buɗe. Farar ƙafarta dake a cikin blue Slippers ta zira waje tana wani zuƙar daddaɗar iskan wajen. Barandan ta ɗakinne kawai, hakan yasa taji ta ta sake dan babu ruwan wani da wani. Sannan anyi iyakar da waɗanda ke maƙwaftaka da ɗakin bazasu gantaba, kamar yanda itama bata ganinsu sai ainahin birnin Vienna da kuma harabar hotel ɗin da ƙaton swimming pool yake. Shima sai idan ta miƙene a jikin ƙarfen barandar zata iya ganin masu hutawa na wanka, wasu kuma suna zaune a kujeru ana zuƙar drinks.
A ɗaya daga cikin kujerar wajen ta zauna, ta ciro buk ɗaya dage cikin ɗan kantan wajen ta ajiye sannan ta hau ƙoƙarin kiran su Baba malam cike da ɗoki. Kamar kuwa jira sukeyi, tana kira ring baifi uku ba Umm ta ɗaga. Dan baba malam yana wanka a lokacin. Cike da ihun murna ta farama Umm magana. Itako daga can sai dariya take da jinjina wauta irin ta ɗiyar tata. Dan ita ta tabbatar ba kuruciyace kawai ke ɗawainiya da Aymah ba. Akwai tsantsar wauta tattare da ita. A dai ƙasar hausa mai shekaru irin nata ai budrwace cikkakkiya kowa ya sani. Biye mata tai ko tanata faman bata labarin haduwar hotel ɗin da suke, da gine-ginen garin Vienna. Harda cewa Umm bara ta katse ta kira video call wai dan ta gani. da sauri Umn tace, “A'a shugabar rawan kai na gode. Nima ai nazo na gani da idona”.
“Yo Umm ai dai bakiyi yawoba” tai maganar cike da shagwaɓa. Dariya Umm tayi da faɗin, “ALLAH ya shiryeki Nu'aymah. Ga Abbanki nidai barni na hutama raina. Ga autana can kwance yana fama da zazzaɓi bara naje naji da shi”.
A take kuma sai mood ɗin Aymah ya canja jin abokin faɗa babu lafiya. Duk sai ta marairaice kuma har ma abin ya bama Umm da baba malam dariya. Haka dai ya amsa shima ta zuba masa shiriritarta. Sai da yace ta kashe wayar haka karsu ƙararma Yoohan da kuɗi sannan sukai sallama bayan anbama Muhammad shima sun gaisa, duk da a kwance yake bayajin dadi. Daga haka Hajjo ta kira. Itama suka gaisa. Badan tasoba ta haƙura ta ajiye wayan ta ɗauki buk ɗin data ɗauka ta fara dubawa.
Haka Nu'aymah ta kasance ita kaɗai a wannan yini. Duk da gargaɗin karta zauna da yunwa da Yoohan yayta mata bataji ba, sau kusan uku ma'aikatan hotel ɗin na kawo mata abinci amma sau ɗaya taci. Da lokacin shan maganinta yayi kuma tasha kamar yanda ya rubuta mata a note ɗinsa. Novel ɗin data samu ne ya ɗauke duka hankalinta. Dan shi taita karantawa. Salla kawai ke sakata ajiyewa. Bata damu ba da rashin dawowar tasa. Tunda ya rubuta mata uzirinsa zaije ya ƙaraso yau gaba ɗaya shiyyasa. Kuma ya bata haƙuri akan barintan da zaiyi ita kaɗai ɗin.
Lokacin shan maganin darenta nayi taci abincin da aka sake kawo mata kaɗan tasha duk magungunanta tai wanka. Kwanciya tai tana cigaba da karatun buk ɗin har barci yay awon gaba da ita.
A haka Yoohan ya shigo a matuƙar gajiye ya isketa. Ya zauna a bakin gadon yana kallonta. Hannu ya kai ya zare buk ɗin data rungume a ƙirji a hankali. Motsawa tai, tare da buɗe idanunta da ƙyar ta kallesa. Batare datayi maganaba tai luu dasu ta maida tarufe kayanta tare da gyara kwanciya.
Idanu kawai ya lumshe shima ya buɗe akan buk ɗin. Batare da yace komaiba ya ajiye ya miƙe domin yin wanka.
Har ya kammala dukan hidimarsa Aymah nata barcinta. Bai tadataba kuwa yay shirin barci shima tare da sallolinsa da suka rage ya hawo gadon ya kwanta dan a matuƙar gajiye yake. Addu'ar barci yay musu ya rungume matarsa suka lula duniyar barci mai daɗi.
*_WASHE GARI_*
Haka tasa kayan tana mita. ta ringa zazzagama jikinta turarensa wai shine target ɗin farko da zata fara. A gaban ƙaton mirror ɗakin taje ta tsaya tana kallon kanta. Ta wani riƙe ƙugu tana faɗin, ‘Woow na kumafa haɗu’ tai maganar tana jujjuyawa. ‘Yauwa nama tuna. Bara nayi yanda naga matar jiya tayi’ ta faɗa tana tattare ƙasan farar top ɗin tata ta ɗaure a gefe. Hakanne ya bama ɗingilis ɗin wandon nata kalar blue na jeans damar fitowa sosai. ‘Tab, wlhy su Umm an haifo baturiya ba'a saniba. Hummm inama zan haɗu da hajjo yanzun. Nunawafa zanyi bamma santa ba, dan saina gama folata irin nifa bamma san African ɗinnanba sannan’. Ita kanta abun sai ya bata da dariya. Ta ƙyalƙyale kuwa da ita kamar dai har yanzun kan da motsi😂.
