Sashe 132
Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A falon papa ta iske Momy na banbamin jaraba ga Abraham na sharɓar kuka. Dama ta wuto su Joy na nasu masifar a downstairs kuma tasan duk akanta ne. Kallo ɗaya papa yayma fuskarta shi kansa yaji shakkarta. Duk da kasancewarta ƙaramar yarinya kwarjinita na tada masa hankali dan kallon mahaifinta yake mata. Zama tai tana gaishesa batare data kalli ko sashen da Momy take ba. Ya amsa mata da kulawa.
“Daughter miya haɗaki da ɗan ƙanin nakine?”.
Zuciyar Aymah ta gado a ƙirji take. Dan haka tama manta da matsayin wani papa. Cikin ɗacin rai da rufewar idanu tace, “Papa har wannan ɗan mitsitsin yaron yakai girman da zai dinga kawomin raini a gidan nan? Tunda nake bai taɓa gaidani ba. Hakan yasa sam bana shiga sabgarsa. Shine tsabar rainin wayo yanzu yaje yana min magana a tsaitsaye kamar wata sa'arsa, shiyyasa naga ya dace na fara koya masa tarbiya idan wadda aka bashi bata ishesa ba, dan.........”
A wani irin harzuƙe Momy ta katseta. “Yaƙi ya gaishekin? Ke kina girmama nagaba dake ɗinne?”.
“Tabbas ina girmama nagaba dani Momy, sai dai fa inhar shi wannna na sama dani ɗin ya nunamin shekaruna da nasa babu banbanci to wlhy zan bi na taka shima na koyar dashi tarbiyyar daya rasa tun ƙuruciya. Kuma wlhy inhar Abraham baya gaisheni a gidannan, koya sake rainani saina sakasa a makarantar jiki magayi a gidanan a kuma gabanki”.
Ba Momy ba hatta papa lamarin Aymah tsoro ya ƙara bashi. Sai faman jinjina kai yake yana magana da zuciyarsa. ‘Like Father like daughter. Lallai John ya ɗakko mana shugabar ƴan boko haram a gidan. dan kuwa tabbas jinin Sooraj dama bazai kasance na banza ba’. A fili ko sai yaya saurin dakatar da Momy da taso yin magana. “Ya isa Darling. Bakiga yarinya bace ita. bai kamata ki biyetaba. Kuma tama fimu gaskiya. shi Abraham ɗin miyasa baya gaisheta?”.
Nanfa ya shiga yima Abraham faɗa sosai, ya kuma sakashi bama Aymah haƙuri dole. Itama Momy akan abinda ya faru jiya yay mata sulhu da Nu'aymah. Yasa Aymah bata haƙuri, ya kuma jama Momy gargaɗi akan shiga sabgar Nu'aymah inhar ba wadda ta kasance ƙyaƙyƙyawa ba.
Hakan ya sake cima Momy rai akan yarinyar. Amma sai tayi shiru saboda maganar da suka tattauna da papan a daren jiya gameda shirinsu akan mahaifin Aymah dama ita kanta da zasu raba da ɗansu nanda lokaci ƙanƙani.
Daga haka ya sallameta ta tafi. A wannan yinin kaf Nu'aymah tayisa cikin ƙunci ne a gidan. Tare da ɗaukar alwashi kala-kala ga duk jama'ar gidan. Dan ta rantse da gemun baba malam duk sai ta gasa musu aya a hannu. Papa ne kawai zai tsira a cikinsu shima idan yaso.
Dalilin wannan rikici Nu'aymah ta sake tsumewa kowa a gidan. Bata da abokin hira sai Uwaliya sai ko Blessing dasu Destiny dake fakar ido idan su mama debora basa falo su shigo mata. Ko kuma idan ta fita harabar gidan shan iska. Dan yanzu da gadara ma take fitowa har falon ƙasan ko harabar gidan ko garden ta zauna tana latse-latse a wayar da babu sim card a ciki koda kuwa suna zaune a wajen. Kota duba buks ɗinta na boko kona islamiyya. Kosu zauna da Uwaliya suyi hira idan sun gama aiki tunda yazam aikin nasu bawani mai wahalarwa bane ba. Komai tare sukeyi da Uwaliya, ɗakin Yoohan ne dai bata taɓa bama Uwaliya damar ko taɓa murfinba. ɗakinta ma itace ke gyara abinta, sai dai wani dalili yakai Uwaliya ciki amma badan aiki ba. Abinci ma kusan Aymah keyin abinta, sai dai Uwaliyan na tayata.
