Sashe 174
Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
_MAAB LUXURY HOME, TANA SAIDA KAYAYYAKI MASU INGANCI DA KYAWUN GASKE, AKWAI RAHUSA WANDA KOMAI KANKANTAR KUDI KANA IYA SIYAN WANI ABUN AWAJENTA, KAYANTA BA SAI MASU KUDI BA, KOWA YANA IYA GARZAYAWA YA SIYO NASA, ABUBUWAN DA YAWA, KAYAN DAGA CIKI AKWAI IRIN SU:_
_DINNER SETS, SERVING TRAYS, CUTLERY SETS, JUGS, FOOD FLAKS, THERMO FLASKS. DA SAURAN SU ABUBUWAN HOME DECOR._
_DOMIN NEMAN/TUNTUBAR KAYAYYAKIN *MAAB LUXURY HOME*, GA DETAILS DIN KAMAR HAKA: _
_INSTAGRAM: MaabLuxury home._
_WhatsApp number: +491521 4642007_
_Facebook: Maab Luxury Home_
_Adireshin su na yanar gizo: maabluxury.com_
_suna garin KANO. Amman suna tura kayayyakin su ko ina a fad’in nigeria. _
_KYAU, INGANCI, RAHUSA... SAI MAAB LUXURY HOME_
______________
No. 69
............“Oh God baby”. Ya faɗa da kamota ya tayar zaune. Sakata yayi cikin jikinsa ya rungumeta. A tare suka sauke ajiyar zuciya kowa kewar ɗan uwansa na ratsashi.
Sake lafewa tai a jikin nasa tana mai shaƙar ƙamshinsa da ke mata daɗi sosai. Yayinda shi kuma ɗumin jikinta ke ratsashi, tare da tausayinta har ƙasan zuciyarsa. Harga ALLAH yana matuƙar son yara. Musamman a yanzu da yayi aure. Badan hakaba daya cire mata cikin nan dan tayi ƙanƙanta yake gani. Duk da kuwa shi likitane daya zaga cikin duniya. Yayi gamo da mutane iri-iri harma waɗanda basu kaita a shekaruba ya gansu da cikin kuma sun haihu lafiya.
Jin tana neman fara barci ya shafa mata fuska. Idanun ta buɗe a hankali da ɗagowa ta kallesa. Sai kuma ta bi jikinsa da kallon mamaki. Sanye yake cikin wata ɗanyar shadda ash color mai duhu. Tasha ɗinkin da yay dai-dai da samarin wannan zamanin. Hardasu hula ƙube. A bazata murmushi ya suɓuce mata. Ta sake kwantawa a jikinsa da zagayesa da hannayenta tana murmushi.
“Hausa man”. Ta faɗa cike da shauƙi.
Murmushi yayi mai faɗi ganin taji daɗin ganinsa da shigar yarenta. Ya miƙe ɗauke da ita yana ƴar dariya da faɗin, “Hausa man mijin hausa girl”. Dariya suka ƙyalƙyale da shi a tare, dan yanda yay maganar dole ya baka dariya. Ta kai hannu kan tattausan sajensa dai-dai yana zama da ita a kujerar. Tace, “Mun haɗu fa da yawa. Dan irinmu a tarihi kaɗanne”.
Murmushi ya sakeyi mai faɗi yana lumshe ido da buɗewa a kanta. Zai bata amsa kira ya shigo wayarsa. Karkatawa yay kaɗan ya ciro wayar a aljihun gefensa. Hakanne ya bama Aymah damar sauka dan ta tuna ko ruwa bata bashi ba. Da kallo ya bita yana sauke wani nannauyan numfashi da har ya kai Osin jinsa da ga can.
Cikin son ƙarfafa kanta ta haɗa masa ruwa da kofi a ƙaramin tire. Duk da ta fahimci bai cika damuwa da kayan lemo-lemon nan ba ta ɗauka masa shima. Falon ta dawo inda ta barsa har yanzu yana waya. Ta ajiye tiren a table taɗan kallesa. Shima idanunsa ƙyam akanta. Lemo ta fara nuna masa, ya girgiza mata kai alamar a'a. Hakan yasa ta buɗe ruwa. Koda ta miƙo masa sai ya haɗa da hannunta ya maidata saman cinyarsa. Jin numfashin daya furzar ya saka Osin faɗin, “Mr X anya kuwa kana cikin nutsuwarka?. Nikam sai anjima. Ina magana kanata min uhm, ah, a'a”.
