Sashe 112
Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bai fi mintuna huɗu da fita ba ya dawo hannunsa ɗauke da kofin tea ruwan hanta, yanda turiri keta fita ta samansa zai baka tabbacin shayi ne..
A gefen gadon ya zauna daf da ita. Hakanne ya sakata matsawa da sauri. Baki yaɗan taɓe, batare da ya kalleta ba yace, “Oya tashi”. “Na maka mi?” ta bashi amsa tana satar kallonsa. Kofin tea ɗin kawai ya miƙa mata batare da ya sake cewa komai ba.
“Tab, toni nace maka zansha tea ne? Na ƙoshi”.
“Silly girl”
ya faɗa yana hararta a karo na farko. Ya sake tsuke fuska da faɗin, “Malama tashi kiyi breakfast kona juye miki shayin nan ta hanci”.
Tuni idanun Aymah suka ciko da ƙwalla, cikin rawar sanyin da yake ƙaruwa mata tace, “To ana dole ne? Nace na ƙoshi ba sai ka barni ba”. Komai bai sake ce mataba, sai dire kofin yayi a saman bedside drawer ɗin ya miƙe. Fita yay da ga ɗakin. Da sauri Aymah tace, ‘ALLAH ya hanaka ikon dawowa mai zubin masu jajayen kunne, da wani kansa kamar sheƙar angulu’. (Wlhy ke da shi Aymah ni dai ba ruwa na😂).
Ganin abinda ya dawo da shi a hannu ya sakata miƙewa zumbur jikinta na rawa. Shiko ko kallon inda take ya ƙiyi sai ƙoƙarin ɓare syringe ɗin daya shigo da shi ya keyi. Ya sake zama a bakin gadon yana ɓalle bakin kwalbar maganin, tare da saka kan allurar jikin syringe ɗin ya zuƙe ruwan allurar da ya kusa rabin syringe ɗin. Ajiyewa yay a gefenta bayan ya gama, sannan ya ɗakko kofin shayin ya miƙa mata batare da yace komai ba.
Da iya gaskiyarta take ziraro da hawaye, zuciyarta sai bugawa take da sauri-sauri. Tabbas a rayuwarta allura na ɗaya daga cikin abinda take tsoro fiye da hasashen mai karatu, sai kuma duhu. Waɗan nan abubuwan ko a tunani batason tunasu suna tayar mata da hankali. Hakan yasa hannunta har karkarwa yake wajen miƙa hannu ta amshi kofin shayin. Nanma baice da ita komai ba ya sakar mata. Tiren kayan breakfast ɗin ya ɗakko gaba ɗayansa ya ajiye saman gadon a gabanta. Bayan ya buɗe mata koma ya ɗago ya kamata tana jan allurar daya ajiye alamar so take ta ɓoye.
Da ƙyar ya iya danne dariyar data zo masa a maƙoshi. ya sake tsuke fuska yana balla mata harara. “Idanma kin ɓoye inada gomanta a ɗakina, kinga kenan kinyi na banza. Na baki 20minutes kacal naga tray ɗin nan empty”.
Hannu tasa ta sake share hawayen da suka ciko mata idanu, cikin ƙunƙunin da bazaijiba tace, ‘Tunda ga jaka rumbu uwar zira lauma an kawo maka ko’. A fili kuwa duƙar da kai ƙasa tai kamar ta ALLAH😂.
Hannunsa ya ɗora saman nata da har yanzu ke riƙe da syringe ɗin ya zare abarsa. Gefensa ya ajiye tare da gyara filos ɗin dake birjit a saman gadon ya kwanta rigingine. Wayarsa ya ɗauka ya hau dannawa tamkar ya manta da ita a ɗakin.
Ɗagowa goma Aymah zatayi harara ashirin take antaya masa. Baƙar magana kuwa da gorin hawa mata gado da yay tayi yafi sau ɗari babu ɗaya tana tunzura baki gaba. Daka ganta kasan tsoro ne fal ranta kawai da neman faɗa da tafi ƙwarewa a yi. Shi dai bai sake bi ta kanta ba duk da yana jin ƙunƙunin da takeyi da harar da take masa. Sai dai kasancewar hausa takeyi bai damu da abinda take cewarba. Da yake dama yunwar ta keji sai gashi ta shanye tea ɗin duka dan ya mata daɗi. Harko da ayyanawa take a ranta ‘Wai buzun nan ashe ya iya haɗa shayi’ (Kai wagga ɗiya ta baba malam ALLAH dai ya gyara😆😂). A sauran abincin kuwa bread kawai taci, dan yanda aka haɗashi ya mata ƙyau a ido da daɗi a baki. Wai saida ta gama ci kuma sai cewa tai, ‘ALLAH dai yasa ba arnakun nan suka yishiba na wage baki ina turawa kamar a haɗiɗiya’. (Ke dai kika sani🤣).
