Sashe 122
Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kamar yanda Hajjo tai alƙawari da yamma kuwa sai ta shiga gidan su Hamisu wajen mahaifiyarsa Iyami. Sosai Iyami ta dinga haba-haba da hajjo duk da kuwa kasancewar su maƙwafta. Amma da yake ba ɗabi'ar shige-shigence da suba inba da ƙwaƙwaran dalili ba, sai yazam duk randa akaga juna kamar baƙi.
Bayan sun gaisa hajjo tasha ruwan da Iyami ta kawo mata duk da ba ƙishin take jiba, sai dai a cewarta ruwan zuminci yafi zuma garɗi. “Yauwa Iyami nasan kinata mamakin ganina da maraicen nan. To dama ba wani abune ya sani fitarnan ba ta gabannin magriba sai takwarata ƴar jikalleta Zainabu da aka kai Abuja”.
Iyami dake murmushi tace, “Oh ALLAH sarki Nu'aymah amarya zaki cemin, inadai fatan suna nan lafiya ko?”.
“Ah lafiya lau suke sai alkairi kam. Mijin ne dama ya kira wai a nema mata mai aiki daga nan, shine nace to bara nazo da kaina wajenki ƙila ta hanyarki a samo wata mai hankali. Danni ƴan aikin gidan nan namu yanzu tsoro al'amarinsu ke bani wlhy Iyami. Kuma kinsan duk deluwa ce dama take kawo manasu gashi ALLAH yay mata rasuwa”.
“To hajjo babu damuwa. Tunda har kika zaɓeni nikuwa insha ALLAH zan samoma Nu'aymah mai aiki ƴar gaske wadda baza'ayi kuka da ita ba. Duk da dai yanzu kinsa al'amarin mutanen namune sai dai addu'a. Baka fiya ganin abinda ke cikin zuciyar mutum ba a fuskarsa. Sai dai muce ALLAH ya datar damu”.
“To amin dai Iyami. Lamarin bani adama kam na wannan rikitaccen zamani sai godiyar ALLAH kawai. Yanzu dai sai a bincika mana ɗin daga nan zuwa kwana biyu. Amma sai a samo mana ƴar babba ko tunda kinga ba'a haɗa Zainabu da sha katafi irinta ba. Wadda dai idan tayi ba daidaiba za'a tsawatama yaro a kuma ɗorasa akan hanyar data dace”.
“Eh gaskiya kam hajjo, aiko indaima hakane bari zuwa anjima idan cikin su Hamisu wani ya ya shigo sai na saka su kira min Uwaliya idan zatayi, ƴar wajen yafendona ce acan wudil, mijinne ya tafi da ita can kudu da yake ɗansanda ne ya gama wajigo rayuwarta shine fa ya turota da takardar saki har uku. Shekara biyu kenan wani auren ya gagara abu kamar na magani”.
Hajjo daba cika son irin waɗannan ƙananun maganar tayiba ta miƙe tana faɗin, “Ai ɗan adam sai ki barsa kawai Iyami, ALLAH dai ya ƙyauta ya shiryrmu mu da halinmu”.
“Amin dai to”.
Iyami ta faɗa badan taso firar ta tsaya iya haka ba. Daga haka hajjo tai mata sallama ta dawo gidan dan anata haramar fara kiraye-kirayen sallar magriba ma.
_________★★★★_________
*_SUNDAY MORNING_*
Washe gari ta kama Sunday. Gaba ɗaya ahalin gidan sun tashi ne da shirin tafiya church kamar yanda suka saba. Papa ya riga kowa fita shida bodyguard ɗinsa. Aymah da batasan hidimar da sukeyi ba tana tsaka da mopping a falo akai knocking ƙofa. Batare da ta damu da sanin wanene ba ta nufi ƙofar zata buɗe. Dan akwai hijjab ƙarami a saman kayan barcin jikinta.
Momy ce cikin shiga ta alfarma, anci uban kwalliya kamar zataje gasar ƙyau. Abraham biye da ita shima cikin gayunsa. Kamar zata shareta karta gaisheta sai kuma tace, “Good Morning”. Bata saurari amsarta ba tai gaba abinta. Haka kawai itadai Madam Chioma batai mataba, badan mahaifiyar Yoohan bace ba da lallai zamansu a waje ɗaya zai iya haifar da matsaloli, dan a rayuwarta ta tsani wulaƙanci koda a wajen babba ne.
