← Book details Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 126 OF 211

Sashe 126

Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

       Da uban ihu Nu'aymah ta shiga tana ƙwalama su Amal kira. Aiko kamar jira suma sai gasu da gudun sun fitowa suna ihun murnar ganinta. Momy na salla take jiyo ihun nasu. Sai da sukayi mai isarsu sannan suka sarara. Ɗakin Amal ɗin suka nufa inda Yusrah da Adawiya dataƙi fitowa suke hutunsu da basusan dalilinsa ba balle ranar komawa kano.
         Duk da idon Aymah ya ga Adawiya dake kwance a kan gado tana danna waya sai tai tamkar bata ganta ba ta cigaba da biyema su Yusrah dake mata sherin wai ta canja saboda daɗin aure ko sun sami baby ne?. Shaƙiyanci sukaitama juna suna sheƙa dariyar dake sake ƙullar da Adawiya. Dan suma su Amal ɗin ta ishesu. Kullum haka take yini a gidan cikin ɗacin rai, bata shiga sabgarsu basa shiga tata. Momy tayi faɗan harta gaji ta zuba musu idanu.
           Sallar suma sukayi, kafin su idar Adawiya tabar ɗakin ta koma falo. Bayan sun idar cikin dabara Aymah take tambayarsu Amal yaushe Yusrah zata tare tunda taga Yah Ab bai koma ba. Da mamaki sosai Amal tace, “Yah Ab ɗin da ya koma Saudia tun randa aka ɗaura miki aure. Kuma Yusrah ai tace bazata tare a gidansa ba saboda fitinar Adawiya”.
          Bayanin Amal ya matuƙar ɗaure kan Aymah, dan ita dai tabbas-tabbas tanaji a ranta da Yah Ab sukai gamo a inda suka baro. Sai dai batasan dalilinsa na ɓoye mata kansa ba. Danne wannan tunanin tayi a zuciyarta ta fuskanci Yusrah datai kamar bataji mi suke magana a kai ba.
         “Yusrah! Miyasa baƙya son zama da Yah Ab wai dan ALLAH?”.
       Murmushi Yusrah tayi tana ƙoƙarin miƙewa daga wajen gaba ɗaya, Aymah tai saurin maidata ta zauna. “ALLAH babu inda zakije sai kin amsamin tambaya ta”.
        “Humm Aymah kenan, ba amsa tambayarki bace mai wahala, hujjar amsata. Ni bancema kowa bana son Yah Ab ba ai. Kawai dai zaman aurene banason yi da shi. Fatan da nakeson muyi ni da ku kawai shine ya maida Adawiya ɗakinta. Indan ba hakaba kuwa tsugunne bata ƙareba a family ɗinmu wlhy. Adawiya na son Yah Ab sosai duk da nasan tabbas Nu'aymah kin fita sonsa. Amma ke yanzun wannan babin ya shafe a gareki dan dama ƙaddarace tazo muku da wannan yanayin”.
          “Amma Yusrah.…..”
“No Aymah karki sake cewa komai dan ALLAH. Mu ajiye wannan maganar haka kawai. Ku tashima muje dan ga kamar momy can ta fito”.
      Badan Nu'aymah taso ba tai shiru.

  A falo kam zaman Adawiya babu jimawa Abba da Yoohan suka shigo falon Omar biye da su. Ɗago kanta tayi da nufin yima Abba sannu idanunta ya sauka akan Yoohan da shi koma kallon inda take baiyi ba. Ganin har zasu wuce batai magana ba Abbah yace, “Adawiya baki iya gaisuwa ba ne? Ko bakiga mijin ƴar uwarkiba Nu'aymah?”.
       Da gaske gaban Adawiya sai da ya faɗi. Bakinta na rawa ta gaida Yoohan. Sau ɗaya ya amsa tare da mata kallo ɗaya ya ɗauke kansa. Binsa da kallo kuwa ta cigaba da yi harya shige falon Abbah.
       A fili tace, ‘Dama Aymah ba ƙabila akace ta aura ba? Naga kuma balarabe?’. Bata da mai bata wannan amsar dan haka tai shiru tana saƙe-saƙenta a cikin zuciya har Momy ta fito tana tambayarta ihun mi takeji ɗazun. Tana cikin sanar ma Momyn ne su Aymah suka fito. Zuwa Nu'aymah tai ta rungume Momy cike da murna.
       Momy dake dariya tace, “Ja'ira, an girma ba'asan an girma ba”.
         Dariya ta sakeyi su Amal na taya ta. Adawiya dai tai muƙuy kamar bata falon abin duniya ya gama isarta a rai game da ganin mijin Nu'aymah..
          Tura Amal momy tayi ta kira Uwaliya mai aikin da aka kawoma Nu'aymah daga kano. Ashe dama ita suka biyo ɗauka batare da Yoohan ya sanar mata ba. Ba wata tsohuwa bace ba. Zata iya kai kimanin shekaru talatin da bakwai dai. Sun gaisa da Nu'aymah momy tai musu bayanin juna. Har cikin zuciya Aymah taji son zama da Uwaliya kuwa. Dan haka cikin jin daɗi ta miƙe domin zuwa falon Abbah ta gaidashi shima.

          Basu bar gidanba sai goma saura. Sun tafi da Uwaliya. Su Amal ma sun mata alƙawarin zuwa next week dan dama Abbah ne ya hanasu wai karsuje su tada mata hankali. Amma yanzu daya ganta babu wata damuwa yace zai barsu suje ɗin amma sai weekend insha ALLAH.
          Papa kawai suka samu a harabar gidan zaune. Sai su Solomon da suma ke tasu hirar acan gehe. Ita dai tana gaida papan ciki suka wuce da Uwaliya. Shi kuma ya nufi inda papan yake zaune.
         Basu sami kowa a falon ba. Gidan ma shiru alamar duk sun kwanta. Ta fahimci ɗabi'arsu ce barcin wuri, musamman ma yaran saboda makaranta. Da kuma su ɗin kansu daya kasance duk suna fita aiki da safe. Uwaliya nata kalle-kalle ita dai har suka ƙarasa sashensu. Sarai Aymah taga Momy acan ƙofar sashenta zaune. Amma sai tai kamar bata ganta ba suka shige abinsu.
        A falo suka yada zango. Kusan zaman mintuna ashirin sai gashi ya shigo tare da su Solomon da suka kwaso kayan. Anan tsakkiyar falon duk suka zube komai suka fita suna musu sai da safe.
      Batare da Yoohan ya zauna ba ya dubi Aymah yana faɗin, “Ki kaita ɗakin kusa da sashen nan anan zata zauna”. Kamar Aymah zatai magana sai kuma tai shiru ganin ya juya abinsa ya nufi hanyar ɗakinsa. Ta fahimci har yanzu ransa a ɓace yake dai, kamarma an sake tunzurashi ne yanzu da suka shigo. Tashi tai ta raka Uwaliya ɗin, ɗakine babba da katifa a ciki da kwabbot na kaya da toilet ɗinsa kamar kowane ɗaki. Hakan yasa hankali Aymah kwanciya. Itama Uwaliya sai faman washe haƙora takeyi ganin ita da aka kawo tai aiki amma irin wannan aljannar duniya haka.

_________★★★★_________

              Washe gari da yamma tana ɗakinta bisa gado ta baje littatafan ta na islamiyya tana dubawa ya shigo. Batare data ɗago ba ta amsa masa sallamar da yayi. Sai da ya zauna a bakin gadon tare da ɗaukar littafin gabanta na SAHIH AL-BUKHARI da take dubawa sannan ta ɗago.
      Idanu ta ɗan zaro tana kallon abinda ya ke ci. Ta tsuke fuska iya gaskiyarta tana faɗin, “Tab wannan ai chocolate ɗina ce, naga kaine kace kowa yaci abinda ya sayo ai ɗazun da safe ko?”.
          “Oh ashe babu daɗi hajjaju, ni da kika tasamin biscuits a gaba kika cinye banyi maganaba, sai ni danna sha wannan chocolate ɗin da ko wani daɗi babu”.
       Ture buks ɗin tai gefe ta miƙa hannu zata warce a hannunsa. “Tunda babu daɗi bani abuta”.
        Hannun ya riƙe yana wani kafeta da narkakkun idanunsa. Yayinda yake ɗan motsa bakinsa a hankali yana cinye wadda ya gutsira. Ƙara matsowa tai tasa ɗayan hannun zata warce again, dai-dai zai kai bakinsa.
      Fisgota yay gaba ɗayanta ta faɗa jikinsa. Yay baya shima suka faɗa saman gadon. Zabura tai tana faɗin, “Malam kana shigarmin hanci da yawa wl......”
        Bai bari ta ƙarasa ba ya juyata ta koma ƙasa shi ya koma sama. Sai dai rabin jikinsa ne a kanta, a hakanma bai sakar mata nauyinsa ba dan a ganinsa bazata iya ɗauka ba. Amma tsabar ragwantaka na Aymah sai ta wage baki zata masa ihu. Hannu yay saurin ɗorawa akan bakin nata yana ɗan waro idanunsa waje. “Idan kikai ihun nan na ratse sai na haɗiye bakin kinnan yanzun nan”.
         Hannu tasa ta ture nasa hannun tana faɗin, “Tunda kai maye ne basai ka haɗiye ba mugani”.
       “Kema zaki koma mayyar ai”
Yay maganar yana saka idanunsa cikin nata yanda ta kasa magana ta kuma kasa janye nata idanun saboda tsabar yanda ya sarƙeta da nashi.
        Cikin wata irin kasalalliyar murya yace, “In sammiki chocolate ɗin?”.
       Duk yanda taso buɗe baki tayi magana ta kasa. Dan yanda yay maganar gab da fuskarta, ga idanunsa cikin nata sai taji kamar ya mata wani ɗaurine da igiyoyi.
          Chocolate ɗin ya kai bakinsa ya sake gutsira kaɗan, har yanzu idanunsa na a cikin nata bai janye ba. Ya sake matsar da bakinsa gab da nata. A hankali cikin maganar raɗa yace, “Buɗe bakin”.
       Kamar wadda ake juyawa da remote Aymah ta motsa laɓɓanta kaɗan idanunta dake cikin nasa na cikowa da ƙwalla. Bata ankara ba taji laɓɓansa akan nata, a tare suka lumshe idanu, sai dai ita wasu hawaye da batasan na minene ba suka shiga silalo mata saman kumatu da gudu. Yayin shi kuwa Yoohan yake juye mata narkakkiyar chocolate ɗin daya narkar da yawunsa......

    (Kai zafafa fans wannan bada cakuleti na Yoohan yafi ƙarfina, bara naɗan fita na barsu su sarara😱. Amma zan leƙa muku ta kafar mukkuli🏃).
Chapter 126 · 0% Book details