Sashe 181
Saran Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washe gari safiyar juma'a jirgin su Nu'aymah ya sauka a ƙasar haihuwarsu batare da kowa yasan da zuwan nasuba. Sai da taimakon Yoohan ta sakko a jirgin saboda ƙafafunta da sukai mata tsami da kumburi. Sai faman taɓe fuska take kamar zatai kuka. Shi kam dai ga tausayinta ga dariya na cinsa a rai. a zuciya ya ayyana, ‘Abufa yazo ga ma'iya’.
Bayan shigarsu texi taji yace a kaisu hotel. Ai babu shiri ta kallesa, “Hotel kuma Yah Yoohan? Gidan papa ɗin fa?”.
Cikin jin zafin dake taso masa a rai ya girgiza mata kansa. “Zamuje, amma yanzu muje ki huta ko?”.
Hankalinta tashe akan tunawa da hoton nan da sauri tace, “A'a ni dai gaskiya inba gidan papa ba sai dai ka sani a motar kano na wuce. Yaya gamu da gidan iyaye mu kama raɓe-raɓen hotel kamar wasu marasa galihu. Kayi haƙuri gaskiya ni dai bazanje hotel ba”.
Duk yanda yaso lallashinta akan suje hotel ɗin dan shi bayason zuwa gidansu. Ko sha'awar kallon fuskar Momy bayayi sam. Amma Nu'aymah ta tubure duk da bawai dan tanason zama gidan bane itama. Tana son sujene saboda hoton nan. Gara suje tun a yau ta ɗauka kafin papa ya farga suna ƙasar tunda ya bada kwangilar kasheta. Daga lokacin da matsaloli suka fara kuma ai maganar hoto sai tasha ruwa.
Badan Yoohan yaso ba dole yasa mai taxi ɗaukar hanyar anguwarsu dan kuka Aymah ta sanya masa rirus babuko kunya. Sam baya buƙatar damuwarta a irin wannan lokacin. Dan yama fahimci jininta yayi sama saboda wannan tafiyar mai nisa da sukayo. Daga haka kuwa bai ƙara maganaba, sai dai ya sakata a jikinsa kawai yana shafa bayanta alamar lallashi. Saiko faman cijar lip ɗinsa na ƙasa yake da ƙoƙarin danne abinda ke taso masa a rai.
Har ciki mai taxi ɗin ya shiga dasu, koda maigadi ya leƙi yaga Yoohan sai ya koma da sauri ya buɗe gate ɗin ransa fal murnar ganinsu. Da taimakonsa Aymah ta fito yanzunma. yayinda gaba ɗaya Guards ɗin gidan suka rufu musu a ka suna kwasar gaisuwa bakin kowa a washe na murnar ganinsu. Zuciya kam fal gulma ganin Nu'aymah da ciki. Musamman ma Solomon daketa faman zare ido.
Solomon ɗinne ya amshi ƴan kayansu dake a trolly ɗaya sai lap-top bag ɗin Yoohan. handbag ɗin Aymah kuwa tana a hannun Yoohan ɗin ɗayan hannunsa kuma riƙe da nata.
Da Gebrail suka fara cin karo zaune a dining yana lunch ɗin daya makara baiyiba. Idonsa na sauka a kansu kuwa ya sarƙe da abinci har sai da Blessing ta fito daga kitchen a guje dan jin mahaukacin tarin da yakeyi. Ko kallon inda yake kuwa Yoohan da Aymah basuyiba.
Wani bala'in waro idanu Blessing tayi tare da daka tsalle gefe hannayenta duka a saman kai tace, “Heeyyy!!! Ahhhhhh!! Emiiii!!!”.
Dariya ta bama Aymah sosai. Hakan ya sakata darawar kuwa. Yoohan kuwa daya zaunar da ita a kujera ko kallon Blessing ɗin baiyiba. Sai durƙusawa yay a gabanta ya kama ƙafafunta ya zare takalman da take sanye da su masu taushi, amma saboda tsabar hawa da ƙafar tayi sun manne mata har sunyi mata sayi. Matsa mata ƙafar ya farayi a sannu-sannu ransa fal tausayinta duk da yasan bawai wata matsala bane. Yanayine kawai da wasu masu cikin kan shiga.
Ihun Blessing ne ya fito da Joy da Miracle daga ɗaki suma a guje. Sai ga Victoria dasu Favour da har yanzu su suna abuja basu koma ƙauye ba. Makaranta ma Yoohan yace zai duba musu anan, sai kuma aka samu akasi wancan matsalar ta faru Yoohan yabar ƙasar babu shiri.
Da gudun bala'i su Destiny sukayo kan Nu'aymah da itama take kallonsu fuskanta washe da dariyar Blessing data gama kwasa...
A wani zabure Yoohan ya miƙe yana dakatar dasu, amma ina sukam idonsu ya rufe yau saboda farin cikin ganin auntynsu da kullum suke nacin son dawowarta. Gata kuma da ciki zata haifa musu baby a gida.
Goshi kawai Yoohan ya dafe yana faɗin, “Oh GOD!”.