Ganin ta kammala Yoohan ya miƙe zaune sosai yana ajiye wayar hannunsa. Trayn ya sauke ƙasa, batare da ce mata uffan ba ya matso daf da ita sosai har suna jin saukar numfashin juna. Zabura tayi da sauri zata matsa ya riƙota. Baya buƙatar hayaniyarta a yanzu saboda jikinta yay masifar zafin zazzaɓi, shegen taurin kanta ne kawai ya hana bakinta da bai rabo da tsiwa yin shiru. Baki ta buɗe zata fara masa tijara ya mannesa da nashi tare da sake jawota ya matseta a jikinsa tsam. Ƙarfin ba ɗaya bane, hakan yasa duk mutsu-tsunta ko gezau baiyiba balle tasaran kubuta. Syringe ɗin daya ɗura ruwan allura ya ɗauka, batai auneba sai jin shigarta tayi cikin tsokar jikinta. Tabbas da bakinta baya cikin nasa ba ƴan gidan kaɗaiba har maƙwafta sai sunsan ta kwana a gidan yau. Dan allurar malaria ce daya fahimci shike saka mata zazzaɓin yay mata, allurar kam tana da azabar zafi, dan saita ratsa kowacce kafar magudanar jini da ɓargon mutum kafin a hankali ta fara bashi nutsuwa.
Wani irin mugun ƙanƙamesa tayi jikinta na rawa. Harma ya zare allurar yana murza mata wajen bata dawo hayyacinta ba. Bakinsa ya janye a cikin nata a hankali yana sauke wani wahalallen numfashi da gajerun ajiyar zuciya a jere. Itakam kuka ta fashe da shi jin ta samu bakinta, sai ƙara ƙanƙamesa take kamar zata koma masa ciki saboda yanda zafin allurar ke gauraye duk jikinta. Haɓarsa ya ɗaura saman kanta yana ɗan murmushi da lumshe idanunsa. Hannayensa a bayanta yana shafawa a hankali alamar lallashi.
Sun sami tsahon mintuna biyar a haka sannan ta tureshi da ƙarfi tana janye jikinta baya. Cikin kuka kashirɓan tace, “Wlhy sai ALLAH ya mana hisabi da kai tun a duniyarnan tasa. tunda ai cakai idan naci abincin bazaka minba shine ka karya alƙawari. Na rantse saina faɗama Abbana” ta goge bakinta da bargo tana cigaba da faɗin, “Ƙazami kawai mayen bakin mutane”.
Shi dai komai baice mataba. Kallonta kawai yake da narkakkun idanunsa masu cikar gashi da haske. Tana cigaba da masifarta da goge baki yaga ta fara ajiyar zuciya da lumshe idanu alamar gyangyaɗi. Basuyi mintuna bakwai ba a haka ta ɓingire barci. Kansa yaɗan girgiza kawai. A kan laɓɓansa ya furta “Yeyyey girl, mai bakin tsiwa”.
Sauka yay daga kan gadon ya zagaya ɗayan gefen gadon data koma tun turesa da tayi. Kwanciyar ya gyara mata, ya fara ƙoƙarin zare hijjabin jikinta. Amma kasancewar barcin baiyi nisa ba, sai ta shiga ture masa hannu cikin kasala irin ta mai barci. Durƙusawa yay gaban gadon ya riƙe hannun nata cikin nasa. idanunsa ƙyam akan ƙyaƙyƙyawar fuskarta da komai ya dace da ita. Bata zare hannun nataba daga cikin nasa tabbacin barcin ya fara nauyi. Sai ajiyar zuciya da take faman saukewa a jajjere. Sai da ya ƙara bata mintuna kusan uku kafin ya kai dubansa ga hannunta data matse nasa. Zanen ƙunshin ya ringabi da kallo yana ɗan murzawa da babban yatsansa a hankali, abin ya masa ƙyau sosai, sai dai a ƙasan ransa tunani yake badai tattoo bane ba?. Jin ta ɗan motsa ya juyo ya kalleta. Yanda ta wani taɓe baki a cikin barcin kamar zatai kuka sai abin ya so bashi dariya. A fili ya furta “Trouble maker” yana lumshe idanunsa ya sake buɗewa a kanta.
