Sashe 182
Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Hankalin papa ya sake tashi da abinda mahaifiyarsa keyi. Dan har cikin zuciya shima a kiɗimen yake game dayin tozali da wannan cikin da ko a labari bai taɓa sanin akwaishi ba. Lallai wannan shine lokacin daya kamata a fara yaƙin na gaske. Dan tura takai bango anzo dai-dai wajen.
Madam Chioma kam ihu takeyi da kururuwa har su Yoohan dake sama na jiyota.
Idanun Aymah da a yanzu sam batason yawan hayaniya cike da ƙwalla ta kalli Yoohan daketa kai da kawowa a cikin falon. “Yah Yoohan Please ka barni na wuce kano kawai zaifi. Wannan wane irin tashin hankaline? Maimakon ciki ya zama abin farin ciki sai kuma a maidashi tashin hankali? Kayi haƙuri mahaifiyarka ce, amma ina tsoron ta cutar dani nikam gaskiyar magana”.
Kallonta kawai Yoohan yake ransa na ƙara zafafa. Sai dai sam baiji zafin kalamanta ba, dan yasan gaskiyarta take faɗa. Shi kansa a yau ɗin nan ya sake shiga ruɗani dangane da halin mahaifiyar tasa. Wace irin uwace ita? Miyasa halayenta suka banbanta dana sauran iyaye? Tunba yanzuba wasu abubuwan nata suke dama masa lissafinsa da zurmasa a yawan tunani. Sai dai bai taɓa zaman musu fashin baƙiba saboda karta munana a cikin idanunsa. A wannan karon kam yaji bazai iyaba, dolene ko yanaso ko bayaso yasan dilin da yasa mahaifiyar tasa zafafa abubuwa akansa bayan kuma bashi kaɗai bane gudan jininta........
“Yah Yoohan maganafa nake”.
Nu'aymah ta dawo dashi hankalinsa saboda riƙe masa hannu da tayi. Nannauyan numfashi ya sauke tare da rungumota jikinsa yana sauke tagwayen ajiyar zuciya. Sunkai tsahon mintuna uku a haka sannan ya ɗagota, fuskarta cikin tafin hannayensa yana mai kallon ƙwayar idanunta data cika da hawaye. “Nima nafi aminta da tafiyarki Kano baby love, amma ina roƙonki kiyi haƙuri da safe idan ALLAH ya kaimu sai mu wuce kinji. Karkuma ki damu da zantukan Momy babu abinda zatai miki ɓacin rai ne kawai yasata faɗinsu itama kinji Heartbeat ɗina”.
Duk da bata gamsu baneba sai ta ɗaga masa kanta dan babu abinda take hange a cikin idanusa sai tsantsar tashin hankali da damuwa, itakuwa indai akan iyayensane bazata bari ya shiga tashin hankaliba insha ALLAH.
Yaji daɗin yanda ta nuna ta amince. Dan haka ya zaunar da ita duk da akwai ƴar ƙura a falon. Fita yay da kansa. Bai iske Momy ba da papa a falon, da alama sun shige daga ciki. Sai mama debora dake waya tana masifa da alama da ɗaya a cikin su momy Destiny take wayar, dan tana faɗa mata abinda ya farune.
Baibi takantaba itama yay kiran Blessing dasu Destiny suzo su musu gyara. Tare ya koma dasu, ya zauna yana mammatsama Aymah ƙafa daya tarar tana matsawa, su kuma suka fara aikin gyaran.
Koda suka kammala ɗakinsa ya janyeta sukai wanka a tare. Suna fitowa babu jimawa Blessing tai knocking. Jallabiya ya zura ya fita danya duba wanene?. Samunta yay tsaye da ƙaton tire ɗauke da abinci. Hanya ya bata ta shiga. Ta ajiye tiren a dining sannan ta fita kanta a ƙasa. Ƙofar ya maida ya rufe, yaje ya ɗauki tiren ya nufi ɗakinsa da shi.
Nu'aymah na kwance a gado ko towel ɗin jikinsa ta kasa cirewa saboda gajiya da barcin dake ci mata idanu. “Kefa yanzu kin zama raguwa Sweet girl. Tashi to ga abinci”.
Tashi tai zaune fuskarta da murmushi itama. Tace, “Duk ba ɗanka bane ya maidani hakan? Nida naci burin duk randa nazo 9ja yawo sai inda ƙarfina ya ƙare. Amma gashi tun ba'aje ko inaba lalaci ya fara mamayeni”.