Haka taita shirmenta ita kaɗai harta gaji ta bari taje ta gyara gadon da kanta. A wajen gyaranne taci karo da note ɗinsa. Koda ta gama karantawa saita murmusa. Wayar daya ajiye ɗin ta ɗauka ta nufi ƙofar da taga sun fita jiya ta danna yanda taga yayi da zai rufe. a take kuwa labulen ya zuge. Ta sake dannawa ƙofar glass ɗin itana ta buɗe. Farar ƙafarta dake a cikin blue Slippers ta zira waje tana wani zuƙar daddaɗar iskan wajen. Barandan ta ɗakinne kawai, hakan yasa taji ta ta sake dan babu ruwan wani da wani. Sannan anyi iyakar da waɗanda ke maƙwaftaka da ɗakin bazasu gantaba, kamar yanda itama bata ganinsu sai ainahin birnin Vienna da kuma harabar hotel ɗin da ƙaton swimming pool yake. Shima sai idan ta miƙene a jikin ƙarfen barandar zata iya ganin masu hutawa na wanka, wasu kuma suna zaune a kujeru ana zuƙar drinks.
A ɗaya daga cikin kujerar wajen ta zauna, ta ciro buk ɗaya dage cikin ɗan kantan wajen ta ajiye sannan ta hau ƙoƙarin kiran su Baba malam cike da ɗoki. Kamar kuwa jira sukeyi, tana kira ring baifi uku ba Umm ta ɗaga. Dan baba malam yana wanka a lokacin. Cike da ihun murna ta farama Umm magana. Itako daga can sai dariya take da jinjina wauta irin ta ɗiyar tata. Dan ita ta tabbatar ba kuruciyace kawai ke ɗawainiya da Aymah ba. Akwai tsantsar wauta tattare da ita. A dai ƙasar hausa mai shekaru irin nata ai budrwace cikkakkiya kowa ya sani. Biye mata tai ko tanata faman bata labarin haduwar hotel ɗin da suke, da gine-ginen garin Vienna. Harda cewa Umm bara ta katse ta kira video call wai dan ta gani. da sauri Umn tace, “A'a shugabar rawan kai na gode. Nima ai nazo na gani da idona”.
“Yo Umm ai dai bakiyi yawoba” tai maganar cike da shagwaɓa. Dariya Umm tayi da faɗin, “ALLAH ya shiryeki Nu'aymah. Ga Abbanki nidai barni na hutama raina. Ga autana can kwance yana fama da zazzaɓi bara naje naji da shi”.
A take kuma sai mood ɗin Aymah ya canja jin abokin faɗa babu lafiya. Duk sai ta marairaice kuma har ma abin ya bama Umm da baba malam dariya. Haka dai ya amsa shima ta zuba masa shiriritarta. Sai da yace ta kashe wayar haka karsu ƙararma Yoohan da kuɗi sannan sukai sallama bayan anbama Muhammad shima sun gaisa, duk da a kwance yake bayajin dadi. Daga haka Hajjo ta kira. Itama suka gaisa. Badan tasoba ta haƙura ta ajiye wayan ta ɗauki buk ɗin data ɗauka ta fara dubawa.
Haka Nu'aymah ta kasance ita kaɗai a wannan yini. Duk da gargaɗin karta zauna da yunwa da Yoohan yayta mata bataji ba, sau kusan uku ma'aikatan hotel ɗin na kawo mata abinci amma sau ɗaya taci. Da lokacin shan maganinta yayi kuma tasha kamar yanda ya rubuta mata a note ɗinsa. Novel ɗin data samu ne ya ɗauke duka hankalinta. Dan shi taita karantawa. Salla kawai ke sakata ajiyewa. Bata damu ba da rashin dawowar tasa. Tunda ya rubuta mata uzirinsa zaije ya ƙaraso yau gaba ɗaya shiyyasa. Kuma ya bata haƙuri akan barintan da zaiyi ita kaɗai ɗin.
Lokacin shan maganin darenta nayi taci abincin da aka sake kawo mata kaɗan tasha duk magungunanta tai wanka. Kwanciya tai tana cigaba da karatun buk ɗin har barci yay awon gaba da ita.
A haka Yoohan ya shigo a matuƙar gajiye ya isketa. Ya zauna a bakin gadon yana kallonta. Hannu ya kai ya zare buk ɗin data rungume a ƙirji a hankali. Motsawa tai, tare da buɗe idanunta da ƙyar ta kallesa. Batare datayi maganaba tai luu dasu ta maida tarufe kayanta tare da gyara kwanciya.
Idanu kawai ya lumshe shima ya buɗe akan buk ɗin. Batare da yace komaiba ya ajiye ya miƙe domin yin wanka.
Har ya kammala dukan hidimarsa Aymah nata barcinta. Bai tadataba kuwa yay shirin barci shima tare da sallolinsa da suka rage ya hawo gadon ya kwanta dan a matuƙar gajiye yake. Addu'ar barci yay musu ya rungume matarsa suka lula duniyar barci mai daɗi.
*_WASHE GARI_*