Sashe 55
Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Kuturun ubancan kayyasa! Yanzu wane algungumine mai wannan shirya tafiyar a gidanmu?”. Adawiya daketa faman zagaye ɗakinta ita kaɗai ta faɗa tana cizar laɓe kamar zata hudashi. Ganin babu mai bata amsa ta rarumo waya ta fara neman maman Aaida. Bugu biyu kuwa ta ɗaga. Harta fara tsokanarta Adawiyan ta katseta da faɗin, “Maman Aaida yanzu ba lokacin wasa bane, ko kinsan sister ɗin nan nawa da zata auri Yah Ab da, ta biyo kakarmu sunzo Umrah tare?”.
Da ƙarfi Maman Aaida tace, “Na shiga uku, da gaske dan ALLAH?”. Adawiya da ranta ya ƙara dugunzuma tace, “Wlhy kuwa. Bama zuwan nata bane tashin hankalina Maman Aaida, kinga kuwa yanda Yah Ab duk ya susuce, gashi kakarmu ɗin nan shegen sa idone da ita wlhy”.
“Tab, lallai aiki ya samemu, dan kuwa wlhy mukai sanya to ki tabbatar nanda wata ɗaya ko sati biyu ma mijinku zai koma na mata uku....”
“ALLAH ya kiyaye” Adawiya tai saurin katse Maman Aaida hawaye na ziraro mata a idanu. Takaicin maganganun maman Aaida ya sakata katse kiranma gaba ɗaya tai wurgi da wayar kan gado.
Abdallah dake ƙoƙarin shigowa ɗakin yace, “Lafiyarki kuwa kike wurgi da waya? Kamar ba kuɗi akasa aka saya ba!”. Da sauri tasaka hannu ta share hawayenta, kafin ta nufesa ta rungume da ƙarfi. Saurin tureta yay yana faɗin, “Haba Adawiya, shin wai kina mantawa muna azumi ne? Duk hanyar da zaki raunanama mutum azumi kin santa”.
“Kayi haƙuri Yah Ab, wlhy ɗokin zuwan Nu'aymah ne ya sakani yin hakan”.
“Umyim! Kina ɗokin zuwan natane kika barta tafiya ɗakin da Hajjo zata zauna ta sauka”. Kamar zatai kuka ta kallesa, acan ƙasan ranta kuma tamkar ana babbaka wuta, cikin shagwaɓa tace, “Damafa jira nake kazo na kawo maka ƙararta ALLAH, nayi-nayi tazo mu zauna anan taƙi, wai batason shiga haƙƙinmu”.
Kafeta yay da idanu kamar mai nazarinta, sai kuma ya ɗauke kawai yana ƙaɗa kansa ya fice batare daya bata amsa ba.
Harara ta raka bayansa da shi harya fice, taja gajeren tsaki, ‘Wlhy tunda aka munafunceni sai yarinyarnan ta gwammaci kiɗa da karatu a gidan nan, ni kama ƙaramin haske akan dawowarta ɗakin nan Yah Ab, dan wannan itace babar damar da zan riƙe wajen tarwatsa zuciyarta, saina maidata mahaukaciyar gaske idan da ƙaramin haukane a kan nata mtsoww!! Aikin banza kawai’.
Oho, ita Nu'aymah ma batasan tanayiba, dan bata sake leƙo falonba har lokacin shan ruwa ya ƙarasa, itama Adawiya bata shiga inda sukeba ta maƙale akan shirya kayan shan ruwa takeyi. Duk da kuwa ba ita ta girkaba. Fita Abdallah yay ya musu order ɗin komai daya dace, dan yasan Adawiya bazata iyaba ita kaɗai tunda sunada yawa. Bai kuma kamata asa Nu'aymah shiga kitchen ba daga zuwansu.
Aikin da Adawiya tayi kawai shine shirya abincin a tsakkiyar falo, wanda saida Abdallah ma ya tayata suka tsara komai a inda ya dace.
Koda aka kira salla ruwa da dabino kawai suka ɗanci, sannan suka gabatar da sallar magriba. Daga hajjo har Nu'aymah basu zaƙeba akan abincin, sukai zamansu gefe suna tsumayen tayi daga Adawiya. Itako hankalinta ma baya garesu, tana can tana ƙullama zuciyarta abinda zata aikata a wajen shan ruwan idan an zauna danta cusama Nu'aymah takaici. Shiyyasa ta fara ƙoƙarin shiryama Abdallah nashi tunkafin su shigo.