Itako Aymah da dama ba hankalinne ya gama isartaba oho. Tuni ta tarbi ƴan yaranta da suka nuna mata ƙauna zalla a gidan babu algus. Sai da Yoohan yaga lamarin nasu bana ƙare bane yasa hannu ya fara ɗagasu ɗai-ɗai daga kan Nu'aymahr.
Ihun su Destiny ne ya farkar da mama debora a barcin da takeyi. Ta fito jikinta na rawa dan ta ɗauka wani abunne ya faru da yaran. Kaɗan ya rage bata bangaje su Joy da Miracle tai suman gigitaba ta tarota. Kota kansu batabiba ta fara sauka a benen da gudu zane a hannu.
Wani bala'in waro ido tayi akan Nu'aymah tana faɗin, “Jesus John matarka ne da ciki? Cikin jikana ɗanka. Kaima zaka haifi yaronka John ?”. Sai kuma ta nufeta cike da Sassarfa. A take annurin fuskar Aymah ya ɓace ɓat, hakama Yoohan kallon kakar tasa yake yaga mizatayi. A mamakin kowa sai mama debora ta fashe da kuka tana rungume Nu'aymah. Sai kuma ta durƙusa ƙasa ta ɗaura hannunta akan cikin Aymah tana sambatun zance da yare wanda sam Aymah ba ji takeba. Sai dai yanda taga Yoohan ya langaɓe kai yana kallon kakar tasu fuskarsa da murmushi ya sata fahimtar ba mummunan abu mama debora ke faɗi akan gudan jinin nasu ba. Tabbas duk wanda ya kalli mama debora a wannan lokacin yasan farin cikine na gaske tattare da ita. Ba komai yay silarsaba kuma sai cikin jikin Nu'aymah ɗin. Dan kanta batasan yaya akai ƙaunar cikin ta saukar mata ba lokaci ɗaya tare da Nu'aymahn kanta. (Nace Ƙarfin addu'a ce mama debora).
Tana faman sharar ƙwalla ta kamo hannun Yoohan ta zaunar a kusa da Nu'aymah. Ta haɗa hannayensu cikin na juna sannan tai Kneeling a gabansu tare da rufe idanunta duka ta ɗaga hannaye sama ta fara raira waƙar addu'a da yare tana hawaye, ganin hakan yasa su Victoria ma durƙusawa tare da Blessing suka fara tayata suma duk idanu a rufe.
Cike da zaro idanu Nu'aymah ta kalli Yoohan kamar zatai kuka. Dariya taso kufce masa. Amma sai ya gimtse yay murmushi kawai. A cikin kunnenta yace, “Karki damu addu'ar kariya sukema baby dakema ALLAH ya saukeki lafiya cikin ƙoshin lafiya”.
Duk da tasan su ba musulmai bane ta ɗanji sanyi a ranta tunda ba wani tsafi baneba dai. sai kawai ta ɗora kanta a gefen hannunsa tana mai addu'a a ranta itama ALLAH yasa sunada rabon musulinci. Dan tabbas yau taji gaba ɗaya haushin mama debora da takeji ya kwaranye. Dama ance mai ɗa wawa.
Bayan sun gama addu'arsu sun zauna, mama debora nata wani ji da Nu'aymah. Ita dai abin har dariya yake bata. Hakam Yoohan dariya kakar tasa ke basa da gaske. Ta dungure masa kai tana faɗin, “Mara mutunci. kasan matarka nada ciki baka taɓa faɗama kowaba. Yarinyata watansa nawa?”. Ta maida maganar kan Nu'aymah bayan ta zubama Yoohan dake kumbura mata fuska saboda mangarar masa ƙeya da tayi harara.
Haka kawai sai Aymah taji nauyin faɗa. Sai Yoohan ɗinne ya bata amsa. Sai kawai ta tashi ta kama rawa tana waƙar yarensu irinta tsoffi.
A wannan yanayin papa da Madam Chioma da basa gidan suka shigo suka samesu. Gaban Nu'aymah yay mummunan faɗuwa. Da sauri ta shiga karanto addu'a a cikin ranta. Sannan ta yunƙura ta miƙe kamar yanda taga Yoohan ya miƙe fuskarsa a tsuke saboda ganin Momy.
Da wani irin kallo papa kebin Nu'aymah da cikinta. madam Chioma kam Yoohan take kallo kamar wata tsohuwar mayya. Dan sam hankalinta bai kai kan Aymah ba tukkunna.
Cike da farin ciki Mama debora ta nufi papa tana rera waƙarta da ke nuna tana a tsantsar farin ciki na haƙiƙa, hannunsa ta kamo ta nufi inda Nu'aymah take. Da sauri Madam Chioma takai dubanta inda mama debora ta nufa da Papa. Aiki idanunta sukai mata mummunan gani. Da tsanin gigita ta furta, “What??! Impossible!. Na rantse da ALLAH impossible!!!”.
A kusan tare kowa dake a falon ya kalleta, sai kawai ganinta sukai a ƙasa ta sulale sumammiya.
A guje su Destiny sukayi kanta da papa. Yoohan kam fuska ya kauda gefe cike da ƙunar zuciya. Nu'aymah da tasan ba sonta madam Chioma keyiba dama can sai bata ɗauki hakan komaiba face ƙiyayyar da take nuna mata dama can.
