← Book details Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 151 OF 211

Sashe 151

Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

ZAFAFA BIYAR 2021

Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

          Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗

        Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗

        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗

         Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋

    Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.*_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.

No. 61

...........Da Solomon sukaci karo a jikin wata dalleliyar mota tsaye. sai baturen dake cikin Uniform ɗin hotel ɗin. Da girmamawa Solo yake gaisheta da sake tambayarta ƙarfin jiki. Cike da takaicin zamantowarsa tamkar jelar Yoohan ɗin ya sakata amsawa a taƙaice. Yoohan ya buɗe mata da kansa ya taimaka mata ta shiga. rufewa yay, ya zagaya inda baturen ya buɗe masa shi kuma ya shiga. Baturen ne ya shiga a matsayin driver, Solomon kuwa gefensa. wannan abu ya zafi Nu'aymah a rai. Kenan duk inda mijin nata yake dole wannan basamuden sai ya kasance da shi?. Dolene tasan matsayin wannan bibbinin kuwa. Galla masa harara tayi lokacin da drivern ke harba motar a titi suka fice daga harabar hotel ɗin.
        Idanu Yoohan ya lumshe da jingina kansa da kujera. Ya saki ajiyar zuciya, a ransa yana ayyana ‘hakan shine kawai mafita a gareni. idan ba ɗan fitar mukaiba bazan iya barin yarinyar nan ba. komai zan iya aikatawa kamar yanda zuciyarsa ke bani ƙwarin gwiwar game da ita’.
          Nu'aymah dai ta fahimci motar hotel ɗince ya ara. Sai dai batasan ina suka nufaba. Dan haka ta ware idanu da ƙyau tana sake kallon tsarin garin na Vienna da ya gama haɗuwa da ababen more rayuwa kala-kala. Duk da ranta cike yake da taikaicin tafiya tare da Solomon, kai harshi kansa Yoohan ɗin haushinsa takeji akan Solo.
         Sun fara zuwa wani haɗaɗɗen wajen Saloon, bata fahemci hakanba kuwa sai da suka shiga ciki. Ta kallesa tana yamutse fuska, “Mi zamuyi anan?”. Kallonta kawai yake shidai fuska a tsuke shima. Dan shi kaɗai yasan a halin da yake ciki. Sai dai yana mamakin miya ɓata mata rai haka? Ya fahimci tun fitowarsu cikin hotel ɗin wajensu Solo ta ciskule fuska, saɓanin farko da kunyarsace kawai tattare da ita.
      Bai bata amsaba, sai ma ma'aikatan wajen da sukazo musu tarba ta mutuntawa. Da Garman language yay musu bayanin abinda suke buƙata. Hakan yasa Aymah bataji komaiba. Saima mamakin dama yanajin yaren data fahimci mafi yawan ƴan garin sunfiyi kenan?. Bata da mai bata amsa, sai jan hannunta da ma'aikaciyar tayi zuwa sashen mata. Binsu yay har ciki, shine ya zaɓa duk abinda za'ai mata. Nu'aymah dai ta zubama sarautar ALLAH ido tana kallonsu. Shiko yaƙi yarda su haɗa idon. Yana gama zaɓa ya biyasu kuɗinsu. Sai shi kuma ya nufi na maza dan yana buƙatar gyaran fuska da yankan farce.
         Haushi ya hana Aymah yin magana har aka fara wanke mata kanta. Ganin babu kitso dai yasa bata damuba. An mata wankin ƙafa da gyaran farce, sannan aka kaita wani ɗaki wai na gyaran jiki ne. Nu'aymah dai taga abinda ya girmeta, har tsoron shiga waɗan nan injina ta ringayi, a ganinta idan aka ɗauke wuta mutum na ciki kuma ai shikenan labarinsa ya ƙare. ‘Kai wannan mutumin ba kawoni yay kuwa a markaɗeniba ma?’ ta aiyana a ranta tana ƙunƙuni da hausa. Su dai ma'aikatan ba jinta sukeba. Hakan yasa suketa aikinsu kawai. Anyi mata gyaran jiki na musamman da ita kanta tasan eh ta gyaru ƙwarai da gaske. Aka kuma kaita wani waje wai tausa nankuma za'ai mata. ‘Babbar bala'i’ ta faɗa a fili cikin suɓutar baki. ‘Amma wannan mai jajayen kunnen ya gama sakamin rayuwa a gaba. Yoni nace masa ina buƙatar duk wannan ne ko mi?’. Haka taita zuba mita ana mata tausa. gashi kuma sai faman lumtse idanu takeyi alamar tanajin daɗin jikinta. Bayan kammala tausan an maidata wajen gyaran jiki, daga haka aka ƙarasa gyara mata kanta. Haɗaɗɗun wando da riga aka kawo mata ta saka ƙyautar da shagon ke badawa kenan idan suka maka aiki mai tsada irin haka. Badan taso ba ta amsa ta saka. Ta yana gyalen jallabiyar ta akai suka fito inda Yoohan ke zaune yana jiransu. Dan shi tuni an kammala masa.