Da harara Momy ta raka bayan Aymah data koma kan aikinta batare da ta sake bi takansu ba. Ɗakin Yoohan kai tsaye ta nufa Abraham biye da ita. Sai dai koda ta tura ƙofar suka shiga sai taga wayam. Jikin ƙofar toilet taje nanma babu wani motsi, ta tura ƙofar ta leƙa babu kowa a ciki, amma dai da alama anyi amfani da shi babu jimawa. Tunanin ko yana ɗakin motsa jikinsa ne ya sata fitowa ta nufi can. Lokacin Aymah tana dining tana aikinta ko kallonsu batayi ba. Canma babu Yoohan, babuma alamar yau ya shigo wajen dan komai tsaf yake.
“K ina my son?”.
Nu'aymah taji muryar Momy a bazata. Ɗago dara-daran idanunta dake saka tsigar jikin Momy tayi tana kallonta. A yanayin halin ko-inkula tace, “Nima ban gansa ba tunda na tashi”. Daga haka ta ɗauki botikin ruwan mopping ɗinta ta nufi ɗakin Yoohan ɗin danta gyara tunda taji baya a ciki.
Cike da takaici Madam Chioma ta bita da harara, kafin taja hannun Abraham su fice. Fita tai harabar gidan, dan sauranma duk sun fita harma sun shishshiga motoci.
Guards ɗin Yoohan ɗin ta shiga tambaya ko sunga fitarsa?. Solomon ya bata amsa da cewar ya fita tun ɗazun ma, sunce zasu bisa yace baya buƙata. Ranta a ɓace tace, “Baku da hankali, sau nawa nake jaddada muku kubar barinsa yana fita shi kaɗai?. Da wace motama ya fita tunda naga duk ga motocinsa?”.
Kan Solomon a ƙasa yace, “Sorry maa. Babu yanda banyiba koni kaɗaima na bisa amma yaki, a mashin ya fita kuma”.
Wani shegen ihu ta buga tana ambaton “Jesus!!. Da wannan uban iskan safiyan kuka barshi ya fita a mashin dan ku kidahumai ne? idan Asthma ɗinsa ya tashi fa?”. Duk yanda sukaso ta fahimci ba laifinsu bane sam taƙi. Ihunta sai da yasa harsu Gebrail da suka shiga cikin mota duk suka fito. Nu'aymah kanta dake can sama sai da ta jiyo, hakan yasata buɗe Window ɗin bedroom ɗin Yoohan tana leƙosu. Ba ƙaramin dariya madam Chioma ta bataba yanda taketa faman tsalle da bala'i harta yadda takalman gayun nata saboda jarabar da takema guards ɗin Yoohan. Dariya sosai Aymah tasha harda hawaye, a ranta tana sake jinjina hauka da rashin kangado irin na waɗannan mutanen. Danma batasan akan mi madam Chioma ke bala'in bane😂.
Jin gidan yayi tsitt bayan gama bala'in madam Chioma da wucewarsu sai tunanin maganar hoto ta dawo mata a cikin rai. Tabbas wannan shine lokacin da take da shi akan hakan tunda taga duk sun fice kamar maigadi ne kawai aka bari. Sai dai bata sani ba ko hadda duk masu aikin gidan. Sannan kuma bataga Miracle ba ma a amasu tafiyar.
Ɗakinta ta koma tai wanka a gurguje. Shiryawa tai cikin doguwar rigar jallabiya blue. A falo ta zauna danta karya saboda yunwa dake cinta. Jiya tayi barci da wuri bataci abinci ba, duk da ma har yanzun ta kasa sakin jiki da abincin gidan sam. Ta gwammace zaman cin kayan ƙwalam ɗin da Yoohan ya ajiye. Aiko dukta kusan ganin ƙarshensu batare da ya sani ba.