Kullum sai tayi waya da Umm da Baba malam da Hajjo a wayar Uwaliya. Yoohan kam basu taɓa waya ba tunda ya tafi, ita harma mantawa take da lamarinsa. sai dai duk sanda zata sha chocolate sai abinda ya faru tsakaninsu akanta ya faɗo mata a rai. Haka kawai abin kan sakata murmushi, kokuma taita ƙunƙuni tana kiransa ƙazami mayen baki.
Bata taɓama kowa zancen hoton data ɗakko a ɗakin papa ba, tundama ta ɓoyesa bata sake waiwayarsa ba. duk da kuwa batunsa na nan damar cikin zuciyarta. A dalilin hakannema ya sata mugun sakama duk wani motsi na madam Chioma da papa a gidan idanu. Tanason ta gano ainahin gaskiyar abinda ranta ke raya mata game da madam Chioma ba itace mahaifiyarsa ba. Abinda Aymah ta fara fahimta shine akwai wani haramtaccen business da papa keyi a ɓoye da Yoohan baisan da shiba. Dan inhar Yoohan yana a gari komansa yakan zama taka tsan-tsan. Amma yanzu da baya nan sai take ganin wasu baƙin halaye muraran ga papan duk da bawai yana fitowa fili yanayi bane, sai idan ka kasance mai lura sosai kamar ita data saka masa idon mikiya ne zaka fahimta.
Wannan ne ya saka ƙaramin tunaninta sake faɗaɗa, harta kasa haƙuri suna waya da baba malam take faɗa masa ita lamarin papan Yoohan na bata tsoro. Da yake dama baba malam ɗinne yay mata tambayar akan papan cikin hikima. Koda ta faɗi hakan dariya kawai yayi, bai tambayeta mita gani ba ko dalilinta nacewar hakan sukai sallama.
Daga ranar kuma baba malam bai sake takalar Aymah da zancen papa ba. Itama kuma bata sake masa ba ta cigaba da hidimarta.
__________★
Yau ta kasance asabar. Kusan ƙarfe sha biyu sai ga su Amal Yah Omar ya kawo mata su. Wayyo zokaga murna kamar zata tashi sama danjin daɗi. Hatta Adawiya da Abbah ya tilastama biyosu dan dole Aymah sai da ta rungumeta. Ranar dai ƴan gidan sunsha kallo dan duk suna gida. Gebrail le kawai yanacan gantalinsa da abokai tunda babu makaranta.
Jama'ar gidan sun sake yarda Nu'aymah bata fito a ƙaramin gida ba, dan motar da Omar ya kawo su Yusrah a ciki kawai ta isa shaida. Ga uban tsaraba da suka shigo dashi kamar sunzo daga wani garine. Nasu daban na Aymah daban kuma.
Adawiya dai nata kallon makeken gidan da aka kawo Aymah a ciki, musamman sashen Aymah daya tsaru da irin burinta da buƙatarta. Tasan iyayensu nada kuɗi sosai, dukda ta taɓa jin ƙishin-ƙishin a gidansu akan kaso biyu na dukiyar gidansu mallakin baba malam ce. Amma sai taji kamar Aymah ta sake samun matsayine sama dana gidansu duk da tana a tsakkiyar waɗan nan mutanen da babu ALLAH a ransu.
Kayan ƙwalam da maƙulashe ta ɗebo musu sukaci iya cinsu suna kwasar hira cike da farin ciki. Adawiya ce dai data saka kanta a uku bata cewa komai. Suko sun watsar da ita sunata sabgoginsu.
