Sashe 183
Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
...........Washe gari bayan sallar asuba Nu'aymah ta ɗorama Yoohan karatu kamar yanda suka saba. Daga haka ya shiga ɗakin motsa jikinsa. Ita kuma sai tayi amfani da wannan damar ta shiga ɗakinta domin ɗakko hoton nan. Duk da ta jima bata shigesaba ta fahimci an canja mata zaman wasu abubuwa da dama. Wasuma babusu. Bata bar hakan ya dametaba ta nufi Wadrobe direct inda ta ajiye hoto. Sosai gabanta ya faɗi ganin yanda kayanta suka koma a harmutse ba yanda tasan sukeba. Cikin gigita ta shiga tiɗosu ƙasa tana faman zazzagewa. Sai dai kamar da wasa babu hoto babu labarinsa. Hankalinta ya tashi, har takaita da duba indama tasan bata ajiye ɗinba amma ko mai alamarsa babu.
Jagwab ta zauna a bakin gado tanabin ɗakin da kallo daki-daki, dan sai a yanzune ma harmutsewarsa ba yanda ta barsaba yake dawo mata a zuciya daki-daki. Yoohan ta fara kawowa a zuciyarta. Sai kuma ta girgiza kanta dan bata tunanin zai mata bincike. Can ƙasan zuciyarta yace, ‘Omar ne. Bashi kika sanarma maganar hotonba’. Nanma da sauri ta girgiza kanta alamar a'a. Gebrail. ‘Kai bazai zama shiba. Dan shi manufarsa daban data masu hankali. Wannan bashi da man kai akan hakan’. Madam Chioma. Nanma a fili tace, ‘Kai ina bana sata a wannan layin dan kanta baya ja tacika kidahumanci kamar kifi’. ‘To wa zan zarga?. Ko dai papa ne?’. Mikewa tai da sauri tana kaɗa kanta hannayenta duka biyu a saman cikinta. ‘Lallai tabbas shine abin zargina, musamman daya kasance ya riga yabi diddigina akan shigar masa ɗaki da nayi, zai iya kasancewa tunaninsa ya basa zuwa nan yamin bincike. Shin minene wannan mutumin ke ɓoyewane akan mijina? Lallai ya kamata na sani kafin na sake barin ƙasar nan’. Sai kuma ta dafe goshi cike da damuwa. ‘Hoto shine kawai hope ɗina. Gashi yanzu ɗan barahazar ya sace min, bayan na gama baza bayani wajen Abbana da wannan Umar ɗin. Kenan dolene na sake satowa. (Idan bai ƙonaba ko?) zuciyarta ta ayyana mata. Karan farko da matsanancin tsoro ya risketa. Da sauri ta fita a ɗakin zuwa can cikin gidan. Gidan shiru alamar masu gidan babu wanda ya tashi kasancewar weekend ne. Kitchen ta nufa. Tako iske Blessing kawai tana haɗa breakfast kamar yanda tayi hasashe.
Ko gaisuwar Blessing ɗin bata amsaba taja hannunta suka shige cikin store. Sai da ta leƙa ta tabbatar da babu kowa sannan ta tura ƙofar store ɗin ta rufe ta juyo ga Blessing da jikinta harya fara rawa. “Please ki nutsu, ba wani abu bane tambaya zan miki, ina fatan kuma zaki bani amsa kamar yanda kike bama Omar... Oh sorry Richard”.
Cike da tsoro Blessing zata fara rantse-rantse Aymah ta tsaidata......
“Karki wahal da kanki wajen mani rantsuwa nasan komai daga wajensa. Inason nasan zuwan Richard nawa gidan nan?”.
Da tsoro sosai a fuskar Blessing tace, kusan bakwai”.
“Dama can anan yake sauka kenan tunkan aurena da Yoohan kokuwa a yanzune yake sauka anan?”.
“Eh dama yana sauka gaskiya, amma sai Oga yana ƙasar”.
Jimm Nu'aymah tayi alamar tunani, sai kuma tace, “Mikike tunanin yana zuwa yi nan gidan?”.