Yanzun ma madara ta haɗa da kauri tai zaman shan Cornflakes hankalinta kwance. Tana sha tana tunanin hanyar shiga sashen papa ɗakko hoton nan, a gefen zuciyarta kam cike da fargabar ALLAH yasa bai ƙona ɗin ba. Wannan tunanin ne ya saka cornflakes ɗin fita mata a rai ma. Ta ture bowl ɗin gefe tana miƙewa. Bedroom ɗinta ta koma ta leƙa harabar gidan ta Window, sai da ta tabbatar babu motsin kowa sai maigadi kawai sannan ta rufe glass ɗin a hankali.
A falon gidanma bataga motsin kowa ba, hakama sama ko ina shiru ƙofofin bedrooms ɗin duk a rufe. Duk da haka batayi gangancin yin komai kai tsaye ba. Ta sauka downstairs ɗin ta shiga kitchen kamar zata ɗakko wani abu. Babu kowa a kitchen ɗin tabbacin da Blessing aka tafi. Ƙofar da zata kaika bayan gidan ta buɗe ta kitchen ta fito, nanma shiru babu kowa. Ta sake dawowa cikin jin daɗi ta haye upstairs ɗin. Ɗakin da take da tabbacin nasu Miracle ne ta nufa, tunkan ta ƙarasa jikin ƙofar sosai tajiyo minsharin Miracle dake barci. A hankali ta tura ƙofar ɗakin ta leƙa kanta. Kan gado ta hangota a cikin bargo, ga kafarta data sha ɗaurin bandage taɗan leƙo, key ɗin ƙofar dake ta ciki ta zaro a hankali, sannan taja ƙofar ta kulle mira ta waje.
Lumshe idanu tayi a hankali tana karanto addu'oin neman nasara. Daga haka ta nufi sashen papa da addu'ar ALLAH yasa a buɗe yake. Cikin sa'a kuwa tana tura ƙofar sai gashi ta buɗe. Nannauyan numfashi ta sauke da turawa gaba ɗaya ta shiga corridor ɗin. Ƙofar falon ma ta sameta buɗe, nanma ta shige cike da ɗoki.
Koda wasa batai tunanin tsayawa a falon ba, dan tasan yanda papa ya nuna muhimmancin hoton nan bazai yarda ya ajiyesa anan ba sai dai bedroom. Bedroom ɗinma dai a buɗen ta samesa. Da alama ma ko gyara bai samu ba dan gadon duk a curkuɗe yake. Bata damu da wannan ba. Ta fara buɗe-buɗen bedside drawer farko tana ɗaɗɗaga abubuwan ciki. A duka biyun bata sami hotonba. Dan haka tabar nan ta juya kan Wadrobe ɗin kaya. Sai dai koda ta buɗe ma sai ta rasa da ina ya kamata ta fara?. Sunan ALLAH ta shiga ambata tana ɗaɗɗaga duk abinda taci karo da shi. Amma babu alamar wannan hoto. Harta sare da tunanin kodai ya ƙona. Sai idanunta suka sauka kan wani ɗan kanta dake can gefe da tarin littatafai da takardu. Nanma zuwa tai tanata ɗagawa ɗaya bayan ɗaya sai dai babu anan ma.
Kanta ta dafe hawaye na ciko mata idanu dan takaici, tabbas yanzu kam tama yarda ya riga da ya ƙona kenan?. Zuciyarta ce ta ayyana mata ƙasan gado. Saurin nufar gadon tayi. sai dai tana ɗora hannunta a kai tajiyo dariyar Papa a falo yana faɗin, “Kai! Kai kai gaskiya kamin bazata Andrew, da alama ka matsu da kayan nan kam gaskiya”. Dariya wanda ya kira Andrew taji yayi shima, cikin harshen turancin yake faɗin, “Mr Goshpower bazaka ganeba ne, kuɗi masu nauyi ne na hango mana shiyyasa zuciyata ta kasa zama waje guda duk da nasan kana church a irin wannan lokacin”.
Wata shegiyar dariya Papa ya kece da ita yana nufar hanyar bedroom ɗinsa, “Ai kai indai akan kuɗine zakama iya saka kanka a kowane kalar haɗari, shiyyasa kaga bana wasa da al'amarinka”. Ya ƙare maganar yana ƙarasa tura ƙofar bedroom ɗin da Aymah ke a ciki ya shi🙆🏻............✍
Hannuna ya firgita ya gaza aikinsa😱🙆🏻.