Gudun kar hijjabin ya shaƙeta ne ya sashi cire mata shi cikin dabara. Sai kuma yaci karo da bata da riga sai zani data ɗaura. Kallo ɗaya yay mata ya janye idanunsa yaja bargon ya lulluɓa mata.
Oho, ita dai duk batasan yanayi ba, barcinta take zazzaɓin na sauka mata a hankali. Sai da ya gama bin ɗakin da kallo tsaf sannan ya fice a ransa yana yaba ƙoƙarin iyayenta. Dan ko kujerun da aka zauba musu a falon yasan kuɗi sosai aka zuba wajen sayensu.
________★★★_______
A kano ta dabo kam baƙi sun isa gida lafiya da shatara ta arziƙin da suka samu. yanzun kam gidan ya koma shiru duk baƙi sun kama gabansu, hakan yasa suma duk basu wani yi zaman awa bibbiyu ba a gidan duk suka tafi. Sai Ananah kawai da ba yaune ranar tafiyar tataba ita. Amma jikokinta da sauran ƴaƴanta duk sun koma katsina tun jiya...........✍
_Kuyi manage da wannan bajin daɗin jikina nakeba, mura tamin ram🤦🏻_.
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.
No. 47
________
I'm on Instagram as yerwaincense_and_more. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=ayfowzb2ah8k&utm_content=6k8ur6p.
INA MA’ABOTA KARATUN LITTATTAFAN HAUSA? WANDA ZAI NISHADANTAR DAKU, YA FADAKAR, YA KUMA TSUNDUMA KU A KOGIN LOBAYYAR KAUNA? TO KU MATSO KUSA... DOMIN MUNZO MUKU DA ALBISHIR DIN WANI GANGARIYAR LITTAFI.. DAYA NE TAMKAR DA DUBU.. YAZO DA WANI SALO NA DABAN WANDA ZAI SANYAYA ZUKATAH.._
_LITTAFIN *UNCLE NE...* LITTAFI NE FIRST OF ITS KIND, DA YAZO A WANNAN SHEKARA TA 2021. AN BAJE KOLIN BASIRA A BOOK DIN UNCLE NE.._
_”Wait... Dakata hafsat Rano, Kina nufin NIMCYLUV, dai shararriyar murubuciyar nan itace tazo da wani salon rubutun..?..”_
_”Kede bari Billyn Abdul.. Tsaya kiji kanun labarin a tak’aice..*NIMCYLUV* Tace book din a ta’kaice labarin *UNCLE NE* ne yana tafe:_
A gefen gadon ya zauna daf da ita. Hakanne ya sakata matsawa da sauri. Baki yaɗan taɓe, batare da ya kalleta ba yace, “Oya tashi”. “Na maka mi?” ta bashi amsa tana satar kallonsa. Kofin tea ɗin kawai ya miƙa mata batare da ya sake cewa komai ba.
“Tab, toni nace maka zansha tea ne? Na ƙoshi”.
“Silly girl”
ya faɗa yana hararta a karo na farko. Ya sake tsuke fuska da faɗin, “Malama tashi kiyi breakfast kona juye miki shayin nan ta hanci”.
Tuni idanun Aymah suka ciko da ƙwalla, cikin rawar sanyin da yake ƙaruwa mata tace, “To ana dole ne? Nace na ƙoshi ba sai ka barni ba”. Komai bai sake ce mataba, sai dire kofin yayi a saman bedside drawer ɗin ya miƙe. Fita yay da ga ɗakin. Da sauri Aymah tace, ‘ALLAH ya hanaka ikon dawowa mai zubin masu jajayen kunne, da wani kansa kamar sheƙar angulu’. (Wlhy ke da shi Aymah ni dai ba ruwa na😂).
Ganin abinda ya dawo da shi a hannu ya sakata miƙewa zumbur jikinta na rawa. Shiko ko kallon inda take ya ƙiyi sai ƙoƙarin ɓare syringe ɗin daya shigo da shi ya keyi. Ya sake zama a bakin gadon yana ɓalle bakin kwalbar maganin, tare da saka kan allurar jikin syringe ɗin ya zuƙe ruwan allurar da ya kusa rabin syringe ɗin. Ajiyewa yay a gefenta bayan ya gama, sannan ya ɗakko kofin shayin ya miƙa mata batare da yace komai ba.
Da iya gaskiyarta take ziraro da hawaye, zuciyarta sai bugawa take da sauri-sauri. Tabbas a rayuwarta allura na ɗaya daga cikin abinda take tsoro fiye da hasashen mai karatu, sai kuma duhu. Waɗan nan abubuwan ko a tunani batason tunasu suna tayar mata da hankali. Hakan yasa hannunta har karkarwa yake wajen miƙa hannu ta amshi kofin shayin. Nanma baice da ita komai ba ya sakar mata. Tiren kayan breakfast ɗin ya ɗakko gaba ɗayansa ya ajiye saman gadon a gabanta. Bayan ya buɗe mata koma ya ɗago ya kamata tana jan allurar daya ajiye alamar so take ta ɓoye.