Cike da tsoro sosai Blessing ta buɗe ƙofar kaɗan ta leƙa, hakan yasa Yoohan daya biyo Aymah yake a laɓe saurin komawa ya lafe a bango. sai da ta sake tabbatar da babu kowa sannan ta dubi Aymah murya can ƙasa sosai. “Na yarda dake sosai Aunty na, dan tun a zuwanki gidan nan na fahimci ke mutuniyar kirkice wlhy. dan haka zan sanar miki komai duk da nima ba komai ɗin na saniba”.
“Okay ina saurarenki”.
“Tun bayan wucewarku Austria nakeji wasu maganganu masu gidan nayi a kanki. Dan akwai randama na taɓajin an bada kwangilar kasheki ta hanyar likitan da zasu miki aiki. To sai dai kwanan mutuwarki bai rigada yazoba dan ke ƴar baiwane. Sai akazo baki mutuba. Su boss sunje dubaki, bandai san miya faruba bayan dawowarsu Uncle Richard naga ya nacema zuwa gidannan. Sanan yakan sani na masa wasu abubuwa akan boss ko madam ɗin gidan nan. Sannan ko baya gida zai kirani yaji mi akayi ko mi ya faru. Badai komai nake fahimtaba gaskiya, tunda banida hurumin yin komai. Sai dai matsalar dana fuskanta shine randa su papa suka shiga sashenku ita da Solomon da Madam. Sun miki bincike a ɗaki sai dai basu sami komaiba suka fita. Bayan hakan Uncle John yazo ƙasarnan yaga yanda akai miki da ɗaki shine ya zane Gebrail a tunaninsa shine ya shigar miki. A zahiri papa baicema Uncle John komaiba akan dukan Gebrail. Amma bayan barinsa gidannan ba ƙaramin rikici akayiba tsakaninsa da maman madam dama madam ɗin. Shima kuma papan naji yana wasu maganganu tsakaninsa da Brothers ɗin nan nasa wanda ban ganema kansuba sam. Wanann rikicin ne ya saka su Maman Destiny barin gidan nan. Dan sun nuna goyon bayan Uncle Yoohan fiye da Gebrail. Shine yasa akai rikici duk suka wuce. Bayan nan kuma sai Uncle john ɗin da yazo last time madam ɗin gidan nan ta shigar masa ɗ.........”
Da sauri Yoohan dake a laɓe ya rin tse idanunsa tare da shiga kiran sunan Nu'aymah tamkar ya shigo nemantane. Rikicewa sosai Blessing tayi, amma Aymah ko'a jikinta saima ɓata fuska tayi ta buɗe ƙofar bayan ta ɗebo noodles guda biyu.
“Oh Sweet boo ganinanfa a store. Nazo amsar noodles ne a wajen Blessing shine take nunamin inda take”.
Cike da mamaki yake jinjina wayonta. Amma shima sai ya waske yana mai dafe kansa da faɗin, “Kinsa duk na ruɗe na fito ban gankiba a gaba ɗaya sashen”.
“I am sorry Hubby”.
“Silly girl yana iya dake. Yanzu yaya za'ai da Noodles ɗin?”.
“Zan dafa ne anan”. Ta faɗa saboda son ya barta ta ƙarasa jin zance a wajen Blessing.
Fahimtar hakan da yayine ya sakashi hayewa saman kitchen cabinet ɗin yana cewa, “Okay dafa to mu wuce. Dan kinsan akwaima fa inda zamuji ga lokaci nata ƙurewa, Omar ma jiranmu yakeyi tuni. Koma kibama Blessing ɗin ta dafa miki muje ki shirya data gama sai kici kawai”.
Duk da Aymah bataso hakan ba sai ta amince kawai. Dan ita bama cin noodles ɗin zatayiba sam. Blessing ta ƙwalama kira. Sai gata ta fito da sauri hannunta ɗauke da abinda zata dafa da rana irin dai shi ta tsaya ɗebowa. Sai dai kallo ɗaya Yoohan ya mata ya fahimci tsoron dake tattare da ita.
Bata dahuwar noodles ɗin tayi suka fice. Gaba ɗaya hankali Nu'aymah akan Blessing yake. Amma Yoohan yay mata tsayuwar sojan badakkare aka komai tare sukayi. Koda suka fito Blessing ta kawo noodles ɗin catai ta ƙoshi. Sai Yoohan ɗinne yaci tare da Omar. Dama yasan baci zataiba ai. Dan tunda ta samu cikin nan tabar cin indomie sam.