“A'a Hajjo ya naga baku fara buɗa bakin ba?”. Abdallah da ke ƙoƙarin ƙarasowa cikin falon sosai ya faɗa idonsa akan Nu'aymah dake danna waya. Wando da rigane marasa nauyi a jikinta, sanin basu kaɗai bane ya sakata ɗoro hijjab a sama wanda yaje mata har gwiwa.
Murmushi hajjo dake kallon Adawiya cike da nazari tayi, sai kuma ta maida kallonta ga Abdallahn tana faɗin, “Ku muke jira mana, dan zaifi daɗin ci ai”. Cike da jin daɗi ya kama hannunta ya sumbata, kafin ya zauna kusa da ita yana gaisheta da mata barka da shan ruwa. Nu'aymah dake a ɗayan gefen Hajjo itama tace, “Barkanku da shan ruwa”. Ahmad dake ƙoƙarin zama kusa da Abdallah ne kawai ya amsa, sai hajjo data ƙwace wayar tana harararta da faɗin, “Sai yanzu kika san damu?”.
“Waini miyasama na biyoki?”. Nu'aymah ta faɗa cikin haushin amshe mata waya tana tura baki cike da shagwaɓa. Hajjo da Ahmad sukai dariya, hajjo tace, “Tambayi kanki mana, ja'ira kawai”.
Adawiya da abun sam bai burgetaba, ta kalli Abdallah da gaba ɗaya hankalinsa akan Nu'aymah yake. Haushine ya sake turniƙeta, murya a cinkushe tace, “Yah Ab ga abincinka”. Kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa. “Gasu hajjo da suke baƙi baki haɗa musuba sai ni da ko shigowa banyiba........?”
Katseshi Hajjo tai da faɗin, “Kaga barta, ai abincinma so nake a haɗesa a babban tray mu haɗu tare mu sami ladan juna”.
‘Tabɗi jan’ Adawiya ta faɗa a ranta tana jin wani tuƙuƙin baƙin ciki, a fili kuwa sai ta kafe Abdallah da ido a zatonta ko zaice wani abu. Duk da ya ganta sarai baice uffanba, saima ɗauke kansa yay abinsa.
Hajjo da duk take lura da motsin kowa tace, “Zainabu zuba abincin, ki haɗe da wanda Adawiya ta zuba duk a haɗu kowa ya saka hannunsa”.
Murmushi Nu'aymah tayi a karon farko, ta gyara zamanta tana faɗin, “Angama Hajjaju uwar masu gida, uwar gida ran gidan malam Hashimu ɗan jibiya”.
Sosai Abdallah, Ahmad da Hajjo suka sanya dariya da kirarin na Nu'aymah. Hajjo ta ranƙwasheta akai tana faɗin, “Ja'ira”. Adawiya kam wani baƙin cikine ya kumeta a rai, harta kasa daurewa ta miƙe.
Abdallah yace, “K kuma ina zaki?”. Da ƙyar ta iya haɗiye kukanta tace, “Zan ɗakko abune a kitchen”. Bata jira amsarsa ba tai gaba.
Wani shegen murmushi Hajjo da Nu'aymah suka saki, wanda kowa da manufar nasa.
Hawaye sosai Adawiya tayi a kitchen, sai dai gudun kar wani ya biyota yasata saurin wanke fuskarta ta ɗakko ruwa ta fito.
Koda ta dawo babu wanda ya tanka mata, saima ƙoƙarin kai abinci suke a cikinsu. Yayinda Abdallah duk Motsin Nu'aymah na gunada ne a idonsa. Itama Nu'aymahr dai hankalinta na a kansa. Sai dai tana ƙoƙarin fuskewa ita babu mai ganeta.
A haka dai suka kammala buɗa bakin, yayinda kowa yaci komai dai-dai misalin da bazai cutu ba. Duk da akwai gajiya tattare dasu haka suka rarrafa zuwa massallaci sukai isha'i da asham. Kafin su dawo kowa ya nema makwanci.
Abin mamaki sai ga Adawiya tayi shiri ta tafi kwana ɗakin Abdallah.