Da ƙyar ya iya danne dariyar data zo masa a maƙoshi. ya sake tsuke fuska yana balla mata harara. “Idanma kin ɓoye inada gomanta a ɗakina, kinga kenan kinyi na banza. Na baki 20minutes kacal naga tray ɗin nan empty”.
Hannu tasa ta sake share hawayen da suka ciko mata idanu, cikin ƙunƙunin da bazaijiba tace, ‘Tunda ga jaka rumbu uwar zira lauma an kawo maka ko’. A fili kuwa duƙar da kai ƙasa tai kamar ta ALLAH😂.
Hannunsa ya ɗora saman nata da har yanzu ke riƙe da syringe ɗin ya zare abarsa. Gefensa ya ajiye tare da gyara filos ɗin dake birjit a saman gadon ya kwanta rigingine. Wayarsa ya ɗauka ya hau dannawa tamkar ya manta da ita a ɗakin.
Ɗagowa goma Aymah zatayi harara ashirin take antaya masa. Baƙar magana kuwa da gorin hawa mata gado da yay tayi yafi sau ɗari babu ɗaya tana tunzura baki gaba. Daka ganta kasan tsoro ne fal ranta kawai da neman faɗa da tafi ƙwarewa a yi. Shi dai bai sake bi ta kanta ba duk da yana jin ƙunƙunin da takeyi da harar da take masa. Sai dai kasancewar hausa takeyi bai damu da abinda take cewarba. Da yake dama yunwar ta keji sai gashi ta shanye tea ɗin duka dan ya mata daɗi. Harko da ayyanawa take a ranta ‘Wai buzun nan ashe ya iya haɗa shayi’ (Kai wagga ɗiya ta baba malam ALLAH dai ya gyara😆😂). A sauran abincin kuwa bread kawai taci, dan yanda aka haɗashi ya mata ƙyau a ido da daɗi a baki. Wai saida ta gama ci kuma sai cewa tai, ‘ALLAH dai yasa ba arnakun nan suka yishiba na wage baki ina turawa kamar a haɗiɗiya’. (Ke dai kika sani🤣).
Ganin ta kammala Yoohan ya miƙe zaune sosai yana ajiye wayar hannunsa. Trayn ya sauke ƙasa, batare da ce mata uffan ba ya matso daf da ita sosai har suna jin saukar numfashin juna. Zabura tayi da sauri zata matsa ya riƙota. Baya buƙatar hayaniyarta a yanzu saboda jikinta yay masifar zafin zazzaɓi, shegen taurin kanta ne kawai ya hana bakinta da bai rabo da tsiwa yin shiru. Baki ta buɗe zata fara masa tijara ya mannesa da nashi tare da sake jawota ya matseta a jikinsa tsam. Ƙarfin ba ɗaya bane, hakan yasa duk mutsu-tsunta ko gezau baiyiba balle tasaran kubuta. Syringe ɗin daya ɗura ruwan allura ya ɗauka, batai auneba sai jin shigarta tayi cikin tsokar jikinta. Tabbas da bakinta baya cikin nasa ba ƴan gidan kaɗaiba har maƙwafta sai sunsan ta kwana a gidan yau. Dan allurar malaria ce daya fahimci shike saka mata zazzaɓin yay mata, allurar kam tana da azabar zafi, dan saita ratsa kowacce kafar magudanar jini da ɓargon mutum kafin a hankali ta fara bashi nutsuwa.
Wani irin mugun ƙanƙamesa tayi jikinta na rawa. Harma ya zare allurar yana murza mata wajen bata dawo hayyacinta ba. Bakinsa ya janye a cikin nata a hankali yana sauke wani wahalallen numfashi da gajerun ajiyar zuciya a jere. Itakam kuka ta fashe da shi jin ta samu bakinta, sai ƙara ƙanƙamesa take kamar zata koma masa ciki saboda yanda zafin allurar ke gauraye duk jikinta. Haɓarsa ya ɗaura saman kanta yana ɗan murmushi da lumshe idanunsa. Hannayensa a bayanta yana shafawa a hankali alamar lallashi.