_____________________________
ZAFAFA BIYAR 2021
_______________________
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Bayan sun gaisa hajjo tasha ruwan da Iyami ta kawo mata duk da ba ƙishin take jiba, sai dai a cewarta ruwan zuminci yafi zuma garɗi. “Yauwa Iyami nasan kinata mamakin ganina da maraicen nan. To dama ba wani abune ya sani fitarnan ba ta gabannin magriba sai takwarata ƴar jikalleta Zainabu da aka kai Abuja”.
Iyami dake murmushi tace, “Oh ALLAH sarki Nu'aymah amarya zaki cemin, inadai fatan suna nan lafiya ko?”.
“Ah lafiya lau suke sai alkairi kam. Mijin ne dama ya kira wai a nema mata mai aiki daga nan, shine nace to bara nazo da kaina wajenki ƙila ta hanyarki a samo wata mai hankali. Danni ƴan aikin gidan nan namu yanzu tsoro al'amarinsu ke bani wlhy Iyami. Kuma kinsan duk deluwa ce dama take kawo manasu gashi ALLAH yay mata rasuwa”.
“To hajjo babu damuwa. Tunda har kika zaɓeni nikuwa insha ALLAH zan samoma Nu'aymah mai aiki ƴar gaske wadda baza'ayi kuka da ita ba. Duk da dai yanzu kinsa al'amarin mutanen namune sai dai addu'a. Baka fiya ganin abinda ke cikin zuciyar mutum ba a fuskarsa. Sai dai muce ALLAH ya datar damu”.
“To amin dai Iyami. Lamarin bani adama kam na wannan rikitaccen zamani sai godiyar ALLAH kawai. Yanzu dai sai a bincika mana ɗin daga nan zuwa kwana biyu. Amma sai a samo mana ƴar babba ko tunda kinga ba'a haɗa Zainabu da sha katafi irinta ba. Wadda dai idan tayi ba daidaiba za'a tsawatama yaro a kuma ɗorasa akan hanyar data dace”.
“Eh gaskiya kam hajjo, aiko indaima hakane bari zuwa anjima idan cikin su Hamisu wani ya ya shigo sai na saka su kira min Uwaliya idan zatayi, ƴar wajen yafendona ce acan wudil, mijinne ya tafi da ita can kudu da yake ɗansanda ne ya gama wajigo rayuwarta shine fa ya turota da takardar saki har uku. Shekara biyu kenan wani auren ya gagara abu kamar na magani”.
Hajjo daba cika son irin waɗannan ƙananun maganar tayiba ta miƙe tana faɗin, “Ai ɗan adam sai ki barsa kawai Iyami, ALLAH dai ya ƙyauta ya shiryrmu mu da halinmu”.
“Amin dai to”.
Iyami ta faɗa badan taso firar ta tsaya iya haka ba. Daga haka hajjo tai mata sallama ta dawo gidan dan anata haramar fara kiraye-kirayen sallar magriba ma.
_________★★★★_________
*_SUNDAY MORNING_*
Washe gari ta kama Sunday. Gaba ɗaya ahalin gidan sun tashi ne da shirin tafiya church kamar yanda suka saba. Papa ya riga kowa fita shida bodyguard ɗinsa. Aymah da batasan hidimar da sukeyi ba tana tsaka da mopping a falo akai knocking ƙofa. Batare da ta damu da sanin wanene ba ta nufi ƙofar zata buɗe. Dan akwai hijjab ƙarami a saman kayan barcin jikinta.
Momy ce cikin shiga ta alfarma, anci uban kwalliya kamar zataje gasar ƙyau. Abraham biye da ita shima cikin gayunsa. Kamar zata shareta karta gaisheta sai kuma tace, “Good Morning”. Bata saurari amsarta ba tai gaba abinta. Haka kawai itadai Madam Chioma batai mataba, badan mahaifiyar Yoohan bace ba da lallai zamansu a waje ɗaya zai iya haifar da matsaloli, dan a rayuwarta ta tsani wulaƙanci koda a wajen babba ne.