(😂ta wajena Adawiya gara ki dage ki samu kan, gaskiya fa, dan naga su o'e anzo saudia da shirin Snatching mijin mutane.😎🙄🚶🏻)
_______________________________
*_NIGERIA_*
“Wai tunanin mi kiketayi ne haka da zurfi Darling? indai akan Yoohan ne na samo mana mafita”.
Da sauri Momy ta juyo tana kallon papa da ke maganar da yarensu, bakinta har ɗan rawa yake wajen tambayarsa wace irin mafita ya samo?.
Sai da ya rungumeta kafin yace, “Mu lallaɓashi ya auri Miracle kawai”. A wani irin zumbur ta miƙe zaune tamkar wadda maciji ya sara. Ta nuna Papa da yatsa tana faɗin, “Kasan mi kake faɗ kuwa Darling? duka-duka shekarar Yoohan ɗin nawa da kake maganar yay aure? Indama son Miracle ɗin yake to da sauƙi, amma kana ganin yanda yake mata a gidan nan ai ko”.
Tsuru papa yay yana kallon yanda matar tasa ke masifa kamar zata haɗiye harshenta, sai da takai ayar zancenta tana wani huci sannan yay saurin jawota jikinsa yana girgiza kansa. “Ki fahimceni mana, idan Yoohan yay aure matarsa zata dinga ɗebe masa kewa a duk lokacin da ya shiga irin wannan damuwar, kum.......”
“Kaga nifa bani da lokacin wannan maganar, ka barni barci nakeji”. Ta faɗa ranta a ɓace da ƙwace jikinta taje gefen gadon ta kwanta. Da kallo kawai ya iya binta har na tsahon lokaci, kafin shima ya kwanta ɗin yana sauke tagwayen ajiyar zuciya. A cikin ransa kuwa ya ƙudiri aniyar lallaɓata ita da Yoohan ɗin har sai sun amince da ƙudirinsa.
*_WASHE GARI_* safiyar lahadi, tunda safe jama'ar gidan suka shiga hada-hadar shirin fita church, dan papa ma tun da sauran duhun safiya ya fice shi.
Rich daya fito wanka ya kai dubansa ga Yoohan dake zaune kan sofa, ƙafafunsa miƙe akan table, ya jingina bayansa kansa na kallon sama. Duk da idanunsa a lumshe suke ya tabbatar ba barci yake ba.
“Doctor ya kamata ka tashi kai shiri mu shiga church ko? Idan mun fito sai mu ɗan zaga gari danni yau da yamma zan koma Lagos”.
Shiru Yoohan bai motsaba, duk da kuwa sarai yanajin Rich ɗin. Sai da ya ɓata wasu mintuna kafin ya buɗe idanunsa da sukai wani irin kumburowa, fatarsu tayi jaa sosai alamar jin barci tattare da shi, hakama fuskar tayi jajur sosai abin tausayi. Miƙewa yay batare da yayi magana ba, ya wuce toilet yana ɗan ɗingisa ƙafarsa da bata gama sakiba, sai dai hakan kuma sai ya bama tafiyar tasa wani style daban kamar mai tafiyar izza.
Baija dogon lokaciba ya fito ɗaure da towel ruwan gwaiduwar ƙwai. Babu kowa a ɗakin dan Richard ya gama shirinsa ya fice. Ya ƙarasa gaban mirror, shafe jikinsa yay da mai da kayan ƙamshi tamkar yanda ya saba, kafin ya nufi wajen kayansa. Fararen suit ya ɗakko yana ɗan yamutsa fuska da kallonsu. Sai kuma yabar wajen dasu zuwa gaban gado. Tsaf ya shirya a cikin suit ɗin da sukai masifar zama masa a jiki, tare da fiddo surarsa mai jan hankalin mata dama mazan kansu. Necktie ɗin ya ɗauka a hannu tare da jacket ɗin suit ɗin, dan shi kam har yanzu ɗaura tie na masa wahala. Gaban mirror ya sake komawa ya feshe kansa da kalolin designers ɗin turarurrukansa, kafin ya ɗau sarƙa ɗaya a cikin sarƙoƙinsa na Cross da taji zallar diamond tanata ɗaukar idanu ya saka. Ya ɗauki agogo ya ɗaura tare ɗan wani abin hannu na gayu ya ɗaura a ɗayan hannun, ya kuma manna ɗan kunnensa a kunne ɗaya. Yayi ƙyau sosai, duk da kuwa fuskar a turɓune take matuƙa. Amma yanda yau ya gyara kansa da sajensa sai yay ɗas da shi kamar ka suresa ga gudu.