         A tare suka zubama juna ido. Kowanne yana zancen ƙyawun da ɗan uwansa yay masa a zuciya. Sake tashi hankalin Yoohan yayi matuƙa, wata sabuwar buƙata da tafi ta farko sai ƙara bijiro masa takeyi. Nannauyan numfashi ya furzar da yin luuu da idanunsa da launinsu na fari ya sirka zuwa ja. Sai da ya lumshesu sannan ya sake buɗewa akanta. Da ƙyar ya iya miƙewa tsaye zuwa gareta. Ita dai kanta a ƙasa tun kallon datai masa na farko da yaba ƙyawun da gyaran fuskar da yay yayi masa, dan an canja masa style ɗin sajensa. bata ƙara yarda ta dubesaba saboda kallon ƙurullar data ga shima yana mata. Hannu yasa a hankali ya zame gyalen daga bisa kanta yana kallon gyaran gashin nata. Ya kama jelar gashin dake ɗaure a tsakkiya ya murza cikin hannunsa tare da shaƙar ƙamshin da gashin keyi. Duk yanda yaso furta wani abu a harshensa ya kasa hakan....
        Maganar ma'aikaciyar wajen ce ta katsesa daga ƙoƙarin kamo fuskar Aymah da yayi niyyar yi. Ya juyo yana kallonta. Bag ɗin hannunta mai tambarin wajen nasu ta miƙama Nu'aymah fuskarta da murmushi tai musu godiya na zuwa masana'antarsu. Guntun murmushi Aymah tayi mata kawai ta amsa. Kallon jikkar yayi ya maida dubansa ga matashiyar matar. Yay mata tambayar da Aymah batasan ta minene ba, kai kawai ya gyaɗa mata da kama hannun Nu'aymah suka fito Reception, wata hanya sukabi bayan taga ya karanta rubutun wajen da ita dai ba ganewa takeba tunda ba turanci baneba. A shagon kaya ta gansu, yanda baiyi maganaba itama batayiba. Sai hannunta daya riƙe yanabin kayan da kallo. Yayinda ma'aikatan wajen ke musu barka da zuwa.
         Kujera aka bata ta zauna shi kuma yana duba abinda yazo nema. Kallon shagon ya ɗaule mata hankali har batasan dami-dami ya ɗaukaba. Sai da yazo gabanta da riga a hannu ne ta kallesa. ya kamota ya miƙar tsaye yana magana a hankali. “A ƙasar mutane ma sai kin nuna ke bakanuwa ce?”..  
       Harararsa tayi dai-dai yana kamo hannunta ya zura mata hannun rigar coat ɗin ta mata data gama haɗuwa sai wani irin shegen ƙamshi takeyi. Bakinsa ya taɓe ya kamo ɗayan ma ya zura mata ya gyara mata rigar da ƙyau. Takai mata har gwiwa kuwa, hakan yasa ta rufe mata jikin yanda yafi buƙata, dan yaji a ransa bazai iya barinta yawo da kayan da wajen saloon ɗin suka bata ba.
      Ta ƙara ƙyau kuwa sosai masha ALLAH, shi kansa ya kasa ɗauke ido a kanta. Kuɗin abinda ya ɗauka ya biya suka fito a wajen. Inda suka bar su Solomon zaune a harabar wajen nan suka iskesu suna shan coffee. Solomon dake satar kallonsu ta gefen idi yace, ‘Yarinya sai shege ƙyau kamar aljana. Shiyyasa gaba ɗaya oga ya susuce a kanta’.
     Oho Aymah batasan yanayiba. Dan tuni ma ta buɗe mota ta shige ko jiran Yoohan ɗin ya buɗe mata yayi batai ba. Da kallo shima ya bita dan ya fara fahimtar kamar haushin Solomon takeji. Bai dai tabbatar ba, dan haka shima ya shiga motar. Su Solo ma duk shiga sukai suka bar wajen.
         A yanzunma da suka tafi kanta ta juyar tana kallon garin. Shi dai Yoohan nata kallonta ta ƙasan ido da nazarinta har suka ƙarasa wani garden ɗin hutawa. Wajene da masoya kawai ke kai kawo abin zaƙƙyau da burgewa. Sun bar su Solomon acan wajene, shi da ita kawai suka shiga ciki. Inda ya zazzagaya da ita wajejen abubuwan tarihi, sukai hotuna ta sha kallo kuma. Yoohan bai da kuzari gaba ɗaya. Yanata dauriyane kawai, dan a rayuwarsa bai taɓa jin matsananciyar sha'awa irin ta yau ba. Ji yake kamar idan bai akasance da mace ba zai rasa ransa. Itako Aymah gani take shegen miskilancinsa ne ya motsa kawai. Shiyyasa ta tattarasa ta watsar gefe. Ko abu ya faru sai dai taita ƙunƙuni a ranta da gulmarsa a zuciya. A waje sukai sallar la'asar, magriba da isha'i. Sun ɗanyi ciye-ciyensu da Aymah ke ganin wasu ƙazanta. Duk dan lokaci yaɗan ƙara ja sai da Yoohan ya bari tara na agogon ƙasar yayi sannan suka dawo hotel ɗin su.
        Masifaffen ciwon cikin daya taso masane ya sakashi cemata taje ciki yana zuwa zaije asibiti duba wani maralafiya. Bata damuba. Ta kwashi kayan da suka sayo tai ciki. Can ya samu ƙasan wani rumfar ya zauna dan dama babu asibitin da zaije. So yake taɗanyi nesa da shi ko zaiji sassaucin abinda ya keji game da ita. Sai dai kuma ina, rikicewa ma al'amarin ya sake neman yimasa saboda kaiwa da kawowa da matan turawan keyi ta wajen tamkar tsirara. Bai rufa mintuna ashirinba dole ya tashi a wajen ya nufi cikin ɗakin jikinsa na rawa. 
Chapter 151 · 0% Book details