Murmushi Yoohan yayi mai sanyi yana kai hancinsa bisa dokin wuyan Nu'aymah. Osin bai jira amsarsa ba ya yanke wayar cike da jin haushi dan magana dama yake masa akan su papa. Shi kuma harga ALLAH Yoohan hankalinsa gaba ɗaya Aymah ta tattareshi kojin Osin ɗinma bayayi da ƙyau.
“Yah Yoohan zakasa na jiƙamu fa”. Ta faɗa cike da shagwaɓa”. Tai maganar tana ɗan ture masa kai Jin yana neman ruɗar mata da jiki. Bai iya cemata komaiba. Dan a kallo ɗaya zaka fahimci ta gama narkar da shi. Ya kamo hannunta da ruwan ke ciki ya kai bakinsa kozai samu sassauci. Dama gashi ƙishin yakeji. Tas kuwa ya shanye shi.
“A ƙaro?”.
Kai ya girgiza mata da lumshe idanu yana jingina kansa da kujera.
Gaba ɗaya ƙoƙarin Nu'aymah neman gazawa yakeyi, cike da son danne halin da take ciki tace, “Muje kayi wanka ga abinci ma”.
Idanun ya buɗe ya zuba mata su. Dan ya fahimci tanayin komai da ƙarfin haline. Yanzu haka har cikin jikinsa jin zafin nata jikin ya keyi. Baice komaiba ya kamata ya miƙar yana faɗin, “Fara bani abincin naci yu nwa nakeji”.
Koda suka zauna a dining ɗin duk sai taji batason ganin abincin kuma duk da itace ta girkashi. Fahimtar hakan da Yoohan yayi ya sashi cemata taje ta kwanta zai zuba. Da sauri kuwa tabar wajen. Binta yay da kallon tausayi, tana ƙoƙarin kwanciya a ƙasa yay saurin faɗin, “No ba ƙasaba. Koma saman kujera ko kije ɗaki”.
Sosai ta ɓata fuska zatai kuka. “Please Yah Yoohan, wlhy banason ko ina sai nan. Yafi min daɗi”.
“Bazai yuwuba Sweet girl, wannan sanyin illane a gareku ai. Indai kika kwanta a wajen nan tofa na fasa baki maganin zazzaɓi kawai zan haɗa da allura....”
Kafinma ya rufe baki ta haye saman kujera tana hawaye. Murmushi ya ɗanyi ganin yanda ta kwanta da juya masa baya. Bai sake yin maganaba ya hau cin abincinsa yana yabama ƙoƙarin ta, dan shikam yanzu ya sallama mata akan iya girki kuma.
Juye-juye Aymah ta dingayi a kujerar tana ƙunƙunin, sam kwanciyar batai mata daɗi ba, ita tafi son ƙasan saboda sanyin tiles. Yoohan dai na kallonta amma baice komaiba. Sai da ya kammala cin abincinsa hankali kwance sannan ya miƙe. Dan yama tuna kaya na waje. Zuwa yay ya shigo da su duka. Duk da Nu'aymah na jinsa bata juyo ta kallesaba. Cike take da haushin an hanata kwanciya a ƙasa. Babban akwatin kayanta da yazo da shi ya kai ciki, ghana must go ɗin kuwa ya barta anan falon dan baisan mine a ciki ba. Amma yanda yakeji ƙamshi-ƙamshin abubuwa yasan dai ba kaya bane. sannan akwai nauyi ma.
Cak ya ɗauki Aymah daga kujerar ya nufi bedroom da ita. Ƙin motsawa tai, sai ma fuska data kumbure na fushi. Shi dai baice komaiba ya kwantar da ita a gado yana sumbatar goshinta. Daga haka ya cire kayansa ya wuce toilet yin wanka.
Koda ya fito ya sameta a gadon bata sauka ba yaji daɗi. Dan baiyi zaton zata haƙura ba. Boxer kawai ya saka ya haye gadon, yanason yaɗan huta daga uwar gajiyar daya kwaso a sati biyun nan.. Sai yanzu ne ya fahinci ashe barci ƴar rigimar tasa tayi, yay murmushi mai ƙayatarwa da sumbatar laɓɓanta da idanu. ‘My Trouble maker an kusa zama mah-mah’ yay maganar yana ɗaga rigarta da ƙara faɗaɗa murmushinsa. Sunkuyawa yay ya sumbaci cikin da babu alamar akwai wata hallita a ciki. Sannan ya fara magana tamkar jinsa ya keyi, “Little boss how are you?. ALLAH ya kareki. ya fiddoki duniya lafiya, yasa kizam mahaddaciyar Al-qur'ani kaman Mie-mien ki. Ki kumayo kamanninta”. ya ƙarasa faɗa da ɗaga kai yana kallon fuskar Aymah dake barci batasan yanayi ba. Kwanciyarsa ya gyara da rungumeta. Kamar kuwa jira take sai ta sake lafewa dan sanyin jikinsa.
