Sashe 169
Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Cikin mintuna ƙalilan sai ga Dawood ya dawo tare da matashiyar mace da bazata gaza shekaru talatin da biyu zuwa da uku ba. Daka ganta babu tambaya kasan jinin Boss Jawaad Abdul-aziz ce. Sanye take cikin wando da riga na Uniform ɗin hukumar. Da alama itama jami'ace a hukuma (dan ƙari. Bilkisu ƴar bilkisu jikar bilkisu kenan😉. Ita ƴar sanda, mamanrta ƴar sanda. Babanta ɗan sanda😝. Wani aiki sai Jay😂lol).
Fuskarta cike da miskilancin data gada wajen iyayenta ta ƙame tare da salute ɗin mahaifinta kuma oganta a wajen aiki. tace, “Sir gani”.
Daga Yoohan har Omar kallon mamaki suke mata. Dan basa buƙatar ƙarin bayanin komai game da Biljay.
Takardar da Dawood ya rubuta ya miƙa mata cike da bada umarni a gareta matsayin oga ba mahaifiba. “Duba min wannan takardar”.
“Okay sir” ta faɗa tana ɗaukar takardar. Cike da hazaƙar ƙwarewar aiki ta duba rubutun takardar tsaf, kafi. ta ɗago ta kallesa tana sunkuyar da kanta da ƙamewa. “Na duba Sir”.
“Me kika fahimta?”.
“Report ne na case ɗin ɓoyayyun mutane masu laifi”.
“Masha ALLAH. Little bee kece zakiyi wannan aikin. Waɗanan sune masu kawo Report ɗin. Zakiyi joining ɗinsu kuyi aikin tare. Sai dai kece zakiyi kutse a cikin gidan ko mubi ta wata hanyar insha ALLAH. Kinsan banson wasa, bana son kuskuren ganganci akan aiki, so be careful”.
“Insha ALLAH sir”.
Kai ya jinjina mata da maida dubansa kan Dawood. “Dawood tare zakuyi wannan aiki da ita, so zata kasance ƙarƙashin control ɗinka, dukanku kuma zaku kasance akan umarni”.
Shima ya amsa da “Okay sir”.
Daga haka Jay ya maida dubansa gasu Yoohan. “Doctors waɗanan nan sune zasu taimaka muku akan wannan case. Insha ALLAH daga nan zuwa kwana uku zamu san wadda zata shiga cikin gidan matsayin maiyin hutu a wajen Sheikh. Sauran aiki duk zasu yisa baku da damuwa. Sai dai dole kuma sai da hannunku a ciki dan kun fisu sanin sirrin gidan a yanzun. Zaka haɗata ƙawance da matarka ta waya. Dan wasu abubuwan ta hanyartane zasu sami haske sosai. Duk abinda ya dace zaku cigaba da ji ta hanyar Dawood, dan shine oganta”.
Godiya sosai su Yoohan suka shiga yimasa. Dan sam basuyi tunanin samun mafita cikin sauƙiba haka daga garesa oga kwatakwata da ganinsama ke da matuƙar wahala. Yanda bai musu bayani akan matsayin Bilkisu a garesaba suma basu tambayaba duk da sunada buƙatar ji.
A tare da shi suka fito office zuwa massalaci saboda kiran sallar zuhur. Bayan an idar da salla kuma sukai masa sallama da ƙarin godiya suka wuce cike da farin cikin wannan karamci da samun sauƙi. Sai dai ƙasan ran Yoohan shi kaɗai yasan mi yakeji game da Jay ɗin.
Koda suka ɗauki hanya kasa haƙuri Omar yayi sai da yayima Yoohan maganar kallon da yaga Jay ɗin na masa da matarsa. Harma hanata maganar da yayi. Tare da cewa nifa, “Wlhy fisgen kamannima kukaimin”.
Da mamaki Yoohan yace, “Kamanni kuma?”.
“Yes X-man. Wlhy a fisge kunyi kamanni like na jini haka”.
