← Book details Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 156 OF 211

Sashe 156

Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

............Ganin lokacin salla zai wuce ya sakashi mata knocking dan taƙi fitowa. “Sorry baby fito muyi salla kinga munata makara. Na yarda idan mun idar ki hukuntani koda bulalane ok”.
         Fitowa tayi, dan itama batason lokacin sallar ya wuce, dama ta sake  shiga ruwan zafi ne dan tanajin daɗinsa sosai. Ƙin yarda ta kalli inda yake tayi. Taje ta saka doguwar riga, shi kuma ya saka musu abin salla. Suna raka'a ta biyu Richard ya shigo ɗakin bayan yayi knocking yaji shiru. A zatonsa ko jikin nasu ne shiyyasa ya shigo abinsa. A hankali ya ajiye kayan hannunsa idanunsa a kansu. Tsigar jikinsa sai tashi take. Haka ya zauna yanata kallonsu tamkar ya samu television har suka idar. Ajiyar zuciya ya sauke lokacin da Yoohan ya zubo masa harara. Da yare yace, “Shine bazaka jira a baka izinin shigowa ba zaka wani faɗoma mutane ɗaki?”. Jikin Richard duk a sanyaye yake, shiyyasa yace, “I'm sorry” kawai yana furzar da iska. Kauda kai Yoohan yayi ya maida ga Aymah dake jinsu sai dai ko ɗago kai batayiba dan itama shigowar Rich ɗin ta bata haushi. Dan tarbiyyarta ta koya mata shiga waje da sallama da kuma jiran bada dama. Yoohan ya fahimci shigowar Rich ta bata haushi. Dan aɗan zamansu ya fara fahimtar wasu daga halayenta. A hankali yace, “Kiyi haƙuri. Sai kin taimakeni wajen ceto rayuwar ɗan uwana da ga duhu zuwa haske”.
      Karan farko ta ɗago kai ta ɗan kallesa. sai kuma tai ajiyar zuciya da maida dubanta inda Rich yake zaune. Sai dai ba kallonsu yakeba yanzun. “Good Afternoon”. Ta faɗa da dasashshiyar muryarta datasha kuka.
     Miƙewa Yoohan yayi yana faɗin, “Ana gaisheka”.
        Buɗe idanu Rich yayi yana kallonta, ya amsa cike da kulawa da tambayarta ƙarfin jiki. A taƙaice tace, Am better now”.
         “Thanks God”. Ya faɗa shima yana miƙewa.  Fita yay ƴar barandar nan ya zauna, yayinda Yoohan kuma ya zauna inda ya tashi yana kiranta. Batare data tankaba ta miƙe ta nufesa. Gefensa ya nuna mata yana binta da kallo. Ita dai taƙi kallonsa sam. Abincin da Rich ya kawo musu ya buɗe. Gasashshen naman kaza ne da yasa akayisa na musamman domin Nu'aymah, sai haɗin salad da sauran tarkacen abincin Austrian daba gama haddace sunayensu tai ba itakam. Kamo hannunta yay ya matso da ita sosai jikinsa yana magana cike da lallashi.
      “Ki daure kici wannan bakinki zaiyi daɗi sosai. Kuma zaki samu sauƙi insha ALLAH. Dan abincine da ya dace da buƙatar irin yanayin da kike ciki ok”.
       Idanunta cike da ƙwalla tace, “Toni bakina fa babu daɗi ALLAH”.
       “Eh idan kikaci wannan zai miki daɗi, idan kuma kinason na miki allura tom, ina dasu buhu-buhu a ɗakin nan. Ohya buɗe bakin”. Hawayen da take maƙalewa ne suka silalo, jin zancen allura ya sakata buɗe baki ya saka mata. Share mata ya shigayi yana faɗin, “Kefa yanzun babban mace ne, kin girmi harkar yara. Kona tayaki ci ne?”.
     Da sauri ta ɗaga masa kanta alamar eh.
    Yace, “Okay to dinga bani da kanki muyi maza mu mucinye kinga Rich yana jirana”. Babu musu ta dinga bashi shima yana bata. sai ko gashi sun cinye kazar tas harma suka ƙara da wani abun. Yana son ɗaukar allurar da Richard ɗin ya kawo amma bayason ɗaga mata hankali. Hakan ya sakashi ɗaukar ledar yabar wajen. Bata fahimci mizaiyi ba shiyyasa bata maida hankali kansa ba. Sai tattare kayan da sukaci abincin take.
       Batare data san mi yayoba yazo ya sake zama kusa da ita. Kallonsa tayi sau ɗaya ta janye idonta tana tura baki. “Ba kace jiranka akeba”.
        Wuyansa ya shafo yana gyaɗa mata kai. “Magani zansha sannan. Ɗakko min gasu can”. Kamar zata fasa masa kuka ta miƙe inda ledan maganin yake. Batason yin tafiya saboda zafin da takeji. Da kallo ya bita harta ɗakko ta juyo sannan ya janye idonsa.
         Ledar data miƙo masa ya haɗa d hannunta gaba ɗaya ya jawota saman cinyarsa. kafin ta sami damar yin magana ya manne bakinsa da nata tare da saita allurar dake ɓoye cikin ɗayan hannunsa a inda ya dace. Tanajin shigar allurar ta nema fisge jikinta daya fara rawa dan abin yazo mata a bazata. Ya rumtse idanunsa da sauri saboda wani shegen mintsini datake masa a hannunsa. Allurar ya zare tare da bakinsa yana faɗin, “Ouch!!. sweet girl Zaki fasamin fata”.
        Lafewa tai a jikinsa tana sauke ajiyar zuciya a jajjere da shashshekar kuka mara sauti. Ga hawaye na zirara. Goshinta ya sumbata yana ɗan murmushi. Am sorry bazan ƙaraba huyim?”.
      Ita dai bata tankaba. Tanata hawayenta ne. Cigaba yay da shafa bayanta har sai da ta daina kukan sannan ya sauketa a kujerar, a gabanta ya durƙusa hannunta cikin nasa. Ya share mata hawayen da ɗayan hannun, a ransa yana dariyar rakinta akan allura. Sai da ya tabbatar ta samu nutsuwa yanda ya kamata sannan ya duƙo ya sumbaci kumatunta da bakinta. “Bara inje inazuwa. Insha ALLAH wajen zai daina zafi kinji”.
      Batace komaiba. Amma yasan tana jinsa. Ya sake sumbatar laɓɓanta sannan ya miƙe. da kallo tabi bayansa harya fice ƴar barandar nan. Sai ta maida idanun ta lumshe duk da ba barci takejiba kuwa.

       ★★★
Chapter 156 · 0% Book details