Ƴar dariya yayi yana miƙa mata t-shirt ɗinsa mai girma sosai. Ta amsa ta saka sannan tazo inda yake zuba abincin. Tasan Blessing ce tai girkin shiyyasa zataci. Da taimakon Yoohan kuwa taci ta ƙoshi tai nak, shima ta bashi yaci sai dai kaɗan yaci dan sam zuciyarsa bata cikin jin daɗi. Yana dannewane kawai danya ƙarfafa Nu'aymah.
Suna gamawa gadonsa ta haye ta kwanta saboda uban barcin dake cimata idanu. Bai hanataba, saboda shima yafi buƙatar tayi barcin a yanzu. Babu jimawa kuwa barci mai nauyi yay gaba da ita.
_________★
Tunda Blessing mai kawoma Omar rahoton gidansu Yoohan ta kirashi ta sanar masa da abinda ya faru game da isowar su Yoohan ɗin hankalin Umar yay ƙololuwar tashi. dan shi kansa da yasan Yoohan gidansu zai wuce da Nu'aymah ba hotel ba ko kano da bazai bariba. Dolene shima yau ya kwana abuja kuwa dan harga ALLAH lamarin papan Yoohan yanzu tsoro yake bashi harma Momyn, bai ƙara tsinkewa da al'amarinsu ba sai akan abinda ya faru tsakanin Yoohan ɗin da Momy. duk da su hasashe sukeyi tunda su su Blessing bawai sunga komai baneba akan idonsu.
A take ya bincika ko akwai jirgi mai tashi zuwa abuja. Yakoyi sa'ar samun mai tashi nanda sa'oi biyu, dama shekaran jiya ya baro Abujan ai. Bai kira Yoohan ba, dan yafi son ya gansa tsulum kawai a bazata.
___________★
Shiko Yoohan yana samu Aymah tayi barci saiya fito zuwa sashen papa. Zaune ya samesa a falo yana waya. Yana ganin sa kuma ya yanke wayar. Ko a jikin Yoohan, dan ba wannan ne ya kawosa ba.
Zama yay a kujera, batare da ya dubesa ba yace, “Good afternoon”.
Papa ya danne abinda ke a maƙoshinsa da ƙyar ya amsa masa. Ya ɗora da faɗin, “Saukar yaushe haka babu labari. Aini nazata yanzu ni narigada na haifama Sheikh Sooraj ne kai?”.
Shiru Yoohan yayi baiyi magana ba. Hakan sai ya ƙara harzuƙa papa matuƙa. Cikin tsagwaron masifa yace, “Ina magana da kai kamin banza. Wato na fahimci dama nika maida ɗan iska game da cewar wani aiki kakeyi akansa. John dolene yau insan minene tsakaninka da Sooraj?”.
A matuƙar ɓacin ran da Yoohan shima baisan dalilinsaba, cike da suɓutar baki yace, “Papa nima inason sanin shin da gaske Momy itace ta haifeni? Dan ban taɓa jin mai halin uwa irintaba. Inhar ka amsamin wannan tambayar ni kuma na maka alƙawarin sanar maka alaƙata da Uncle Soorajidden Hashim jibiya. Sannan kama matarka gargaɗi, wlhy inhar wani abu ya samu cikina ko matata a gidan nan komaima zan iya aikatawa..”
Yana kaiwa nan ya miƙe fuuuu ya fito yana huci. Da sauri madam Chioma dake bakin ƙofar tsaye tai baya ta bashi hanya cikin matuƙar rawar jiki da tsagwaron tashin hankali. Dan taji komai daya gudana tsakanin papa da ɗan nata.
Wani irin zufar tashin hankalice ta shiga karyoma papa. Jikinsa na rawa ya zamo ƙasa daɓas kan carpet ya zauna. Gaba ɗayama duniyar sai take juya masa. Yau John ɗinsane ke kallan cikin idanunsa yana faɗa masa magana irin haka babu kunya babu tsoro. To tayaya hakan ta faru? Minene kuskurensa? Karfa ace lokacin da yake jira domin nasara ne ke shirin masa juyen ruwan hadarin da ba'a tsammaci zuwansa ba. cikin rawar jiki ya miƙe ya nufi bedroom ɗinsa batare da ya kula da madam Chioma dake a tashin hankalinba itama. A gurguje yay shiri ya fito daga ɗakin. Idonsa a rufe ya sake bangaje madam Chioma ya wuce dan harga ALLAH bai gantaba yanzuma, idanunsa har wani yana-yana suke masa saboda jirkicewar ƙwaƙwalwa dana tunani...........✍
ZAFAFA BIYAR 2021
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.[7/6, 9:38 AM] +234 913 412 2711: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.