Da ƙarfi Maman Aaida tace, “Na shiga uku, da gaske dan ALLAH?”. Adawiya da ranta ya ƙara dugunzuma tace, “Wlhy kuwa. Bama zuwan nata bane tashin hankalina Maman Aaida, kinga kuwa yanda Yah Ab duk ya susuce, gashi kakarmu ɗin nan shegen sa idone da ita wlhy”.
“Tab, lallai aiki ya samemu, dan kuwa wlhy mukai sanya to ki tabbatar nanda wata ɗaya ko sati biyu ma mijinku zai koma na mata uku....”
“ALLAH ya kiyaye” Adawiya tai saurin katse Maman Aaida hawaye na ziraro mata a idanu. Takaicin maganganun maman Aaida ya sakata katse kiranma gaba ɗaya tai wurgi da wayar kan gado.
Abdallah dake ƙoƙarin shigowa ɗakin yace, “Lafiyarki kuwa kike wurgi da waya? Kamar ba kuɗi akasa aka saya ba!”. Da sauri tasaka hannu ta share hawayenta, kafin ta nufesa ta rungume da ƙarfi. Saurin tureta yay yana faɗin, “Haba Adawiya, shin wai kina mantawa muna azumi ne? Duk hanyar da zaki raunanama mutum azumi kin santa”.
“Kayi haƙuri Yah Ab, wlhy ɗokin zuwan Nu'aymah ne ya sakani yin hakan”.
“Umyim! Kina ɗokin zuwan natane kika barta tafiya ɗakin da Hajjo zata zauna ta sauka”. Kamar zatai kuka ta kallesa, acan ƙasan ranta kuma tamkar ana babbaka wuta, cikin shagwaɓa tace, “Damafa jira nake kazo na kawo maka ƙararta ALLAH, nayi-nayi tazo mu zauna anan taƙi, wai batason shiga haƙƙinmu”.
Kafeta yay da idanu kamar mai nazarinta, sai kuma ya ɗauke kawai yana ƙaɗa kansa ya fice batare daya bata amsa ba.
Harara ta raka bayansa da shi harya fice, taja gajeren tsaki, ‘Wlhy tunda aka munafunceni sai yarinyarnan ta gwammaci kiɗa da karatu a gidan nan, ni kama ƙaramin haske akan dawowarta ɗakin nan Yah Ab, dan wannan itace babar damar da zan riƙe wajen tarwatsa zuciyarta, saina maidata mahaukaciyar gaske idan da ƙaramin haukane a kan nata mtsoww!! Aikin banza kawai’.
Oho, ita Nu'aymah ma batasan tanayiba, dan bata sake leƙo falonba har lokacin shan ruwa ya ƙarasa, itama Adawiya bata shiga inda sukeba ta maƙale akan shirya kayan shan ruwa takeyi. Duk da kuwa ba ita ta girkaba. Fita Abdallah yay ya musu order ɗin komai daya dace, dan yasan Adawiya bazata iyaba ita kaɗai tunda sunada yawa. Bai kuma kamata asa Nu'aymah shiga kitchen ba daga zuwansu.
Aikin da Adawiya tayi kawai shine shirya abincin a tsakkiyar falo, wanda saida Abdallah ma ya tayata suka tsara komai a inda ya dace.
Koda aka kira salla ruwa da dabino kawai suka ɗanci, sannan suka gabatar da sallar magriba. Daga hajjo har Nu'aymah basu zaƙeba akan abincin, sukai zamansu gefe suna tsumayen tayi daga Adawiya. Itako hankalinta ma baya garesu, tana can tana ƙullama zuciyarta abinda zata aikata a wajen shan ruwan idan an zauna danta cusama Nu'aymah takaici. Shiyyasa ta fara ƙoƙarin shiryama Abdallah nashi tunkafin su shigo.
