← Book details Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 153 OF 211

Sashe 153

Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

     A firgice ta farka da ga razanannen mafarkin daya risketa cikin barcin daya ɗauketa bayan dawowarsu wani taron karammawa da akaima papa, kasancewar sa dattijon da akeji da shi a yankinsu. Sannan gashi babban Pastor da ba Nigeria kawaiba har wasu ƙasashen ƙetare yana baza komarsa. Wannan taron karammawa ya gudana ne a Abuja bisa jagorancin ƙungiyar Christians reshen catholic. An karamasu su bakwai. sai dai papa shine yafi kowa ɗaukar wannan jinjinar girmamawa.
       Ɗunbin gajiyar data samo acan ne ya saka suna shigowa gidan kaya kawai ta cire ta kwanta ko wanka bata iya samu tayi ba. A cikin wannan barcine tai gamo da mummunan mafarkin da ko'a labari bata fatan tabbatuwarsa. A zabure ta miƙe zuwa inda ajiyayyen asirinta yake na tsahon shekaru kusan goma sha uku. Rawa jikinta ya kamayi kamar mazari ganin ƙullin da akaima igiyar cikin tukunyar ya warware. Da sauri ta ajiye tukunyar a ƙasa saboda karkarwar da hannunta keyi gudun karta yaddata. Waya ta jawo a ruɗe tai kiran ƙawarta. Bugu biyu Madam Rebecca dake holewarta da wani yaro a gidanta dan mijinta baya ƙasar yana can harkar kasuwancinsa ta ɗaga tana riƙe hannun matashin yaron ɗan shekaru ashirin da uku daga sheɗancin da yakeyi a jikinta.
     “Sorry Baby. just 5minutes”. Ta faɗa tana masa kiss da kai wayar kunnenta. Duk Madam Chioma tana jiyosu, ta riga tasan ƙawar tata kullum bata rabo da yara ƙanana tare da ita. Sai dai bama wannan bane damuwarta a yanzun. Damuwarta abinda taci karo da shi. Muryarta na rawa tace, “Rebecca! Tawa ta ƙare”.
       Cike da tsoron jin yanayinta da furicinta Madam Rebecca ta tashi zaune tana tambayarta miya faru?. Cikin kuka rurus Madam Chioma ta zayyane mata komai game da mafarkinta da kuma abinda ta gani a tukunyar tsafinta. Wani shegen murmushin mugunta Madam Rebecca tayi. A fili kuwa sai tace, “Kinga kwantar da hankalinki, bara na gama da babyn nan na gabana zanzo gidan”.
     Da matuƙar tashin hankali madam Chioma tace, “Haba Rebecca. ina miki maganar matsalata kina magana irin haka? ki tausaya min mana. Banason na rasa Yoohan a rayuwata ko cika burina ban samu nayiba”.
      “Hah!! Kinada matsala Chioma. Kema kinsan inaa wannan yanayin babu abinda zan iya miki koda nazo. Garama kiyu hakuri ki bani 1hour kawai”. Cike da matsanancin takaici Madam Chioma ta yanke wayar. Maida akalar kiranta tayi ga Number Yoohan. Sai dai harta yanke ba'a ɗagaba. Dan a lokacin bama wayaba har ita kanta dake matsayin uwarsa ya manta da ita a duniya. Nu'aymah kawai ya sani a yanzu, ita kaɗai kuma yake gani.
      Ta jera masa kira kusan biyar babu amsa. Hakanne ya ƙara rikitata ta koma kiran Solomon. shima dai akai sa'a bai ɗagaba. Dan a lokacin yayi barci saboda gajiyar yawon da sukasha, yana dawowa kuma ya samu wata ƴar baby suka shige da ga ciki. Ai saita sake haukacewa. A ruɗe ta fara haɗa kayan tafiya ƙauyensu Madam Rebecca, dama daga can aka yo mata aikin. Dan bazata iya kwana garin Abuja ba batare data san makomar abinda ta ganiba. Bayi ta shiga ta facaccala wanka ta fito. Yanda take komai a birkice sai ka ɗauka tama zare ne. Sai da ta kimtsa tsaf ta fito jaye da ƙaramin trolly da handbag. Sashen Papa ta nufa, kamar yanda tayi hasashe kuwa ta samesa a falonsa zaune shi da Uncle Godwin suna tattauna mai fishshesu. Da ƙyar ta iya ƙoƙarin control ɗin ruɗaninta suka gaisa da Godwin ɗin. Papa dake binta da kallo ya miƙo mata hannu alamar tazo garesa. Zuwa tayi ta zauna a jikinsa cike da dauriya, ta ɗora kanta a kafaɗarsa. Kiss ya bata a goshi da bakinta yana faɗin, “Are you Ok?”. Kanta ta daga masa. Murya a sanyaye tace, “Yes. I'm. Kirane ya sameni na gaggawa daga office ɗinmu, akwai wani taro wai da zamuyi a Lagos dama tun kusan sati biyu, anata ɗagawa kuma sai yau ne wai sukace gobe za'ayi, gashi yanzun an turomin saƙo ni akeson na halarci wajen wai kuma”.
       Tuni fara'ar papa ta ɓace a fuskarsa. Dan yana tsananin sonta, koda wasa bayason tanayin nesa da shi. Amma kuma bayason ɓacin ranta. Zai yi magana tai saurin ɗora yatsanta akan bakinsa tana faɗin,
    “Please baby”.
Ajiyar zuciya ya sauke a hankali. Badan ransa nasoba yace, “Okay. Yanzu kina buƙatar wani abu ne?”.
       “No thanks you dear. Basai na ɗaura maka wata wahalaba ma”.
       “Bakinta ya sake sumbata, da murmushinsa na yake yace, “Babu damuwa zan miki transfer ɗin kuɗin shan ice-creem ”.
       “Thanks you baby”. Ta faɗa tana sumbatar laɓɓansa da mikewa tsaye. Ta sake cewa “Bey”.
    Kusan a tare shi da Uncle Godwin sukace mata “Safe journey”. Daga haka ta fice tabar papa da jimami. Duk da shima hakan wata damace a garesa da zai shanama tashi rayuwar.
     Ko sallama batai da su mama debora ba ta fice abinta. Yaran kuwa suna can garden dama. Tana fitowa harabar gidan motar madam Rebecca na shigowa. Tsaki taja tare da nufar motar. Batare data yi magana ba ta buɗe gefen driver ta zauna. Reverse kawai Madam Rebecca tayi suka fice da ga gidan.
      Sai da suka hau titi suka fara magana. Madam Chioma ta dage akan a yau zata wuce dan bazata iya kwana cikin abuja ba. Lallaɓata Madam Rebecca ta shiga yi akan ta bari su sami jirgin da zai kaisu jihar River state. Dan tafiyar mota ba abune mai sauƙi a garesu ba. Da farko sam madam Chioma taƙi saurarenta. Sai da tai da gaske da tuna mata ka'idojin bokan sannan ta dawo hayyacinta ta amince zata kwana a gidan Madam Rebecca ɗin. Can suka wuce. Sai dai a ranar sukai booking ɗin jirgi. Tare da kiran bokan shima sukai magana da shi ya basu damar zuwa a goben. Da ga haka suka cigaba da tattaunawa akan lamarin Yoohan da Nu'aymah, dama basusan sunayi ba, dan su suna can a sabuwar duniya😉😎.........✍

Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

          Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗

        Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗

        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗

         Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋

    Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍*_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.

No. 62
Chapter 153 · 0% Book details