Barci sukasha sosai. Sai dai Alhmdllh lokacin da suka tashi zazzaɓin Aymah ya sauka. Tare sukayi wanka bayan Yoohan ya mata gwajin fitsarin da batasan na minene ba. Tsabar wauta kuma bata tsaya tambayarsaba. Ta zata dai ko complain ɗin maganar rashin ganin jinin da sukayi da Umm ne ta sanar masa tunda shi Doctor ne. (Umm ba irinki bace madam😬).
Ta rigashi fitowa. Dan sai da ya jira result sannan ya fito. Duk da ya jima da zargin ɗan tayinsa hakan bai hanashi farin cikiba. Ya ɗagata yanata juyi da ita. Tun tana tambayarsa lafiya harta koma tuntsura dariya kamar yanda yakeyi. Da ƙyar ta samu ya sauketa a godo suna faman hakki.
Yasha murnarsa batare da Aymah tasan dalilinta ba. Dan ya ƙi sanar mata. Acewarsa ba yanzunba. Duk da taso tajin saita share kawai. Musamman da ganin ɗinkinan daya yo mata cike da akwati. Lesss, shadda, atamfa. Dan a cewarsa yana son ganinta a kayan hausawa sosai. Tayi mamakin ganin ɗinkin dai-dai jikinta kuma. Koda ta tambayesa yaya akai yasan seize ɗinta haka? Sai cewa yayi abun sirri ne. Ta fahimci yau jan rai yake mata akan magana. Nanma sai ta share ta shiga jera masa godiya da addu'oi.
Ya ce shifa tabar masa godiya dan akwaima lefenta a kansa wanda baiyiba. Aymah dake dariya tace, “Ai gashi anan kayi my boo”.
Hancinta ya lakace da faɗin, “No. Wancan special ne hausa girl. taso muje kiga saƙon Umm”.
Tunda Aymah taga duk abinda tacema Umm an haɗo mata shi saita haukace da murna har Yoohan na mata dariya. Ta tasa fara gaba ta hau ci harta bashi tausayi. Dan yayi-yayi taci abinci taƙi, tace sai dai suje shagon shan coffee. Haka dole bayan ta gama cin farar da shan su alawar madara ya ɗauketa sukaje shan coffee ɗin. Tako shawosa bana wasaba harda guzirin na anjima. Shi dai gaba ɗaya sai take bashi tausayi, dan yasan da bata shan coffee.
_DINNER SETS, SERVING TRAYS, CUTLERY SETS, JUGS, FOOD FLAKS, THERMO FLASKS. DA SAURAN SU ABUBUWAN HOME DECOR._
_DOMIN NEMAN/TUNTUBAR KAYAYYAKIN *MAAB LUXURY HOME*, GA DETAILS DIN KAMAR HAKA: _
_INSTAGRAM: MaabLuxury home._
_WhatsApp number: +491521 4642007_
_Facebook: Maab Luxury Home_
_Adireshin su na yanar gizo: maabluxury.com_
_suna garin KANO. Amman suna tura kayayyakin su ko ina a fad’in nigeria. _
_KYAU, INGANCI, RAHUSA... SAI MAAB LUXURY HOME_
______________
No. 69
............“Oh God baby”. Ya faɗa da kamota ya tayar zaune. Sakata yayi cikin jikinsa ya rungumeta. A tare suka sauke ajiyar zuciya kowa kewar ɗan uwansa na ratsashi.
Sake lafewa tai a jikin nasa tana mai shaƙar ƙamshinsa da ke mata daɗi sosai. Yayinda shi kuma ɗumin jikinta ke ratsashi, tare da tausayinta har ƙasan zuciyarsa. Harga ALLAH yana matuƙar son yara. Musamman a yanzu da yayi aure. Badan hakaba daya cire mata cikin nan dan tayi ƙanƙanta yake gani. Duk da kuwa shi likitane daya zaga cikin duniya. Yayi gamo da mutane iri-iri harma waɗanda basu kaita a shekaruba ya gansu da cikin kuma sun haihu lafiya.
Jin tana neman fara barci ya shafa mata fuska. Idanun ta buɗe a hankali da ɗagowa ta kallesa. Sai kuma ta bi jikinsa da kallon mamaki. Sanye yake cikin wata ɗanyar shadda ash color mai duhu. Tasha ɗinkin da yay dai-dai da samarin wannan zamanin. Hardasu hula ƙube. A bazata murmushi ya suɓuce mata. Ta sake kwantawa a jikinsa da zagayesa da hannayenta tana murmushi.