Nannauyan numfashi kawai Yoohan yaja da ƙarfi ya fesar batare da ya iya cewa komaiba har suka ƙarasa wani gidan cin abinci. Anan sukai lunch da cigaba da tattaunawa akan abinda ya shafesu. Daga haka sukawuce General hospital wajen Dr Shikurah. Sai dai sunyi rashin sa'ar samunta wai batama ƙasar.
Yoohan yayi gaisuwa da abokan arziƙi suka koma hotel ɗin daya sauka. Omar ya jima a wajensa dan har dare suna a tare sannan ya koma gidan papa dan acan ya sauka shi. Amma sai bai faɗama kowa Yoohan na ƙasarba.
Washe gari Yoohan yaje kaduna yin wani aiki. Sai washe garin daya cika kwana uku a 9ja ya dawo. Dai-dai da ranar da Little bee zata shiga gidan baba malam kenan. Dan haka kai tsaye gidansu ya nufa. Sai dai kawai su Madam Chioma suka gansa tsilum tamkar daren Christmas inji su.
___________★★
Tun wucewar su Yoohan Jay ya kasa zaune ya kasa tsaye a office ɗinsa. Gaba ɗaya man kan sa ya gama tsiyayewa tas akan wannan kamanni. Goshinsa ya murza da cewa, ‘Kai anya kuwa. Dolene nasan wanene wannan yaron’. Ya ƙare maganar da ɗaukar telephone yay kiran Dawood.
Dandanan Dawood ya amsa kiran boss. Nuna masa kujera yayi alamar ya zauna. Bayan kusan mintuna uku ya ture files ɗin gabansa yana kallon Dawood ɗin.
“Dawood nikam a ina kasan yaron nan ne?”.
Cike da girmamawa ya bashi amsa da faɗin, “Sir, tare mukai secondary school da su”.
“Masha ALLAH, lallai kayi masa sani na sosai. Anan cikin abuja suke?”.
“Yes sir. Ai yaron sanannen Pastor ɗin nanne Goshpower mai ƙaton catholic church ɗin nan dake a wuse2”.
Ɗan jimm Jay yay yana kallon
Dawood. Sai kuma ya sauke numfashi kaɗan yana wani guntun murmushi mai kama da an masa dole. “Okay thanks you, zaka iya tafiya”.
Miƙewa Dawood yayi tare da salute ɗinsa ya fice yana mamakin tambayoyin ogan nasu.
Dawood na fita Jay ya shiga Google. Bayanai ya nema akan dukkan handles ɗin papa dake a social network. Cikin mintuna ƙalilan kuwa suka watso masa komai. Facebook, Twitter, Istagram, Telegram, dama wasu daban-daban. Harda youtobe chennal da suke ɗaura dakan abubuwansu na church ɗinsu. Numfashi yaja ya furzar tare da shiga kowanne shafi ya duba followers nashi da duk wani posts da yayi a kai. Yawanci duk akan church ne dai.
Komawa yay bincike akan pictures nashi. A take kuwa suka bashi su da yawa. ‘Oh my GOD!!’. Jay ya faɗa da matuƙar razana. Gaba ɗaya kansa ya sake kullewa. yama rasa kalar tunanin da zaiyi dan da gaske shi dai ya shiga ruɗani. Ta yaya hakan zata kasance bayan shi shaidane akan abinda ya tabbatar a zahirin gani da ido. To amma inhar ta tabbata a tunanin da zuciayarsa ke bijiro masa lallai sai dai idan akwai yaudara a lamarin kenan, ko kuma...... Yay saurin girgiza kansa alamar ba haka baneba sam. dan da sun sani ai.
A wannan yanayin Bilkisu ta sake shigowa ta samesa. Rungumesa tayi ta baya tana sauke ajiyar zuciya. Shima ajiyar zuciyar ya sauke sannan ya zagayo da ita gabansa. Kaɗan ya ranƙwafo ya sumbaci laɓɓanta da goshinta.
“My Boss ina baƙin naka suke?”.
“Sun wuce Miemaa. sai dai ina cikin ruɗani wlhy”. Yay maganar yana jan hannunta wajen kujerarsa.