Sun sami tsahon mintuna biyar a haka sannan ta tureshi da ƙarfi tana janye jikinta baya. Cikin kuka kashirɓan tace, “Wlhy sai ALLAH ya mana hisabi da kai tun a duniyarnan tasa. tunda ai cakai idan naci abincin bazaka minba shine ka karya alƙawari. Na rantse saina faɗama Abbana” ta goge bakinta da bargo tana cigaba da faɗin, “Ƙazami kawai mayen bakin mutane”.
Shi dai komai baice mataba. Kallonta kawai yake da narkakkun idanunsa masu cikar gashi da haske. Tana cigaba da masifarta da goge baki yaga ta fara ajiyar zuciya da lumshe idanu alamar gyangyaɗi. Basuyi mintuna bakwai ba a haka ta ɓingire barci. Kansa yaɗan girgiza kawai. A kan laɓɓansa ya furta “Yeyyey girl, mai bakin tsiwa”.
Sauka yay daga kan gadon ya zagaya ɗayan gefen gadon data koma tun turesa da tayi. Kwanciyar ya gyara mata, ya fara ƙoƙarin zare hijjabin jikinta. Amma kasancewar barcin baiyi nisa ba, sai ta shiga ture masa hannu cikin kasala irin ta mai barci. Durƙusawa yay gaban gadon ya riƙe hannun nata cikin nasa. idanunsa ƙyam akan ƙyaƙyƙyawar fuskarta da komai ya dace da ita. Bata zare hannun nataba daga cikin nasa tabbacin barcin ya fara nauyi. Sai ajiyar zuciya da take faman saukewa a jajjere. Sai da ya ƙara bata mintuna kusan uku kafin ya kai dubansa ga hannunta data matse nasa. Zanen ƙunshin ya ringabi da kallo yana ɗan murzawa da babban yatsansa a hankali, abin ya masa ƙyau sosai, sai dai a ƙasan ransa tunani yake badai tattoo bane ba?. Jin ta ɗan motsa ya juyo ya kalleta. Yanda ta wani taɓe baki a cikin barcin kamar zatai kuka sai abin ya so bashi dariya. A fili ya furta “Trouble maker” yana lumshe idanunsa ya sake buɗewa a kanta.
Gudun kar hijjabin ya shaƙeta ne ya sashi cire mata shi cikin dabara. Sai kuma yaci karo da bata da riga sai zani data ɗaura. Kallo ɗaya yay mata ya janye idanunsa yaja bargon ya lulluɓa mata.
Oho, ita dai duk batasan yanayi ba, barcinta take zazzaɓin na sauka mata a hankali. Sai da ya gama bin ɗakin da kallo tsaf sannan ya fice a ransa yana yaba ƙoƙarin iyayenta. Dan ko kujerun da aka zauba musu a falon yasan kuɗi sosai aka zuba wajen sayensu.
________★★★_______
A kano ta dabo kam baƙi sun isa gida lafiya da shatara ta arziƙin da suka samu. yanzun kam gidan ya koma shiru duk baƙi sun kama gabansu, hakan yasa suma duk basu wani yi zaman awa bibbiyu ba a gidan duk suka tafi. Sai Ananah kawai da ba yaune ranar tafiyar tataba ita. Amma jikokinta da sauran ƴaƴanta duk sun koma katsina tun jiya...........✍
_Kuyi manage da wannan bajin daɗin jikina nakeba, mura tamin ram🤦🏻_.
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.
No. 47
________
I'm on Instagram as yerwaincense_and_more. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=ayfowzb2ah8k&utm_content=6k8ur6p.
INA MA’ABOTA KARATUN LITTATTAFAN HAUSA? WANDA ZAI NISHADANTAR DAKU, YA FADAKAR, YA KUMA TSUNDUMA KU A KOGIN LOBAYYAR KAUNA? TO KU MATSO KUSA... DOMIN MUNZO MUKU DA ALBISHIR DIN WANI GANGARIYAR LITTAFI.. DAYA NE TAMKAR DA DUBU.. YAZO DA WANI SALO NA DABAN WANDA ZAI SANYAYA ZUKATAH.._
_LITTAFIN *UNCLE NE...* LITTAFI NE FIRST OF ITS KIND, DA YAZO A WANNAN SHEKARA TA 2021. AN BAJE KOLIN BASIRA A BOOK DIN UNCLE NE.._
_”Wait... Dakata hafsat Rano, Kina nufin NIMCYLUV, dai shararriyar murubuciyar nan itace tazo da wani salon rubutun..?..”_
_”Kede bari Billyn Abdul.. Tsaya kiji kanun labarin a tak’aice..*NIMCYLUV* Tace book din a ta’kaice labarin *UNCLE NE* ne yana tafe:_