“Hausa man”. Ta faɗa cike da shauƙi.
Murmushi yayi mai faɗi ganin taji daɗin ganinsa da shigar yarenta. Ya miƙe ɗauke da ita yana ƴar dariya da faɗin, “Hausa man mijin hausa girl”. Dariya suka ƙyalƙyale da shi a tare, dan yanda yay maganar dole ya baka dariya. Ta kai hannu kan tattausan sajensa dai-dai yana zama da ita a kujerar. Tace, “Mun haɗu fa da yawa. Dan irinmu a tarihi kaɗanne”.
Murmushi ya sakeyi mai faɗi yana lumshe ido da buɗewa a kanta. Zai bata amsa kira ya shigo wayarsa. Karkatawa yay kaɗan ya ciro wayar a aljihun gefensa. Hakanne ya bama Aymah damar sauka dan ta tuna ko ruwa bata bashi ba. Da kallo ya bita yana sauke wani nannauyan numfashi da har ya kai Osin jinsa da ga can.
Cikin son ƙarfafa kanta ta haɗa masa ruwa da kofi a ƙaramin tire. Duk da ta fahimci bai cika damuwa da kayan lemo-lemon nan ba ta ɗauka masa shima. Falon ta dawo inda ta barsa har yanzu yana waya. Ta ajiye tiren a table taɗan kallesa. Shima idanunsa ƙyam akanta. Lemo ta fara nuna masa, ya girgiza mata kai alamar a'a. Hakan yasa ta buɗe ruwa. Koda ta miƙo masa sai ya haɗa da hannunta ya maidata saman cinyarsa. Jin numfashin daya furzar ya saka Osin faɗin, “Mr X anya kuwa kana cikin nutsuwarka?. Nikam sai anjima. Ina magana kanata min uhm, ah, a'a”.
Murmushi Yoohan yayi mai sanyi yana kai hancinsa bisa dokin wuyan Nu'aymah. Osin bai jira amsarsa ba ya yanke wayar cike da jin haushi dan magana dama yake masa akan su papa. Shi kuma harga ALLAH Yoohan hankalinsa gaba ɗaya Aymah ta tattareshi kojin Osin ɗinma bayayi da ƙyau.
“Yah Yoohan zakasa na jiƙamu fa”. Ta faɗa cike da shagwaɓa”. Tai maganar tana ɗan ture masa kai Jin yana neman ruɗar mata da jiki. Bai iya cemata komaiba. Dan a kallo ɗaya zaka fahimci ta gama narkar da shi. Ya kamo hannunta da ruwan ke ciki ya kai bakinsa kozai samu sassauci. Dama gashi ƙishin yakeji. Tas kuwa ya shanye shi.
“A ƙaro?”.
Kai ya girgiza mata da lumshe idanu yana jingina kansa da kujera.
Gaba ɗaya ƙoƙarin Nu'aymah neman gazawa yakeyi, cike da son danne halin da take ciki tace, “Muje kayi wanka ga abinci ma”.
Idanun ya buɗe ya zuba mata su. Dan ya fahimci tanayin komai da ƙarfin haline. Yanzu haka har cikin jikinsa jin zafin nata jikin ya keyi. Baice komaiba ya kamata ya miƙar yana faɗin, “Fara bani abincin naci yu nwa nakeji”.
Koda suka zauna a dining ɗin duk sai taji batason ganin abincin kuma duk da itace ta girkashi. Fahimtar hakan da Yoohan yayi ya sashi cemata taje ta kwanta zai zuba. Da sauri kuwa tabar wajen. Binta yay da kallon tausayi, tana ƙoƙarin kwanciya a ƙasa yay saurin faɗin, “No ba ƙasaba. Koma saman kujera ko kije ɗaki”.
Sosai ta ɓata fuska zatai kuka. “Please Yah Yoohan, wlhy banason ko ina sai nan. Yafi min daɗi”.
“Bazai yuwuba Sweet girl, wannan sanyin illane a gareku ai. Indai kika kwanta a wajen nan tofa na fasa baki maganin zazzaɓi kawai zan haɗa da allura....”
Kafinma ya rufe baki ta haye saman kujera tana hawaye. Murmushi ya ɗanyi ganin yanda ta kwanta da juya masa baya. Bai sake yin maganaba ya hau cin abincinsa yana yabama ƙoƙarin ta, dan shikam yanzu ya sallama mata akan iya girki kuma.