Da harara Momy ta raka bayan Aymah data koma kan aikinta batare da ta sake bi takansu ba. Ɗakin Yoohan kai tsaye ta nufa Abraham biye da ita. Sai dai koda ta tura ƙofar suka shiga sai taga wayam. Jikin ƙofar toilet taje nanma babu wani motsi, ta tura ƙofar ta leƙa babu kowa a ciki, amma dai da alama anyi amfani da shi babu jimawa. Tunanin ko yana ɗakin motsa jikinsa ne ya sata fitowa ta nufi can. Lokacin Aymah tana dining tana aikinta ko kallonsu batayi ba. Canma babu Yoohan, babuma alamar yau ya shigo wajen dan komai tsaf yake.
“K ina my son?”.
Nu'aymah taji muryar Momy a bazata. Ɗago dara-daran idanunta dake saka tsigar jikin Momy tayi tana kallonta. A yanayin halin ko-inkula tace, “Nima ban gansa ba tunda na tashi”. Daga haka ta ɗauki botikin ruwan mopping ɗinta ta nufi ɗakin Yoohan ɗin danta gyara tunda taji baya a ciki.
Cike da takaici Madam Chioma ta bita da harara, kafin taja hannun Abraham su fice. Fita tai harabar gidan, dan sauranma duk sun fita harma sun shishshiga motoci.
Guards ɗin Yoohan ɗin ta shiga tambaya ko sunga fitarsa?. Solomon ya bata amsa da cewar ya fita tun ɗazun ma, sunce zasu bisa yace baya buƙata. Ranta a ɓace tace, “Baku da hankali, sau nawa nake jaddada muku kubar barinsa yana fita shi kaɗai?. Da wace motama ya fita tunda naga duk ga motocinsa?”.
Kan Solomon a ƙasa yace, “Sorry maa. Babu yanda banyiba koni kaɗaima na bisa amma yaki, a mashin ya fita kuma”.
Wani shegen ihu ta buga tana ambaton “Jesus!!. Da wannan uban iskan safiyan kuka barshi ya fita a mashin dan ku kidahumai ne? idan Asthma ɗinsa ya tashi fa?”. Duk yanda sukaso ta fahimci ba laifinsu bane sam taƙi. Ihunta sai da yasa harsu Gebrail da suka shiga cikin mota duk suka fito. Nu'aymah kanta dake can sama sai da ta jiyo, hakan yasata buɗe Window ɗin bedroom ɗin Yoohan tana leƙosu. Ba ƙaramin dariya madam Chioma ta bataba yanda taketa faman tsalle da bala'i harta yadda takalman gayun nata saboda jarabar da takema guards ɗin Yoohan. Dariya sosai Aymah tasha harda hawaye, a ranta tana sake jinjina hauka da rashin kangado irin na waɗannan mutanen. Danma batasan akan mi madam Chioma ke bala'in bane😂.
Jin gidan yayi tsitt bayan gama bala'in madam Chioma da wucewarsu sai tunanin maganar hoto ta dawo mata a cikin rai. Tabbas wannan shine lokacin da take da shi akan hakan tunda taga duk sun fice kamar maigadi ne kawai aka bari. Sai dai bata sani ba ko hadda duk masu aikin gidan. Sannan kuma bataga Miracle ba ma a amasu tafiyar.
Ɗakinta ta koma tai wanka a gurguje. Shiryawa tai cikin doguwar rigar jallabiya blue. A falo ta zauna danta karya saboda yunwa dake cinta. Jiya tayi barci da wuri bataci abinci ba, duk da ma har yanzun ta kasa sakin jiki da abincin gidan sam. Ta gwammace zaman cin kayan ƙwalam ɗin da Yoohan ya ajiye. Aiko dukta kusan ganin ƙarshensu batare da ya sani ba.
Yanzun ma madara ta haɗa da kauri tai zaman shan Cornflakes hankalinta kwance. Tana sha tana tunanin hanyar shiga sashen papa ɗakko hoton nan, a gefen zuciyarta kam cike da fargabar ALLAH yasa bai ƙona ɗin ba. Wannan tunanin ne ya saka cornflakes ɗin fita mata a rai ma. Ta ture bowl ɗin gefe tana miƙewa. Bedroom ɗinta ta koma ta leƙa harabar gidan ta Window, sai da ta tabbatar babu motsin kowa sai maigadi kawai sannan ta rufe glass ɗin a hankali.