Zama tai a kujerar tana bashi amsa itama. “Bakai kaɗai bane a ruɗani. Ni kaina rikicewar ta hanani zama na gudo nabar su Ummie acan”.
Ta bayanta ya ranƙwafo yana nuna mata abinda ya samo game da papa. Ƙwarai da gaske ta cika da mamaki itama saboda ganin hoton papan. Dan haka sukayi zaman tattaunawa yay mata bayanin dukkan hukuncin daya yanke. Tare da alƙawarin zuwa wajen baba malam kozai ƙara samun wasu bayanai ta wajensa game da papan tunda sun zama surukai.
Ta gamsu ɗari bisa ɗari da hakan. Harma da zuwan wani cikin gidan, dan Little bee bazai yuwu taje gidan baba malam ɗin ta zaunaba saboda mijinta da wahala ya amince duk da yasan dokar aikin. Amma zai tura ƙaramar ƴarsu autar su Little ɗin mai suna Afrah akan case ɗin da su Yoohan ɗin suka kawo report.
_____________★★★
Lokacin da Yoohan ya shigo gidan ya iske duk suna church. Sai guards ɗinsa kawai da maigadi aka bari alamar papa yaji shawararsa ta kwanaki kenan. A cikin gidanma daya shiga ya samu Blessing. Cike dajin daɗin ganinsa da tunanin tare yake da Aymah ta shiga masa welcome. Ya amsa mata kadaran kadahan. Ya kama ƙafar benen zai haura Blessing da haƙurinta ya ƙare tace, “Sir Aunty fa?”.
Juyowa yay ya ɗan kalleta yana lumshe idanu da buɗewa. Sai kuma ya ɗan mata murmushi a bazata dan bata taɓa ganiba. Shi kuma jin daɗin nuna kulawarta ga matarsane ya sakashi yin murmushin. Sai da ya juya ya cigaba da hawa steps ɗin sannan ya bata amsa da, “Tana can na barota. Kina missing nata ne?”.
Cike da haɗiye ɗokinta tace, “Sosai ma Sir. I miss her so much”.
“Thanks you”. Ya faɗa a taƙaice yana idasa hayewa.
Da sanyin jiki Blessing ta koma kitchen dan ta haɗa masa wani ɗan abun duk da baice yana buƙata ba.
Fuskarta cike da miskilancin data gada wajen iyayenta ta ƙame tare da salute ɗin mahaifinta kuma oganta a wajen aiki. tace, “Sir gani”.
Daga Yoohan har Omar kallon mamaki suke mata. Dan basa buƙatar ƙarin bayanin komai game da Biljay.
Takardar da Dawood ya rubuta ya miƙa mata cike da bada umarni a gareta matsayin oga ba mahaifiba. “Duba min wannan takardar”.
“Okay sir” ta faɗa tana ɗaukar takardar. Cike da hazaƙar ƙwarewar aiki ta duba rubutun takardar tsaf, kafi. ta ɗago ta kallesa tana sunkuyar da kanta da ƙamewa. “Na duba Sir”.
“Me kika fahimta?”.
“Report ne na case ɗin ɓoyayyun mutane masu laifi”.
“Masha ALLAH. Little bee kece zakiyi wannan aikin. Waɗanan sune masu kawo Report ɗin. Zakiyi joining ɗinsu kuyi aikin tare. Sai dai kece zakiyi kutse a cikin gidan ko mubi ta wata hanyar insha ALLAH. Kinsan banson wasa, bana son kuskuren ganganci akan aiki, so be careful”.
“Insha ALLAH sir”.
Kai ya jinjina mata da maida dubansa kan Dawood. “Dawood tare zakuyi wannan aiki da ita, so zata kasance ƙarƙashin control ɗinka, dukanku kuma zaku kasance akan umarni”.
Shima ya amsa da “Okay sir”.