No. 72
Madam Chioma kam ihu takeyi da kururuwa har su Yoohan dake sama na jiyota.
Idanun Aymah da a yanzu sam batason yawan hayaniya cike da ƙwalla ta kalli Yoohan daketa kai da kawowa a cikin falon. “Yah Yoohan Please ka barni na wuce kano kawai zaifi. Wannan wane irin tashin hankaline? Maimakon ciki ya zama abin farin ciki sai kuma a maidashi tashin hankali? Kayi haƙuri mahaifiyarka ce, amma ina tsoron ta cutar dani nikam gaskiyar magana”.
Kallonta kawai Yoohan yake ransa na ƙara zafafa. Sai dai sam baiji zafin kalamanta ba, dan yasan gaskiyarta take faɗa. Shi kansa a yau ɗin nan ya sake shiga ruɗani dangane da halin mahaifiyar tasa. Wace irin uwace ita? Miyasa halayenta suka banbanta dana sauran iyaye? Tunba yanzuba wasu abubuwan nata suke dama masa lissafinsa da zurmasa a yawan tunani. Sai dai bai taɓa zaman musu fashin baƙiba saboda karta munana a cikin idanunsa. A wannan karon kam yaji bazai iyaba, dolene ko yanaso ko bayaso yasan dilin da yasa mahaifiyar tasa zafafa abubuwa akansa bayan kuma bashi kaɗai bane gudan jininta........
“Yah Yoohan maganafa nake”.
Nu'aymah ta dawo dashi hankalinsa saboda riƙe masa hannu da tayi. Nannauyan numfashi ya sauke tare da rungumota jikinsa yana sauke tagwayen ajiyar zuciya. Sunkai tsahon mintuna uku a haka sannan ya ɗagota, fuskarta cikin tafin hannayensa yana mai kallon ƙwayar idanunta data cika da hawaye. “Nima nafi aminta da tafiyarki Kano baby love, amma ina roƙonki kiyi haƙuri da safe idan ALLAH ya kaimu sai mu wuce kinji. Karkuma ki damu da zantukan Momy babu abinda zatai miki ɓacin rai ne kawai yasata faɗinsu itama kinji Heartbeat ɗina”.
Duk da bata gamsu baneba sai ta ɗaga masa kanta dan babu abinda take hange a cikin idanusa sai tsantsar tashin hankali da damuwa, itakuwa indai akan iyayensane bazata bari ya shiga tashin hankaliba insha ALLAH.
Yaji daɗin yanda ta nuna ta amince. Dan haka ya zaunar da ita duk da akwai ƴar ƙura a falon. Fita yay da kansa. Bai iske Momy ba da papa a falon, da alama sun shige daga ciki. Sai mama debora dake waya tana masifa da alama da ɗaya a cikin su momy Destiny take wayar, dan tana faɗa mata abinda ya farune.
Baibi takantaba itama yay kiran Blessing dasu Destiny suzo su musu gyara. Tare ya koma dasu, ya zauna yana mammatsama Aymah ƙafa daya tarar tana matsawa, su kuma suka fara aikin gyaran.
Koda suka kammala ɗakinsa ya janyeta sukai wanka a tare. Suna fitowa babu jimawa Blessing tai knocking. Jallabiya ya zura ya fita danya duba wanene?. Samunta yay tsaye da ƙaton tire ɗauke da abinci. Hanya ya bata ta shiga. Ta ajiye tiren a dining sannan ta fita kanta a ƙasa. Ƙofar ya maida ya rufe, yaje ya ɗauki tiren ya nufi ɗakinsa da shi.
Nu'aymah na kwance a gado ko towel ɗin jikinsa ta kasa cirewa saboda gajiya da barcin dake ci mata idanu. “Kefa yanzu kin zama raguwa Sweet girl. Tashi to ga abinci”.
Tashi tai zaune fuskarta da murmushi itama. Tace, “Duk ba ɗanka bane ya maidani hakan? Nida naci burin duk randa nazo 9ja yawo sai inda ƙarfina ya ƙare. Amma gashi tun ba'aje ko inaba lalaci ya fara mamayeni”.