A falon gidanma bataga motsin kowa ba, hakama sama ko ina shiru ƙofofin bedrooms ɗin duk a rufe. Duk da haka batayi gangancin yin komai kai tsaye ba. Ta sauka downstairs ɗin ta shiga kitchen kamar zata ɗakko wani abu. Babu kowa a kitchen ɗin tabbacin da Blessing aka tafi. Ƙofar da zata kaika bayan gidan ta buɗe ta kitchen ta fito, nanma shiru babu kowa. Ta sake dawowa cikin jin daɗi ta haye upstairs ɗin. Ɗakin da take da tabbacin nasu Miracle ne ta nufa, tunkan ta ƙarasa jikin ƙofar sosai tajiyo minsharin Miracle dake barci. A hankali ta tura ƙofar ɗakin ta leƙa kanta. Kan gado ta hangota a cikin bargo, ga kafarta data sha ɗaurin bandage taɗan leƙo, key ɗin ƙofar dake ta ciki ta zaro a hankali, sannan taja ƙofar ta kulle mira ta waje.
Lumshe idanu tayi a hankali tana karanto addu'oin neman nasara. Daga haka ta nufi sashen papa da addu'ar ALLAH yasa a buɗe yake. Cikin sa'a kuwa tana tura ƙofar sai gashi ta buɗe. Nannauyan numfashi ta sauke da turawa gaba ɗaya ta shiga corridor ɗin. Ƙofar falon ma ta sameta buɗe, nanma ta shige cike da ɗoki.
Koda wasa batai tunanin tsayawa a falon ba, dan tasan yanda papa ya nuna muhimmancin hoton nan bazai yarda ya ajiyesa anan ba sai dai bedroom. Bedroom ɗinma dai a buɗen ta samesa. Da alama ma ko gyara bai samu ba dan gadon duk a curkuɗe yake. Bata damu da wannan ba. Ta fara buɗe-buɗen bedside drawer farko tana ɗaɗɗaga abubuwan ciki. A duka biyun bata sami hotonba. Dan haka tabar nan ta juya kan Wadrobe ɗin kaya. Sai dai koda ta buɗe ma sai ta rasa da ina ya kamata ta fara?. Sunan ALLAH ta shiga ambata tana ɗaɗɗaga duk abinda taci karo da shi. Amma babu alamar wannan hoto. Harta sare da tunanin kodai ya ƙona. Sai idanunta suka sauka kan wani ɗan kanta dake can gefe da tarin littatafai da takardu. Nanma zuwa tai tanata ɗagawa ɗaya bayan ɗaya sai dai babu anan ma.
Kanta ta dafe hawaye na ciko mata idanu dan takaici, tabbas yanzu kam tama yarda ya riga da ya ƙona kenan?. Zuciyarta ce ta ayyana mata ƙasan gado. Saurin nufar gadon tayi. sai dai tana ɗora hannunta a kai tajiyo dariyar Papa a falo yana faɗin, “Kai! Kai kai gaskiya kamin bazata Andrew, da alama ka matsu da kayan nan kam gaskiya”. Dariya wanda ya kira Andrew taji yayi shima, cikin harshen turancin yake faɗin, “Mr Goshpower bazaka ganeba ne, kuɗi masu nauyi ne na hango mana shiyyasa zuciyata ta kasa zama waje guda duk da nasan kana church a irin wannan lokacin”.
Wata shegiyar dariya Papa ya kece da ita yana nufar hanyar bedroom ɗinsa, “Ai kai indai akan kuɗine zakama iya saka kanka a kowane kalar haɗari, shiyyasa kaga bana wasa da al'amarinka”. Ya ƙare maganar yana ƙarasa tura ƙofar bedroom ɗin da Aymah ke a ciki ya shi🙆🏻............✍
Hannuna ya firgita ya gaza aikinsa😱🙆🏻.
_____________________________
ZAFAFA BIYAR 2021
_______________________
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