Bayan sallar la'asar Aymah tace su shirya su rakata mtn office tayo register layinta ta ɗora a wayarta da suketa faman santi saboda haɗuwarta. Dan ganin wayarnan sai da ya saka idanun Adawiya cika da ƙwallar baƙin ciki. Duk abinda taima kanta buri da fata sai taga Aymah ta fara samunsa kafin ita. Yah Ab ne kawai tayi nasar ƙwace mata. Shima gashi ya suɓuce mata a daidai lokacin da Nu'aymahr ta samu wanda ya fisa komai. Dan ƙyaƙyƙyawar nasaba ce kawai Abdallah zai bugi ƙirji yace yafi Yoohan da ita.
Kan Nu'aymah tsaye taje ta sanarma drivern gidan zai kaisu anguwa. Duk da tsoron madam Chioma dake a ransa haka ya amsa mata saboda uban kwarjinin datai masa a idanu. Itako bama ta damu da halin da yake a cikiba. Ta miƙa masa ɗaya daga cikin keys ɗin motar Yoohan data ɗakko a ɗakinsa. Idanu ya zaro sosai cikin rawar jiki yake, “Madam ai ko oga sau biyu kawai ya taɓa shiga motarnan, kuma da kansa yay driving, duk guri kuma na musamman yaje a ciki”.
Wani shegen harara ta zuba masa tana kallonsa a iskance. “Kai dokar ogan ta dama. Dalla amshi key muje banason ƙananun magana. Motar wofi makamin mutuwa da har za'a wani zauna yin tsarin shigarta. Koshi ogan naka ya zama mota hawa zanyi na zaga duniya nai kallo mtsoww!”.
Amsa yayi dole dan yasan jarabar Aymah tafi gaban naƙi. Masu gidanma ba raga musu takeba balle shi da yake cin arziƙi. Sai dai kuma abinda Nu'aymah bata saniba shine suna fita guards ɗin Yoohan suma suka bisu a baya. Dan dokar Yoohan ɗince haka a garesu. Bata farga da su ba sai da sukaje har sukayo register ɗin suka fito. Aymah tasa aka kaisu wani wajen shan ice-creem dasu shawarma. Sai gab da magriba suka taso zasu tafi idonta ya sauka akan guards ɗin Yoohan ɗin. Wannan abu ya baƙanta mata rai. Amma sai bata tanka ba. A cewarta da ubangidan nasu zatayi shine dai-dai da ita. Sukam basu kai martabar ji daga gareta ba.
“Daughter miya haɗaki da ɗan ƙanin nakine?”.
Zuciyar Aymah ta gado a ƙirji take. Dan haka tama manta da matsayin wani papa. Cikin ɗacin rai da rufewar idanu tace, “Papa har wannan ɗan mitsitsin yaron yakai girman da zai dinga kawomin raini a gidan nan? Tunda nake bai taɓa gaidani ba. Hakan yasa sam bana shiga sabgarsa. Shine tsabar rainin wayo yanzu yaje yana min magana a tsaitsaye kamar wata sa'arsa, shiyyasa naga ya dace na fara koya masa tarbiya idan wadda aka bashi bata ishesa ba, dan.........”
A wani irin harzuƙe Momy ta katseta. “Yaƙi ya gaishekin? Ke kina girmama nagaba dake ɗinne?”.
“Tabbas ina girmama nagaba dani Momy, sai dai fa inhar shi wannna na sama dani ɗin ya nunamin shekaruna da nasa babu banbanci to wlhy zan bi na taka shima na koyar dashi tarbiyyar daya rasa tun ƙuruciya. Kuma wlhy inhar Abraham baya gaisheni a gidannan, koya sake rainani saina sakasa a makarantar jiki magayi a gidanan a kuma gabanki”.
Ba Momy ba hatta papa lamarin Aymah tsoro ya ƙara bashi. Sai faman jinjina kai yake yana magana da zuciyarsa. ‘Like Father like daughter. Lallai John ya ɗakko mana shugabar ƴan boko haram a gidan. dan kuwa tabbas jinin Sooraj dama bazai kasance na banza ba’. A fili ko sai yaya saurin dakatar da Momy da taso yin magana. “Ya isa Darling. Bakiga yarinya bace ita. bai kamata ki biyetaba. Kuma tama fimu gaskiya. shi Abraham ɗin miyasa baya gaisheta?”.