Daga haka Jay ya maida dubansa gasu Yoohan. “Doctors waɗanan nan sune zasu taimaka muku akan wannan case. Insha ALLAH daga nan zuwa kwana uku zamu san wadda zata shiga cikin gidan matsayin maiyin hutu a wajen Sheikh. Sauran aiki duk zasu yisa baku da damuwa. Sai dai dole kuma sai da hannunku a ciki dan kun fisu sanin sirrin gidan a yanzun. Zaka haɗata ƙawance da matarka ta waya. Dan wasu abubuwan ta hanyartane zasu sami haske sosai. Duk abinda ya dace zaku cigaba da ji ta hanyar Dawood, dan shine oganta”.
Godiya sosai su Yoohan suka shiga yimasa. Dan sam basuyi tunanin samun mafita cikin sauƙiba haka daga garesa oga kwatakwata da ganinsama ke da matuƙar wahala. Yanda bai musu bayani akan matsayin Bilkisu a garesaba suma basu tambayaba duk da sunada buƙatar ji.
A tare da shi suka fito office zuwa massalaci saboda kiran sallar zuhur. Bayan an idar da salla kuma sukai masa sallama da ƙarin godiya suka wuce cike da farin cikin wannan karamci da samun sauƙi. Sai dai ƙasan ran Yoohan shi kaɗai yasan mi yakeji game da Jay ɗin.
Koda suka ɗauki hanya kasa haƙuri Omar yayi sai da yayima Yoohan maganar kallon da yaga Jay ɗin na masa da matarsa. Harma hanata maganar da yayi. Tare da cewa nifa, “Wlhy fisgen kamannima kukaimin”.
Da mamaki Yoohan yace, “Kamanni kuma?”.
“Yes X-man. Wlhy a fisge kunyi kamanni like na jini haka”.
Nannauyan numfashi kawai Yoohan yaja da ƙarfi ya fesar batare da ya iya cewa komaiba har suka ƙarasa wani gidan cin abinci. Anan sukai lunch da cigaba da tattaunawa akan abinda ya shafesu. Daga haka sukawuce General hospital wajen Dr Shikurah. Sai dai sunyi rashin sa'ar samunta wai batama ƙasar.
Yoohan yayi gaisuwa da abokan arziƙi suka koma hotel ɗin daya sauka. Omar ya jima a wajensa dan har dare suna a tare sannan ya koma gidan papa dan acan ya sauka shi. Amma sai bai faɗama kowa Yoohan na ƙasarba.
Washe gari Yoohan yaje kaduna yin wani aiki. Sai washe garin daya cika kwana uku a 9ja ya dawo. Dai-dai da ranar da Little bee zata shiga gidan baba malam kenan. Dan haka kai tsaye gidansu ya nufa. Sai dai kawai su Madam Chioma suka gansa tsilum tamkar daren Christmas inji su.
___________★★
Tun wucewar su Yoohan Jay ya kasa zaune ya kasa tsaye a office ɗinsa. Gaba ɗaya man kan sa ya gama tsiyayewa tas akan wannan kamanni. Goshinsa ya murza da cewa, ‘Kai anya kuwa. Dolene nasan wanene wannan yaron’. Ya ƙare maganar da ɗaukar telephone yay kiran Dawood.
Dandanan Dawood ya amsa kiran boss. Nuna masa kujera yayi alamar ya zauna. Bayan kusan mintuna uku ya ture files ɗin gabansa yana kallon Dawood ɗin.
“Dawood nikam a ina kasan yaron nan ne?”.
Cike da girmamawa ya bashi amsa da faɗin, “Sir, tare mukai secondary school da su”.
“Masha ALLAH, lallai kayi masa sani na sosai. Anan cikin abuja suke?”.
“Yes sir. Ai yaron sanannen Pastor ɗin nanne Goshpower mai ƙaton catholic church ɗin nan dake a wuse2”.
Ɗan jimm Jay yay yana kallon
Dawood. Sai kuma ya sauke numfashi kaɗan yana wani guntun murmushi mai kama da an masa dole. “Okay thanks you, zaka iya tafiya”.
Miƙewa Dawood yayi tare da salute ɗinsa ya fice yana mamakin tambayoyin ogan nasu.