Ƴar dariya yayi yana miƙa mata t-shirt ɗinsa mai girma sosai. Ta amsa ta saka sannan tazo inda yake zuba abincin. Tasan Blessing ce tai girkin shiyyasa zataci. Da taimakon Yoohan kuwa taci ta ƙoshi tai nak, shima ta bashi yaci sai dai kaɗan yaci dan sam zuciyarsa bata cikin jin daɗi. Yana dannewane kawai danya ƙarfafa Nu'aymah.
Suna gamawa gadonsa ta haye ta kwanta saboda uban barcin dake cimata idanu. Bai hanataba, saboda shima yafi buƙatar tayi barcin a yanzu. Babu jimawa kuwa barci mai nauyi yay gaba da ita.
_________★
Tunda Blessing mai kawoma Omar rahoton gidansu Yoohan ta kirashi ta sanar masa da abinda ya faru game da isowar su Yoohan ɗin hankalin Umar yay ƙololuwar tashi. dan shi kansa da yasan Yoohan gidansu zai wuce da Nu'aymah ba hotel ba ko kano da bazai bariba. Dolene shima yau ya kwana abuja kuwa dan harga ALLAH lamarin papan Yoohan yanzu tsoro yake bashi harma Momyn, bai ƙara tsinkewa da al'amarinsu ba sai akan abinda ya faru tsakanin Yoohan ɗin da Momy. duk da su hasashe sukeyi tunda su su Blessing bawai sunga komai baneba akan idonsu.
A take ya bincika ko akwai jirgi mai tashi zuwa abuja. Yakoyi sa'ar samun mai tashi nanda sa'oi biyu, dama shekaran jiya ya baro Abujan ai. Bai kira Yoohan ba, dan yafi son ya gansa tsulum kawai a bazata.
___________★
Shiko Yoohan yana samu Aymah tayi barci saiya fito zuwa sashen papa. Zaune ya samesa a falo yana waya. Yana ganin sa kuma ya yanke wayar. Ko a jikin Yoohan, dan ba wannan ne ya kawosa ba.
Zama yay a kujera, batare da ya dubesa ba yace, “Good afternoon”.
Papa ya danne abinda ke a maƙoshinsa da ƙyar ya amsa masa. Ya ɗora da faɗin, “Saukar yaushe haka babu labari. Aini nazata yanzu ni narigada na haifama Sheikh Sooraj ne kai?”.
Shiru Yoohan yayi baiyi magana ba. Hakan sai ya ƙara harzuƙa papa matuƙa. Cikin tsagwaron masifa yace, “Ina magana da kai kamin banza. Wato na fahimci dama nika maida ɗan iska game da cewar wani aiki kakeyi akansa. John dolene yau insan minene tsakaninka da Sooraj?”.
A matuƙar ɓacin ran da Yoohan shima baisan dalilinsaba, cike da suɓutar baki yace, “Papa nima inason sanin shin da gaske Momy itace ta haifeni? Dan ban taɓa jin mai halin uwa irintaba. Inhar ka amsamin wannan tambayar ni kuma na maka alƙawarin sanar maka alaƙata da Uncle Soorajidden Hashim jibiya. Sannan kama matarka gargaɗi, wlhy inhar wani abu ya samu cikina ko matata a gidan nan komaima zan iya aikatawa..”
Yana kaiwa nan ya miƙe fuuuu ya fito yana huci. Da sauri madam Chioma dake bakin ƙofar tsaye tai baya ta bashi hanya cikin matuƙar rawar jiki da tsagwaron tashin hankali. Dan taji komai daya gudana tsakanin papa da ɗan nata.
Wani irin zufar tashin hankalice ta shiga karyoma papa. Jikinsa na rawa ya zamo ƙasa daɓas kan carpet ya zauna. Gaba ɗayama duniyar sai take juya masa. Yau John ɗinsane ke kallan cikin idanunsa yana faɗa masa magana irin haka babu kunya babu tsoro. To tayaya hakan ta faru? Minene kuskurensa? Karfa ace lokacin da yake jira domin nasara ne ke shirin masa juyen ruwan hadarin da ba'a tsammaci zuwansa ba. cikin rawar jiki ya miƙe ya nufi bedroom ɗinsa batare da ya kula da madam Chioma dake a tashin hankalinba itama. A gurguje yay shiri ya fito daga ɗakin. Idonsa a rufe ya sake bangaje madam Chioma ya wuce dan harga ALLAH bai gantaba yanzuma, idanunsa har wani yana-yana suke masa saboda jirkicewar ƙwaƙwalwa dana tunani...........✍
ZAFAFA BIYAR 2021
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.[7/6, 9:38 AM] +234 913 412 2711: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.
No. 72