“A'a Hajjo ya naga baku fara buɗa bakin ba?”. Abdallah da ke ƙoƙarin ƙarasowa cikin falon sosai ya faɗa idonsa akan Nu'aymah dake danna waya. Wando da rigane marasa nauyi a jikinta, sanin basu kaɗai bane ya sakata ɗoro hijjab a sama wanda yaje mata har gwiwa.
Murmushi hajjo dake kallon Adawiya cike da nazari tayi, sai kuma ta maida kallonta ga Abdallahn tana faɗin, “Ku muke jira mana, dan zaifi daɗin ci ai”. Cike da jin daɗi ya kama hannunta ya sumbata, kafin ya zauna kusa da ita yana gaisheta da mata barka da shan ruwa. Nu'aymah dake a ɗayan gefen Hajjo itama tace, “Barkanku da shan ruwa”. Ahmad dake ƙoƙarin zama kusa da Abdallah ne kawai ya amsa, sai hajjo data ƙwace wayar tana harararta da faɗin, “Sai yanzu kika san damu?”.
“Waini miyasama na biyoki?”. Nu'aymah ta faɗa cikin haushin amshe mata waya tana tura baki cike da shagwaɓa. Hajjo da Ahmad sukai dariya, hajjo tace, “Tambayi kanki mana, ja'ira kawai”.
Adawiya da abun sam bai burgetaba, ta kalli Abdallah da gaba ɗaya hankalinsa akan Nu'aymah yake. Haushine ya sake turniƙeta, murya a cinkushe tace, “Yah Ab ga abincinka”. Kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa. “Gasu hajjo da suke baƙi baki haɗa musuba sai ni da ko shigowa banyiba........?”
Katseshi Hajjo tai da faɗin, “Kaga barta, ai abincinma so nake a haɗesa a babban tray mu haɗu tare mu sami ladan juna”.
‘Tabɗi jan’ Adawiya ta faɗa a ranta tana jin wani tuƙuƙin baƙin ciki, a fili kuwa sai ta kafe Abdallah da ido a zatonta ko zaice wani abu. Duk da ya ganta sarai baice uffanba, saima ɗauke kansa yay abinsa.
Hajjo da duk take lura da motsin kowa tace, “Zainabu zuba abincin, ki haɗe da wanda Adawiya ta zuba duk a haɗu kowa ya saka hannunsa”.
Murmushi Nu'aymah tayi a karon farko, ta gyara zamanta tana faɗin, “Angama Hajjaju uwar masu gida, uwar gida ran gidan malam Hashimu ɗan jibiya”.
Sosai Abdallah, Ahmad da Hajjo suka sanya dariya da kirarin na Nu'aymah. Hajjo ta ranƙwasheta akai tana faɗin, “Ja'ira”. Adawiya kam wani baƙin cikine ya kumeta a rai, harta kasa daurewa ta miƙe.
Abdallah yace, “K kuma ina zaki?”. Da ƙyar ta iya haɗiye kukanta tace, “Zan ɗakko abune a kitchen”. Bata jira amsarsa ba tai gaba.
Wani shegen murmushi Hajjo da Nu'aymah suka saki, wanda kowa da manufar nasa.
Hawaye sosai Adawiya tayi a kitchen, sai dai gudun kar wani ya biyota yasata saurin wanke fuskarta ta ɗakko ruwa ta fito.
Koda ta dawo babu wanda ya tanka mata, saima ƙoƙarin kai abinci suke a cikinsu. Yayinda Abdallah duk Motsin Nu'aymah na gunada ne a idonsa. Itama Nu'aymahr dai hankalinta na a kansa. Sai dai tana ƙoƙarin fuskewa ita babu mai ganeta.
A haka dai suka kammala buɗa bakin, yayinda kowa yaci komai dai-dai misalin da bazai cutu ba. Duk da akwai gajiya tattare dasu haka suka rarrafa zuwa massallaci sukai isha'i da asham. Kafin su dawo kowa ya nema makwanci.
Abin mamaki sai ga Adawiya tayi shiri ta tafi kwana ɗakin Abdallah.
(😂ta wajena Adawiya gara ki dage ki samu kan, gaskiya fa, dan naga su o'e anzo saudia da shirin Snatching mijin mutane.😎🙄🚶🏻)
_______________________________
*_NIGERIA_*
“Wai tunanin mi kiketayi ne haka da zurfi Darling? indai akan Yoohan ne na samo mana mafita”.