Dawood na fita Jay ya shiga Google. Bayanai ya nema akan dukkan handles ɗin papa dake a social network. Cikin mintuna ƙalilan kuwa suka watso masa komai. Facebook, Twitter, Istagram, Telegram, dama wasu daban-daban. Harda youtobe chennal da suke ɗaura dakan abubuwansu na church ɗinsu. Numfashi yaja ya furzar tare da shiga kowanne shafi ya duba followers nashi da duk wani posts da yayi a kai. Yawanci duk akan church ne dai.
Komawa yay bincike akan pictures nashi. A take kuwa suka bashi su da yawa. ‘Oh my GOD!!’. Jay ya faɗa da matuƙar razana. Gaba ɗaya kansa ya sake kullewa. yama rasa kalar tunanin da zaiyi dan da gaske shi dai ya shiga ruɗani. Ta yaya hakan zata kasance bayan shi shaidane akan abinda ya tabbatar a zahirin gani da ido. To amma inhar ta tabbata a tunanin da zuciayarsa ke bijiro masa lallai sai dai idan akwai yaudara a lamarin kenan, ko kuma...... Yay saurin girgiza kansa alamar ba haka baneba sam. dan da sun sani ai.
A wannan yanayin Bilkisu ta sake shigowa ta samesa. Rungumesa tayi ta baya tana sauke ajiyar zuciya. Shima ajiyar zuciyar ya sauke sannan ya zagayo da ita gabansa. Kaɗan ya ranƙwafo ya sumbaci laɓɓanta da goshinta.
“My Boss ina baƙin naka suke?”.
“Sun wuce Miemaa. sai dai ina cikin ruɗani wlhy”. Yay maganar yana jan hannunta wajen kujerarsa.
Zama tai a kujerar tana bashi amsa itama. “Bakai kaɗai bane a ruɗani. Ni kaina rikicewar ta hanani zama na gudo nabar su Ummie acan”.
Ta bayanta ya ranƙwafo yana nuna mata abinda ya samo game da papa. Ƙwarai da gaske ta cika da mamaki itama saboda ganin hoton papan. Dan haka sukayi zaman tattaunawa yay mata bayanin dukkan hukuncin daya yanke. Tare da alƙawarin zuwa wajen baba malam kozai ƙara samun wasu bayanai ta wajensa game da papan tunda sun zama surukai.
Ta gamsu ɗari bisa ɗari da hakan. Harma da zuwan wani cikin gidan, dan Little bee bazai yuwu taje gidan baba malam ɗin ta zaunaba saboda mijinta da wahala ya amince duk da yasan dokar aikin. Amma zai tura ƙaramar ƴarsu autar su Little ɗin mai suna Afrah akan case ɗin da su Yoohan ɗin suka kawo report.
_____________★★★
Lokacin da Yoohan ya shigo gidan ya iske duk suna church. Sai guards ɗinsa kawai da maigadi aka bari alamar papa yaji shawararsa ta kwanaki kenan. A cikin gidanma daya shiga ya samu Blessing. Cike dajin daɗin ganinsa da tunanin tare yake da Aymah ta shiga masa welcome. Ya amsa mata kadaran kadahan. Ya kama ƙafar benen zai haura Blessing da haƙurinta ya ƙare tace, “Sir Aunty fa?”.
Juyowa yay ya ɗan kalleta yana lumshe idanu da buɗewa. Sai kuma ya ɗan mata murmushi a bazata dan bata taɓa ganiba. Shi kuma jin daɗin nuna kulawarta ga matarsane ya sakashi yin murmushin. Sai da ya juya ya cigaba da hawa steps ɗin sannan ya bata amsa da, “Tana can na barota. Kina missing nata ne?”.
Cike da haɗiye ɗokinta tace, “Sosai ma Sir. I miss her so much”.
“Thanks you”. Ya faɗa a taƙaice yana idasa hayewa.
Da sanyin jiki Blessing ta koma kitchen dan ta haɗa masa wani ɗan abun duk da baice yana buƙata ba.