Juye-juye Aymah ta dingayi a kujerar tana ƙunƙunin, sam kwanciyar batai mata daɗi ba, ita tafi son ƙasan saboda sanyin tiles. Yoohan dai na kallonta amma baice komaiba. Sai da ya kammala cin abincinsa hankali kwance sannan ya miƙe. Dan yama tuna kaya na waje. Zuwa yay ya shigo da su duka. Duk da Nu'aymah na jinsa bata juyo ta kallesaba. Cike take da haushin an hanata kwanciya a ƙasa. Babban akwatin kayanta da yazo da shi ya kai ciki, ghana must go ɗin kuwa ya barta anan falon dan baisan mine a ciki ba. Amma yanda yakeji ƙamshi-ƙamshin abubuwa yasan dai ba kaya bane. sannan akwai nauyi ma.
Cak ya ɗauki Aymah daga kujerar ya nufi bedroom da ita. Ƙin motsawa tai, sai ma fuska data kumbure na fushi. Shi dai baice komaiba ya kwantar da ita a gado yana sumbatar goshinta. Daga haka ya cire kayansa ya wuce toilet yin wanka.
Koda ya fito ya sameta a gadon bata sauka ba yaji daɗi. Dan baiyi zaton zata haƙura ba. Boxer kawai ya saka ya haye gadon, yanason yaɗan huta daga uwar gajiyar daya kwaso a sati biyun nan.. Sai yanzu ne ya fahinci ashe barci ƴar rigimar tasa tayi, yay murmushi mai ƙayatarwa da sumbatar laɓɓanta da idanu. ‘My Trouble maker an kusa zama mah-mah’ yay maganar yana ɗaga rigarta da ƙara faɗaɗa murmushinsa. Sunkuyawa yay ya sumbaci cikin da babu alamar akwai wata hallita a ciki. Sannan ya fara magana tamkar jinsa ya keyi, “Little boss how are you?. ALLAH ya kareki. ya fiddoki duniya lafiya, yasa kizam mahaddaciyar Al-qur'ani kaman Mie-mien ki. Ki kumayo kamanninta”. ya ƙarasa faɗa da ɗaga kai yana kallon fuskar Aymah dake barci batasan yanayi ba. Kwanciyarsa ya gyara da rungumeta. Kamar kuwa jira take sai ta sake lafewa dan sanyin jikinsa.
Barci sukasha sosai. Sai dai Alhmdllh lokacin da suka tashi zazzaɓin Aymah ya sauka. Tare sukayi wanka bayan Yoohan ya mata gwajin fitsarin da batasan na minene ba. Tsabar wauta kuma bata tsaya tambayarsaba. Ta zata dai ko complain ɗin maganar rashin ganin jinin da sukayi da Umm ne ta sanar masa tunda shi Doctor ne. (Umm ba irinki bace madam😬).
Ta rigashi fitowa. Dan sai da ya jira result sannan ya fito. Duk da ya jima da zargin ɗan tayinsa hakan bai hanashi farin cikiba. Ya ɗagata yanata juyi da ita. Tun tana tambayarsa lafiya harta koma tuntsura dariya kamar yanda yakeyi. Da ƙyar ta samu ya sauketa a godo suna faman hakki.
Yasha murnarsa batare da Aymah tasan dalilinta ba. Dan ya ƙi sanar mata. Acewarsa ba yanzunba. Duk da taso tajin saita share kawai. Musamman da ganin ɗinkinan daya yo mata cike da akwati. Lesss, shadda, atamfa. Dan a cewarsa yana son ganinta a kayan hausawa sosai. Tayi mamakin ganin ɗinkin dai-dai jikinta kuma. Koda ta tambayesa yaya akai yasan seize ɗinta haka? Sai cewa yayi abun sirri ne. Ta fahimci yau jan rai yake mata akan magana. Nanma sai ta share ta shiga jera masa godiya da addu'oi.
Ya ce shifa tabar masa godiya dan akwaima lefenta a kansa wanda baiyiba. Aymah dake dariya tace, “Ai gashi anan kayi my boo”.
Hancinta ya lakace da faɗin, “No. Wancan special ne hausa girl. taso muje kiga saƙon Umm”.
Tunda Aymah taga duk abinda tacema Umm an haɗo mata shi saita haukace da murna har Yoohan na mata dariya. Ta tasa fara gaba ta hau ci harta bashi tausayi. Dan yayi-yayi taci abinci taƙi, tace sai dai suje shagon shan coffee. Haka dole bayan ta gama cin farar da shan su alawar madara ya ɗauketa sukaje shan coffee ɗin. Tako shawosa bana wasaba harda guzirin na anjima. Shi dai gaba ɗaya sai take bashi tausayi, dan yasan da bata shan coffee.