Koda suka gama ficewa sukai a gidan batare da sunbi takan kowa ba. garama mama debora sun haɗu da ita a falo tana shan shayi. Tako hanasu fita saida akaima Aymah addu'oi ita da cikinta. Dan tace ita yanzu ta daina yarda da madam Chioma a gidan sam😂🤣.
Jagwab ta zauna a bakin gado tanabin ɗakin da kallo daki-daki, dan sai a yanzune ma harmutsewarsa ba yanda ta barsaba yake dawo mata a zuciya daki-daki. Yoohan ta fara kawowa a zuciyarta. Sai kuma ta girgiza kanta dan bata tunanin zai mata bincike. Can ƙasan zuciyarta yace, ‘Omar ne. Bashi kika sanarma maganar hotonba’. Nanma da sauri ta girgiza kanta alamar a'a. Gebrail. ‘Kai bazai zama shiba. Dan shi manufarsa daban data masu hankali. Wannan bashi da man kai akan hakan’. Madam Chioma. Nanma a fili tace, ‘Kai ina bana sata a wannan layin dan kanta baya ja tacika kidahumanci kamar kifi’. ‘To wa zan zarga?. Ko dai papa ne?’. Mikewa tai da sauri tana kaɗa kanta hannayenta duka biyu a saman cikinta. ‘Lallai tabbas shine abin zargina, musamman daya kasance ya riga yabi diddigina akan shigar masa ɗaki da nayi, zai iya kasancewa tunaninsa ya basa zuwa nan yamin bincike. Shin minene wannan mutumin ke ɓoyewane akan mijina? Lallai ya kamata na sani kafin na sake barin ƙasar nan’. Sai kuma ta dafe goshi cike da damuwa. ‘Hoto shine kawai hope ɗina. Gashi yanzu ɗan barahazar ya sace min, bayan na gama baza bayani wajen Abbana da wannan Umar ɗin. Kenan dolene na sake satowa. (Idan bai ƙonaba ko?) zuciyarta ta ayyana mata. Karan farko da matsanancin tsoro ya risketa. Da sauri ta fita a ɗakin zuwa can cikin gidan. Gidan shiru alamar masu gidan babu wanda ya tashi kasancewar weekend ne. Kitchen ta nufa. Tako iske Blessing kawai tana haɗa breakfast kamar yanda tayi hasashe.
Ko gaisuwar Blessing ɗin bata amsaba taja hannunta suka shige cikin store. Sai da ta leƙa ta tabbatar da babu kowa sannan ta tura ƙofar store ɗin ta rufe ta juyo ga Blessing da jikinta harya fara rawa. “Please ki nutsu, ba wani abu bane tambaya zan miki, ina fatan kuma zaki bani amsa kamar yanda kike bama Omar... Oh sorry Richard”.
Cike da tsoro Blessing zata fara rantse-rantse Aymah ta tsaidata......
“Karki wahal da kanki wajen mani rantsuwa nasan komai daga wajensa. Inason nasan zuwan Richard nawa gidan nan?”.
Da tsoro sosai a fuskar Blessing tace, kusan bakwai”.
“Dama can anan yake sauka kenan tunkan aurena da Yoohan kokuwa a yanzune yake sauka anan?”.
“Eh dama yana sauka gaskiya, amma sai Oga yana ƙasar”.
Jimm Nu'aymah tayi alamar tunani, sai kuma tace, “Mikike tunanin yana zuwa yi nan gidan?”.
Cike da tsoro sosai Blessing ta buɗe ƙofar kaɗan ta leƙa, hakan yasa Yoohan daya biyo Aymah yake a laɓe saurin komawa ya lafe a bango. sai da ta sake tabbatar da babu kowa sannan ta dubi Aymah murya can ƙasa sosai. “Na yarda dake sosai Aunty na, dan tun a zuwanki gidan nan na fahimci ke mutuniyar kirkice wlhy. dan haka zan sanar miki komai duk da nima ba komai ɗin na saniba”.
“Okay ina saurarenki”.