Nanfa ya shiga yima Abraham faɗa sosai, ya kuma sakashi bama Aymah haƙuri dole. Itama Momy akan abinda ya faru jiya yay mata sulhu da Nu'aymah. Yasa Aymah bata haƙuri, ya kuma jama Momy gargaɗi akan shiga sabgar Nu'aymah inhar ba wadda ta kasance ƙyaƙyƙyawa ba.
Hakan ya sake cima Momy rai akan yarinyar. Amma sai tayi shiru saboda maganar da suka tattauna da papan a daren jiya gameda shirinsu akan mahaifin Aymah dama ita kanta da zasu raba da ɗansu nanda lokaci ƙanƙani.
Daga haka ya sallameta ta tafi. A wannan yinin kaf Nu'aymah tayisa cikin ƙunci ne a gidan. Tare da ɗaukar alwashi kala-kala ga duk jama'ar gidan. Dan ta rantse da gemun baba malam duk sai ta gasa musu aya a hannu. Papa ne kawai zai tsira a cikinsu shima idan yaso.
Dalilin wannan rikici Nu'aymah ta sake tsumewa kowa a gidan. Bata da abokin hira sai Uwaliya sai ko Blessing dasu Destiny dake fakar ido idan su mama debora basa falo su shigo mata. Ko kuma idan ta fita harabar gidan shan iska. Dan yanzu da gadara ma take fitowa har falon ƙasan ko harabar gidan ko garden ta zauna tana latse-latse a wayar da babu sim card a ciki koda kuwa suna zaune a wajen. Kota duba buks ɗinta na boko kona islamiyya. Kosu zauna da Uwaliya suyi hira idan sun gama aiki tunda yazam aikin nasu bawani mai wahalarwa bane ba. Komai tare sukeyi da Uwaliya, ɗakin Yoohan ne dai bata taɓa bama Uwaliya damar ko taɓa murfinba. ɗakinta ma itace ke gyara abinta, sai dai wani dalili yakai Uwaliya ciki amma badan aiki ba. Abinci ma kusan Aymah keyin abinta, sai dai Uwaliyan na tayata.
Kullum sai tayi waya da Umm da Baba malam da Hajjo a wayar Uwaliya. Yoohan kam basu taɓa waya ba tunda ya tafi, ita harma mantawa take da lamarinsa. sai dai duk sanda zata sha chocolate sai abinda ya faru tsakaninsu akanta ya faɗo mata a rai. Haka kawai abin kan sakata murmushi, kokuma taita ƙunƙuni tana kiransa ƙazami mayen baki.
Bata taɓama kowa zancen hoton data ɗakko a ɗakin papa ba, tundama ta ɓoyesa bata sake waiwayarsa ba. duk da kuwa batunsa na nan damar cikin zuciyarta. A dalilin hakannema ya sata mugun sakama duk wani motsi na madam Chioma da papa a gidan idanu. Tanason ta gano ainahin gaskiyar abinda ranta ke raya mata game da madam Chioma ba itace mahaifiyarsa ba. Abinda Aymah ta fara fahimta shine akwai wani haramtaccen business da papa keyi a ɓoye da Yoohan baisan da shiba. Dan inhar Yoohan yana a gari komansa yakan zama taka tsan-tsan. Amma yanzu da baya nan sai take ganin wasu baƙin halaye muraran ga papan duk da bawai yana fitowa fili yanayi bane, sai idan ka kasance mai lura sosai kamar ita data saka masa idon mikiya ne zaka fahimta.
Wannan ne ya saka ƙaramin tunaninta sake faɗaɗa, harta kasa haƙuri suna waya da baba malam take faɗa masa ita lamarin papan Yoohan na bata tsoro. Da yake dama baba malam ɗinne yay mata tambayar akan papan cikin hikima. Koda ta faɗi hakan dariya kawai yayi, bai tambayeta mita gani ba ko dalilinta nacewar hakan sukai sallama.
Daga ranar kuma baba malam bai sake takalar Aymah da zancen papa ba. Itama kuma bata sake masa ba ta cigaba da hidimarta.