Mama debora kam wani irin taɓe baki tayi da faɗin, “Aiko Chioma zaki mutune a haifamin jikana duniya. Kujimin yarinya da baƙin halin baƙin ciki. Ke sanda kika haifi John nayi miki hassada ne? Bandama inada zuciya me ƙyau ai saina saka ayar tambaya a kanki dan Yoohana baya kama dake, nayi shirune kawai dan yana kama da yarona, amma kekam ai kamarma ba ɗanki ba. Sai shi yanzu zaki baƙin ciki matarsa zata haifa masa ɗa. Kema sai kinji abinda naji na rabani da ɗana da kikayi......”
A guje Blessing ta kawo ruwa aka yayyafama Madam Chioma. Tako fasa wata razananniyar ƙara da miƙewa zaune tana nuna Nu'aymah. “Wannan ba cikin yarona bane, kufitarmin da ashawo ɗinnan a gida, na rantse da ALLAH john wannan ba cikinka baneba. Dan hakan bazata taɓa kaswncewaba. Idan baku fitarmin da ita a gidaba zan kasheta. Ku kaita can ta nemo uban cikinta dan bana John bane. Darling narsantse damfararmu yarinyar nan zatayi cikin nan bana John bane. Sun tsafemin yaro sun rabani da shi. Yanzu zasu manna masa cikin kuma da ba nasab.......”
Yanda take surutan zaka ɗauka bata da hankalima sam. Yoohan da takaici ya kume yaja hannun Nu'aymah suka haye sama abinsu batare da yayi ko tariba. Mama debora ma wani dariya da ihu ta sanya tana tafa hannaye. “Chioma kishi da matar ɗanki yasa kin haukace gaskiya. Tunda ni kakar John na yarda cikinsa ne koke da goshpower kukaƙi yarda nasan kishi ne. Yanda nasha baƙin cikin rabani da ɗana da kikayi kema sai kinsha fiye da wannan baƙin cikin na rabuwa da John. Wuuuuuuu!!! She she Shem!!! Wuuuuuu!!!! Hhhhhhhh!!!! Anji kunya uwa mai kishi da matar yaronta!!!!”.
Bayan shigarsu texi taji yace a kaisu hotel. Ai babu shiri ta kallesa, “Hotel kuma Yah Yoohan? Gidan papa ɗin fa?”.
Cikin jin zafin dake taso masa a rai ya girgiza mata kansa. “Zamuje, amma yanzu muje ki huta ko?”.
Hankalinta tashe akan tunawa da hoton nan da sauri tace, “A'a ni dai gaskiya inba gidan papa ba sai dai ka sani a motar kano na wuce. Yaya gamu da gidan iyaye mu kama raɓe-raɓen hotel kamar wasu marasa galihu. Kayi haƙuri gaskiya ni dai bazanje hotel ba”.
Duk yanda yaso lallashinta akan suje hotel ɗin dan shi bayason zuwa gidansu. Ko sha'awar kallon fuskar Momy bayayi sam. Amma Nu'aymah ta tubure duk da bawai dan tanason zama gidan bane itama. Tana son sujene saboda hoton nan. Gara suje tun a yau ta ɗauka kafin papa ya farga suna ƙasar tunda ya bada kwangilar kasheta. Daga lokacin da matsaloli suka fara kuma ai maganar hoto sai tasha ruwa.
Badan Yoohan yaso ba dole yasa mai taxi ɗaukar hanyar anguwarsu dan kuka Aymah ta sanya masa rirus babuko kunya. Sam baya buƙatar damuwarta a irin wannan lokacin. Dan yama fahimci jininta yayi sama saboda wannan tafiyar mai nisa da sukayo. Daga haka kuwa bai ƙara maganaba, sai dai ya sakata a jikinsa kawai yana shafa bayanta alamar lallashi. Saiko faman cijar lip ɗinsa na ƙasa yake da ƙoƙarin danne abinda ke taso masa a rai.
Har ciki mai taxi ɗin ya shiga dasu, koda maigadi ya leƙi yaga Yoohan sai ya koma da sauri ya buɗe gate ɗin ransa fal murnar ganinsu. Da taimakonsa Aymah ta fito yanzunma. yayinda gaba ɗaya Guards ɗin gidan suka rufu musu a ka suna kwasar gaisuwa bakin kowa a washe na murnar ganinsu. Zuciya kam fal gulma ganin Nu'aymah da ciki. Musamman ma Solomon daketa faman zare ido.
Solomon ɗinne ya amshi ƴan kayansu dake a trolly ɗaya sai lap-top bag ɗin Yoohan. handbag ɗin Aymah kuwa tana a hannun Yoohan ɗin ɗayan hannunsa kuma riƙe da nata.
Da Gebrail suka fara cin karo zaune a dining yana lunch ɗin daya makara baiyiba. Idonsa na sauka a kansu kuwa ya sarƙe da abinci har sai da Blessing ta fito daga kitchen a guje dan jin mahaukacin tarin da yakeyi. