Sashe 134
Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A ciki kuwa, tun a ihun farko da Aymah tayi Gebrail ya ruɗe. Yay saurin sakinta daga rungumar da yay mata jikinsa na ɓari. Faɗuwar da tayi a kan hannunta ne yasata sake ƙwalla ƙara ta buyu a take ta sanƙame a sume.
Da lalube ya buɗe ƙofar ya fito, kirif ya kife ƙasa a cikin falon. Goshinsa ne ya bugi tiles sai ga jini. Bai damu ba, ya miƙe da sauri zuciyarsa kamar zata zubo ƙasa saboda firgici da tashin hankali. Ya kai hannu ya murza key ɗin data sakama ƙofar falon, zai buɗe ƙofar kenan aka turo. Da sauri ya koma bayan ƙofar ya maƙale fitsari na zubo masa a jiki dan jin ƙamshin turaren Yoohan, hannu yasa ya danne bakinsa da sauri.
Kasancewar Yoohan a rikice ya ke hankalinsa bai kai ga Gebrail ba, ɗakin Nu'aymah kawai ya tasarmawa yana ƙwala kiran “Zeeynab! Zeeynab!! Where are you?!”.
Da wannan damar Gebrail ya fita a guje zuwa ɗakinsa hannunsa tare da goshinsa dake zubda jini. Akan idanun Uwaliya dake shirin fitowa daga ɗakinta Gebrail ya fito daga sashen Aymah. Sun dawo suma babu jimawa. Sai dai ganin lokacin salla na ƙara wuceta ya sata nufar ɗakinta da nufin sai tayi sallar sannan taje ta sanarma Aymah sun dawo. Blessing kuwa tana can backyard tana tattaro shanyar da tayi kafin su fita. Ihun Aymah kawai taji hakan yasa suka shigo falon kusan a tare da su momy da suka dawo church.
Gaba ɗaya Yoohan yama rikice, ya rasa miya kamata yayi saboda ganin duhu a ɗakin Nu'aymah daya shiga. Da ƙyar ya iya lalubar makunnar fitila ya kunna. Ganinta yashe a ƙasa ya sakashi zabura kanta yana sake ƙwala mata kira da wata irin razananniyar murya data sake rikita su Momy Destiny da ke shigowa sashen.
Gaba ɗayanta ya ɗago zuwa jikinsa, ya sakata a ƙirjinsa yana bubbuga fuskarta da cigaba da kiran sunanta. Fahimtar da yay numfashinta yayi nisa sosai ya sakashi miƙewa da ita gaba ɗaya zuwa gado. Su dai su Momy sunyi cirko-cirko kowa yana tambayar kansa miya sameta?. Babu mai basu amsa, dan haka suka cigaba da kallonsa.
Shimfiɗeta yay a gadon ya shiga murza tafin hannunta. Sai kuma ya koma ƙafafunta. Babu dai alamar zata motsa. Kansa ya dafe yana ambaton sunan ALLAH. Ya kai tsahon seconds sha biyar kafin ya koma ƙasa gaban gadon ya durƙusa saitin fuskarta. Bakinsa ya ɗora saman nata ya toshe mata hanci da yatsunsa biyu ya shiga jawo numfashinta cike da dabararsu ta likitoci. Kusan tsahon seconds ashirin kafin ta kawo wani irin dogon numfashi tare da zabura ta saki wahalalliyar ƙara saboda sakin mata baki da yayi.
Zabura tai ta haye jikinsa dan ya dawo bakin gadon ya zauna yana sauke ajiyar zuciyar jin daɗin ganin ta farfaɗo. Ta ƙanƙamesa tana faɗin, “Duhu Umm. Banason duhu ki samun fitila. Umm ki kiramin Abbana banason duhu Yaya Yoohannnnn!!”.
Idanu Yoohan ya lumshe a hankali saboda jin yanda taja sunansa akan harshenta, ya saka duka hannayensa ya rungumeta a jikinsa da ƙyau dan jikinta wani irin karkarwa yakeyi. A haka ya ɗora bakinsa saman kunnenta ya shiga hura mata iska a ciki. Hannayensa kuwa na shafa bayanta. A hankali ta fara sassauta surutan da takeyi, rawar jikinta na raguwa. Sai kuma ta koma sauke ajiyar zuciya hawayenta dake fita masu ɗumi na saukar masa a ƙirji.
A haka ta sake sumewa, Hankalinsane ya tashi da wannan sumar, dan sumace da yake da tabbacin mai haɗarice a gareta. sai ji yay ta masa nauyi kawai. Ajiyar zuciya ya sake saukewa a karo na babu adadi, hankalinsa na ƙara afkawa cikin ƙololuwar damuwa. Ya buɗe idanunsa da suka rine da ja yana kallo ahanlinsa dake zagaye da su a cikin ɗakin. Baice komai ba, dan bayason susan komai ɗin, sai kwantar da ita da yayi a hankali yaja bargo ya rufa mata, tare da ɗaukar remote ɗin ac dake a durowar gefen gadon a ajiye ya ƙara gudunsa saboda sanyin da yasan tafi buƙata a yanzun.
Sake maida hankalinsa yay gasu Momy yana musu alamar suje waje. Babu wanda yace komai duk suka fara fitowa shima ya biyo bayansu yaja ƙofar ya rufe mata dan dolene yaje ya nema mafita.
Dukansu babu wanda baibi jinin Gebrail daya fasa kai ba da kallo. Yoohan da yay ƙarshen fitowa ya jinjina kansa kawai yana kallon jinin da tunani barkatai a ransa.
Momy Favour ce ta fara faɗin, “Wai miya sameta ne haka John?”.
Kansa ya girgiza. Muryarsa na nuna alamun damuwa yace, “Aunt ban saniba nima. Ihunta kawai naji dai-dai muna shigowa gidan nan. Sai dai da alama wanine ya shigo ya tsoratata da duhu dan batason ganin duhu”.
Kallon-kallo suka shigayi a tsakaninsu. Momy tace, “Amma babu kowa a gidan nan sai ita da su Blessing. Dan muma shigowarmu kenan daga church muke. Joy da Gebrail suna school. Miracle kuma bata dawo daga wajen aiki ba har yanzu da alama”.
Batare da Yoohan yace wani abuba ya dubi Blessing da Uwaliya. Cikin sauri Blessing tace, “No Sir. na rantse da ALLAH muna bamusan miya sameta ba. Dan bamufi 5minutes da shigowaba mukaji ihunta. Ni inama backyard ina kwashe kayan dana shanya danai wanki ɗazun. Uwaliya kuwa tacemin zataje tai salla sai dai ban saniba ko.......”
“Wlhy nima salla na shigayi banje wajentaba saboda ganin zan makara”. Uwaliya tai saurin tarar numfashin Blessing ɗin.
Hannu Yoohan yasa a goshinsa yana ɗan murzawa. Sai kuma ya furzar da huci mai zafi. Batare da ya sake magana ba ya nufi ɗakinsa kawai.
Suma duk jan ƙafafu sukai gwiwa a sage suka fita harsu mama debora da suka gaza cewa komai. Su Victoria kam dama sunsan idan Yoohan na magana da iyayensu baya buƙatar cewarsu, shiyyasa basu tofa ko ‘A’ ba a maganar. Daka gansu dai kasan tausayin Nu'aymah ya cika musu zukata.
Kowa ɗakinsa ya nufa, sai dai Momy na shiga nata taci karo da Gebrail cikin toilet yana leƙo kansa. Yanajin motsin za'a buɗe kofa yay saurin komawa zai rufe ƙofar. Da sauri momy tace, “Kai waye anan?”.
Jin muryar momynsa ne ya sakashi fitowa jikinsa na rawa. Yay saurin faɗin, “Momy shiii!! Karkiyi magana Please”.
Sosai gabanta ya faɗi ganin yanda jikinsa ke ɓari. Ga jini ya jiƙe handkerchief ɗin daya ɗora a goshinsa inda yaji ciwo garin gudu. Saurin ruƙo masa hannu tayi suka koma cikin toilet ɗin itama nata jikin yana rawa. Ta maida ƙofar ta rufe tana magana a matuƙar tashin hankali. “Gebrail! Badai kaine ka aikata ba?”.
Hawaye na zuba masa a idanu jikinsa na karkarwa yace, “Momy idan Brother John yasan nine kasheni zaiyi. Na rantse tsautsayine momy kuma ban mata komai ba. Na rungumeta ne kawai na kashe wutar ɗakin shine tamin ihu”.
Kai momy ta dafe tana faɗin “Oh my lord”. Sai kuma ta kama kafaɗun Gebrail ta shiga girgizawa. “Gebrail baka da hankali. matar John? Bayan kasan halinsa a gidan nan”.
“Momy na rantse tsautsayi ne, ina sonta da gaba ɗaya zuciyata. Amma nasan Brother Yoohan zai halakani idan ya sani, kasheni zaiyi da hannunsa momy, ki taimakeni karki bari ya gane nine momy”.
Kuka yake sosai jikinsa na karkarwa. Jansa tayi jikinsa ta rungume duk da itama harga ALLAH a mugun tsoracen take. Dan tasan shirun da Yoohan yayi tabbas bazai zama na banza ba. Sai da taji bugun zuciyar Gebrail yaɗan dai-daita sannan ta ciresa a jikinta ta zaunar akan bathtub. Fita tai ta ɗakko First aid box ta dawo toilet ɗin bayan ta murzama ƙofar bedroom ɗinta key. Zuwa tai tai masa dressing wajen. Ta miƙe tana faɗin, “Kayi wanka zanje na ɗakko maka kaya a ɗakinka, dolene kabar gidanann a daren nan Gebrail. Kaje ka kama hotel koka koma cikin hostel ɗin makarantarku har sai wannan ciwon da kaji ya warke. Inba hakaba sai Yoohan ya gano kaine dan kowa yaga jinin daka zubar a sashen. Ka kuma san shi mutumne mai tsanani basira akan duk abinda ya ƙwafa”.
Kansa ya ɗaga mata yana faɗin, “Thanks you momy, thanks you so much”.
Bata sake cemasa komaiba ta fita tana tunanin yanda zata shiga ɗakinsa ta ɗakko kayan cikin dabara ba tare da kowa ya fahimta ba.
★★★★
Da lalube ya buɗe ƙofar ya fito, kirif ya kife ƙasa a cikin falon. Goshinsa ne ya bugi tiles sai ga jini. Bai damu ba, ya miƙe da sauri zuciyarsa kamar zata zubo ƙasa saboda firgici da tashin hankali. Ya kai hannu ya murza key ɗin data sakama ƙofar falon, zai buɗe ƙofar kenan aka turo. Da sauri ya koma bayan ƙofar ya maƙale fitsari na zubo masa a jiki dan jin ƙamshin turaren Yoohan, hannu yasa ya danne bakinsa da sauri.
Kasancewar Yoohan a rikice ya ke hankalinsa bai kai ga Gebrail ba, ɗakin Nu'aymah kawai ya tasarmawa yana ƙwala kiran “Zeeynab! Zeeynab!! Where are you?!”.
Da wannan damar Gebrail ya fita a guje zuwa ɗakinsa hannunsa tare da goshinsa dake zubda jini. Akan idanun Uwaliya dake shirin fitowa daga ɗakinta Gebrail ya fito daga sashen Aymah. Sun dawo suma babu jimawa. Sai dai ganin lokacin salla na ƙara wuceta ya sata nufar ɗakinta da nufin sai tayi sallar sannan taje ta sanarma Aymah sun dawo. Blessing kuwa tana can backyard tana tattaro shanyar da tayi kafin su fita. Ihun Aymah kawai taji hakan yasa suka shigo falon kusan a tare da su momy da suka dawo church.
Gaba ɗaya Yoohan yama rikice, ya rasa miya kamata yayi saboda ganin duhu a ɗakin Nu'aymah daya shiga. Da ƙyar ya iya lalubar makunnar fitila ya kunna. Ganinta yashe a ƙasa ya sakashi zabura kanta yana sake ƙwala mata kira da wata irin razananniyar murya data sake rikita su Momy Destiny da ke shigowa sashen.
Gaba ɗayanta ya ɗago zuwa jikinsa, ya sakata a ƙirjinsa yana bubbuga fuskarta da cigaba da kiran sunanta. Fahimtar da yay numfashinta yayi nisa sosai ya sakashi miƙewa da ita gaba ɗaya zuwa gado. Su dai su Momy sunyi cirko-cirko kowa yana tambayar kansa miya sameta?. Babu mai basu amsa, dan haka suka cigaba da kallonsa.
Shimfiɗeta yay a gadon ya shiga murza tafin hannunta. Sai kuma ya koma ƙafafunta. Babu dai alamar zata motsa. Kansa ya dafe yana ambaton sunan ALLAH. Ya kai tsahon seconds sha biyar kafin ya koma ƙasa gaban gadon ya durƙusa saitin fuskarta. Bakinsa ya ɗora saman nata ya toshe mata hanci da yatsunsa biyu ya shiga jawo numfashinta cike da dabararsu ta likitoci. Kusan tsahon seconds ashirin kafin ta kawo wani irin dogon numfashi tare da zabura ta saki wahalalliyar ƙara saboda sakin mata baki da yayi.
Zabura tai ta haye jikinsa dan ya dawo bakin gadon ya zauna yana sauke ajiyar zuciyar jin daɗin ganin ta farfaɗo. Ta ƙanƙamesa tana faɗin, “Duhu Umm. Banason duhu ki samun fitila. Umm ki kiramin Abbana banason duhu Yaya Yoohannnnn!!”.
Idanu Yoohan ya lumshe a hankali saboda jin yanda taja sunansa akan harshenta, ya saka duka hannayensa ya rungumeta a jikinsa da ƙyau dan jikinta wani irin karkarwa yakeyi. A haka ya ɗora bakinsa saman kunnenta ya shiga hura mata iska a ciki. Hannayensa kuwa na shafa bayanta. A hankali ta fara sassauta surutan da takeyi, rawar jikinta na raguwa. Sai kuma ta koma sauke ajiyar zuciya hawayenta dake fita masu ɗumi na saukar masa a ƙirji.
A haka ta sake sumewa, Hankalinsane ya tashi da wannan sumar, dan sumace da yake da tabbacin mai haɗarice a gareta. sai ji yay ta masa nauyi kawai. Ajiyar zuciya ya sake saukewa a karo na babu adadi, hankalinsa na ƙara afkawa cikin ƙololuwar damuwa. Ya buɗe idanunsa da suka rine da ja yana kallo ahanlinsa dake zagaye da su a cikin ɗakin. Baice komai ba, dan bayason susan komai ɗin, sai kwantar da ita da yayi a hankali yaja bargo ya rufa mata, tare da ɗaukar remote ɗin ac dake a durowar gefen gadon a ajiye ya ƙara gudunsa saboda sanyin da yasan tafi buƙata a yanzun.
Sake maida hankalinsa yay gasu Momy yana musu alamar suje waje. Babu wanda yace komai duk suka fara fitowa shima ya biyo bayansu yaja ƙofar ya rufe mata dan dolene yaje ya nema mafita.
Dukansu babu wanda baibi jinin Gebrail daya fasa kai ba da kallo. Yoohan da yay ƙarshen fitowa ya jinjina kansa kawai yana kallon jinin da tunani barkatai a ransa.
Momy Favour ce ta fara faɗin, “Wai miya sameta ne haka John?”.
Kansa ya girgiza. Muryarsa na nuna alamun damuwa yace, “Aunt ban saniba nima. Ihunta kawai naji dai-dai muna shigowa gidan nan. Sai dai da alama wanine ya shigo ya tsoratata da duhu dan batason ganin duhu”.
Kallon-kallo suka shigayi a tsakaninsu. Momy tace, “Amma babu kowa a gidan nan sai ita da su Blessing. Dan muma shigowarmu kenan daga church muke. Joy da Gebrail suna school. Miracle kuma bata dawo daga wajen aiki ba har yanzu da alama”.
Batare da Yoohan yace wani abuba ya dubi Blessing da Uwaliya. Cikin sauri Blessing tace, “No Sir. na rantse da ALLAH muna bamusan miya sameta ba. Dan bamufi 5minutes da shigowaba mukaji ihunta. Ni inama backyard ina kwashe kayan dana shanya danai wanki ɗazun. Uwaliya kuwa tacemin zataje tai salla sai dai ban saniba ko.......”
“Wlhy nima salla na shigayi banje wajentaba saboda ganin zan makara”. Uwaliya tai saurin tarar numfashin Blessing ɗin.
Hannu Yoohan yasa a goshinsa yana ɗan murzawa. Sai kuma ya furzar da huci mai zafi. Batare da ya sake magana ba ya nufi ɗakinsa kawai.
Suma duk jan ƙafafu sukai gwiwa a sage suka fita harsu mama debora da suka gaza cewa komai. Su Victoria kam dama sunsan idan Yoohan na magana da iyayensu baya buƙatar cewarsu, shiyyasa basu tofa ko ‘A’ ba a maganar. Daka gansu dai kasan tausayin Nu'aymah ya cika musu zukata.
Kowa ɗakinsa ya nufa, sai dai Momy na shiga nata taci karo da Gebrail cikin toilet yana leƙo kansa. Yanajin motsin za'a buɗe kofa yay saurin komawa zai rufe ƙofar. Da sauri momy tace, “Kai waye anan?”.
Jin muryar momynsa ne ya sakashi fitowa jikinsa na rawa. Yay saurin faɗin, “Momy shiii!! Karkiyi magana Please”.
Sosai gabanta ya faɗi ganin yanda jikinsa ke ɓari. Ga jini ya jiƙe handkerchief ɗin daya ɗora a goshinsa inda yaji ciwo garin gudu. Saurin ruƙo masa hannu tayi suka koma cikin toilet ɗin itama nata jikin yana rawa. Ta maida ƙofar ta rufe tana magana a matuƙar tashin hankali. “Gebrail! Badai kaine ka aikata ba?”.
Hawaye na zuba masa a idanu jikinsa na karkarwa yace, “Momy idan Brother John yasan nine kasheni zaiyi. Na rantse tsautsayine momy kuma ban mata komai ba. Na rungumeta ne kawai na kashe wutar ɗakin shine tamin ihu”.
Kai momy ta dafe tana faɗin “Oh my lord”. Sai kuma ta kama kafaɗun Gebrail ta shiga girgizawa. “Gebrail baka da hankali. matar John? Bayan kasan halinsa a gidan nan”.
“Momy na rantse tsautsayi ne, ina sonta da gaba ɗaya zuciyata. Amma nasan Brother Yoohan zai halakani idan ya sani, kasheni zaiyi da hannunsa momy, ki taimakeni karki bari ya gane nine momy”.
Kuka yake sosai jikinsa na karkarwa. Jansa tayi jikinsa ta rungume duk da itama harga ALLAH a mugun tsoracen take. Dan tasan shirun da Yoohan yayi tabbas bazai zama na banza ba. Sai da taji bugun zuciyar Gebrail yaɗan dai-daita sannan ta ciresa a jikinta ta zaunar akan bathtub. Fita tai ta ɗakko First aid box ta dawo toilet ɗin bayan ta murzama ƙofar bedroom ɗinta key. Zuwa tai tai masa dressing wajen. Ta miƙe tana faɗin, “Kayi wanka zanje na ɗakko maka kaya a ɗakinka, dolene kabar gidanann a daren nan Gebrail. Kaje ka kama hotel koka koma cikin hostel ɗin makarantarku har sai wannan ciwon da kaji ya warke. Inba hakaba sai Yoohan ya gano kaine dan kowa yaga jinin daka zubar a sashen. Ka kuma san shi mutumne mai tsanani basira akan duk abinda ya ƙwafa”.
Kansa ya ɗaga mata yana faɗin, “Thanks you momy, thanks you so much”.
Bata sake cemasa komaiba ta fita tana tunanin yanda zata shiga ɗakinsa ta ɗakko kayan cikin dabara ba tare da kowa ya fahimta ba.
★★★★