Da sauri Momy ta juyo tana kallon papa da ke maganar da yarensu, bakinta har ɗan rawa yake wajen tambayarsa wace irin mafita ya samo?.
Sai da ya rungumeta kafin yace, “Mu lallaɓashi ya auri Miracle kawai”. A wani irin zumbur ta miƙe zaune tamkar wadda maciji ya sara. Ta nuna Papa da yatsa tana faɗin, “Kasan mi kake faɗ kuwa Darling? duka-duka shekarar Yoohan ɗin nawa da kake maganar yay aure? Indama son Miracle ɗin yake to da sauƙi, amma kana ganin yanda yake mata a gidan nan ai ko”.
Tsuru papa yay yana kallon yanda matar tasa ke masifa kamar zata haɗiye harshenta, sai da takai ayar zancenta tana wani huci sannan yay saurin jawota jikinsa yana girgiza kansa. “Ki fahimceni mana, idan Yoohan yay aure matarsa zata dinga ɗebe masa kewa a duk lokacin da ya shiga irin wannan damuwar, kum.......”
“Kaga nifa bani da lokacin wannan maganar, ka barni barci nakeji”. Ta faɗa ranta a ɓace da ƙwace jikinta taje gefen gadon ta kwanta. Da kallo kawai ya iya binta har na tsahon lokaci, kafin shima ya kwanta ɗin yana sauke tagwayen ajiyar zuciya. A cikin ransa kuwa ya ƙudiri aniyar lallaɓata ita da Yoohan ɗin har sai sun amince da ƙudirinsa.
*_WASHE GARI_* safiyar lahadi, tunda safe jama'ar gidan suka shiga hada-hadar shirin fita church, dan papa ma tun da sauran duhun safiya ya fice shi.
Rich daya fito wanka ya kai dubansa ga Yoohan dake zaune kan sofa, ƙafafunsa miƙe akan table, ya jingina bayansa kansa na kallon sama. Duk da idanunsa a lumshe suke ya tabbatar ba barci yake ba.
“Doctor ya kamata ka tashi kai shiri mu shiga church ko? Idan mun fito sai mu ɗan zaga gari danni yau da yamma zan koma Lagos”.
Shiru Yoohan bai motsaba, duk da kuwa sarai yanajin Rich ɗin. Sai da ya ɓata wasu mintuna kafin ya buɗe idanunsa da sukai wani irin kumburowa, fatarsu tayi jaa sosai alamar jin barci tattare da shi, hakama fuskar tayi jajur sosai abin tausayi. Miƙewa yay batare da yayi magana ba, ya wuce toilet yana ɗan ɗingisa ƙafarsa da bata gama sakiba, sai dai hakan kuma sai ya bama tafiyar tasa wani style daban kamar mai tafiyar izza.
Baija dogon lokaciba ya fito ɗaure da towel ruwan gwaiduwar ƙwai. Babu kowa a ɗakin dan Richard ya gama shirinsa ya fice. Ya ƙarasa gaban mirror, shafe jikinsa yay da mai da kayan ƙamshi tamkar yanda ya saba, kafin ya nufi wajen kayansa. Fararen suit ya ɗakko yana ɗan yamutsa fuska da kallonsu. Sai kuma yabar wajen dasu zuwa gaban gado. Tsaf ya shirya a cikin suit ɗin da sukai masifar zama masa a jiki, tare da fiddo surarsa mai jan hankalin mata dama mazan kansu. Necktie ɗin ya ɗauka a hannu tare da jacket ɗin suit ɗin, dan shi kam har yanzu ɗaura tie na masa wahala. Gaban mirror ya sake komawa ya feshe kansa da kalolin designers ɗin turarurrukansa, kafin ya ɗau sarƙa ɗaya a cikin sarƙoƙinsa na Cross da taji zallar diamond tanata ɗaukar idanu ya saka. Ya ɗauki agogo ya ɗaura tare ɗan wani abin hannu na gayu ya ɗaura a ɗayan hannun, ya kuma manna ɗan kunnensa a kunne ɗaya. Yayi ƙyau sosai, duk da kuwa fuskar a turɓune take matuƙa. Amma yanda yau ya gyara kansa da sajensa sai yay ɗas da shi kamar ka suresa ga gudu.