“Tun bayan wucewarku Austria nakeji wasu maganganu masu gidan nayi a kanki. Dan akwai randama na taɓajin an bada kwangilar kasheki ta hanyar likitan da zasu miki aiki. To sai dai kwanan mutuwarki bai rigada yazoba dan ke ƴar baiwane. Sai akazo baki mutuba. Su boss sunje dubaki, bandai san miya faruba bayan dawowarsu Uncle Richard naga ya nacema zuwa gidannan. Sanan yakan sani na masa wasu abubuwa akan boss ko madam ɗin gidan nan. Sannan ko baya gida zai kirani yaji mi akayi ko mi ya faru. Badai komai nake fahimtaba gaskiya, tunda banida hurumin yin komai. Sai dai matsalar dana fuskanta shine randa su papa suka shiga sashenku ita da Solomon da Madam. Sun miki bincike a ɗaki sai dai basu sami komaiba suka fita. Bayan hakan Uncle John yazo ƙasarnan yaga yanda akai miki da ɗaki shine ya zane Gebrail a tunaninsa shine ya shigar miki. A zahiri papa baicema Uncle John komaiba akan dukan Gebrail. Amma bayan barinsa gidannan ba ƙaramin rikici akayiba tsakaninsa da maman madam dama madam ɗin. Shima kuma papan naji yana wasu maganganu tsakaninsa da Brothers ɗin nan nasa wanda ban ganema kansuba sam. Wanann rikicin ne ya saka su Maman Destiny barin gidan nan. Dan sun nuna goyon bayan Uncle Yoohan fiye da Gebrail. Shine yasa akai rikici duk suka wuce. Bayan nan kuma sai Uncle john ɗin da yazo last time madam ɗin gidan nan ta shigar masa ɗ.........”
Da sauri Yoohan dake a laɓe ya rin tse idanunsa tare da shiga kiran sunan Nu'aymah tamkar ya shigo nemantane. Rikicewa sosai Blessing tayi, amma Aymah ko'a jikinta saima ɓata fuska tayi ta buɗe ƙofar bayan ta ɗebo noodles guda biyu.
“Oh Sweet boo ganinanfa a store. Nazo amsar noodles ne a wajen Blessing shine take nunamin inda take”.
Cike da mamaki yake jinjina wayonta. Amma shima sai ya waske yana mai dafe kansa da faɗin, “Kinsa duk na ruɗe na fito ban gankiba a gaba ɗaya sashen”.
“I am sorry Hubby”.
“Silly girl yana iya dake. Yanzu yaya za'ai da Noodles ɗin?”.
“Zan dafa ne anan”. Ta faɗa saboda son ya barta ta ƙarasa jin zance a wajen Blessing.
Fahimtar hakan da yayine ya sakashi hayewa saman kitchen cabinet ɗin yana cewa, “Okay dafa to mu wuce. Dan kinsan akwaima fa inda zamuji ga lokaci nata ƙurewa, Omar ma jiranmu yakeyi tuni. Koma kibama Blessing ɗin ta dafa miki muje ki shirya data gama sai kici kawai”.
Duk da Aymah bataso hakan ba sai ta amince kawai. Dan ita bama cin noodles ɗin zatayiba sam. Blessing ta ƙwalama kira. Sai gata ta fito da sauri hannunta ɗauke da abinda zata dafa da rana irin dai shi ta tsaya ɗebowa. Sai dai kallo ɗaya Yoohan ya mata ya fahimci tsoron dake tattare da ita.
Bata dahuwar noodles ɗin tayi suka fice. Gaba ɗaya hankali Nu'aymah akan Blessing yake. Amma Yoohan yay mata tsayuwar sojan badakkare aka komai tare sukayi. Koda suka fito Blessing ta kawo noodles ɗin catai ta ƙoshi. Sai Yoohan ɗinne yaci tare da Omar. Dama yasan baci zataiba ai. Dan tunda ta samu cikin nan tabar cin indomie sam.
Koda suka gama ficewa sukai a gidan batare da sunbi takan kowa ba. garama mama debora sun haɗu da ita a falo tana shan shayi. Tako hanasu fita saida akaima Aymah addu'oi ita da cikinta. Dan tace ita yanzu ta daina yarda da madam Chioma a gidan sam😂🤣.