__________★
Yau ta kasance asabar. Kusan ƙarfe sha biyu sai ga su Amal Yah Omar ya kawo mata su. Wayyo zokaga murna kamar zata tashi sama danjin daɗi. Hatta Adawiya da Abbah ya tilastama biyosu dan dole Aymah sai da ta rungumeta. Ranar dai ƴan gidan sunsha kallo dan duk suna gida. Gebrail le kawai yanacan gantalinsa da abokai tunda babu makaranta.
Jama'ar gidan sun sake yarda Nu'aymah bata fito a ƙaramin gida ba, dan motar da Omar ya kawo su Yusrah a ciki kawai ta isa shaida. Ga uban tsaraba da suka shigo dashi kamar sunzo daga wani garine. Nasu daban na Aymah daban kuma.
Adawiya dai nata kallon makeken gidan da aka kawo Aymah a ciki, musamman sashen Aymah daya tsaru da irin burinta da buƙatarta. Tasan iyayensu nada kuɗi sosai, dukda ta taɓa jin ƙishin-ƙishin a gidansu akan kaso biyu na dukiyar gidansu mallakin baba malam ce. Amma sai taji kamar Aymah ta sake samun matsayine sama dana gidansu duk da tana a tsakkiyar waɗan nan mutanen da babu ALLAH a ransu.
Kayan ƙwalam da maƙulashe ta ɗebo musu sukaci iya cinsu suna kwasar hira cike da farin ciki. Adawiya ce dai data saka kanta a uku bata cewa komai. Suko sun watsar da ita sunata sabgoginsu.
Bayan sallar la'asar Aymah tace su shirya su rakata mtn office tayo register layinta ta ɗora a wayarta da suketa faman santi saboda haɗuwarta. Dan ganin wayarnan sai da ya saka idanun Adawiya cika da ƙwallar baƙin ciki. Duk abinda taima kanta buri da fata sai taga Aymah ta fara samunsa kafin ita. Yah Ab ne kawai tayi nasar ƙwace mata. Shima gashi ya suɓuce mata a daidai lokacin da Nu'aymahr ta samu wanda ya fisa komai. Dan ƙyaƙyƙyawar nasaba ce kawai Abdallah zai bugi ƙirji yace yafi Yoohan da ita.
Kan Nu'aymah tsaye taje ta sanarma drivern gidan zai kaisu anguwa. Duk da tsoron madam Chioma dake a ransa haka ya amsa mata saboda uban kwarjinin datai masa a idanu. Itako bama ta damu da halin da yake a cikiba. Ta miƙa masa ɗaya daga cikin keys ɗin motar Yoohan data ɗakko a ɗakinsa. Idanu ya zaro sosai cikin rawar jiki yake, “Madam ai ko oga sau biyu kawai ya taɓa shiga motarnan, kuma da kansa yay driving, duk guri kuma na musamman yaje a ciki”.
Wani shegen harara ta zuba masa tana kallonsa a iskance. “Kai dokar ogan ta dama. Dalla amshi key muje banason ƙananun magana. Motar wofi makamin mutuwa da har za'a wani zauna yin tsarin shigarta. Koshi ogan naka ya zama mota hawa zanyi na zaga duniya nai kallo mtsoww!”.
Amsa yayi dole dan yasan jarabar Aymah tafi gaban naƙi. Masu gidanma ba raga musu takeba balle shi da yake cin arziƙi. Sai dai kuma abinda Nu'aymah bata saniba shine suna fita guards ɗin Yoohan suma suka bisu a baya. Dan dokar Yoohan ɗince haka a garesu. Bata farga da su ba sai da sukaje har sukayo register ɗin suka fito. Aymah tasa aka kaisu wani wajen shan ice-creem dasu shawarma. Sai gab da magriba suka taso zasu tafi idonta ya sauka akan guards ɗin Yoohan ɗin. Wannan abu ya baƙanta mata rai. Amma sai bata tanka ba. A cewarta da ubangidan nasu zatayi shine dai-dai da ita. Sukam basu kai martabar ji daga gareta ba.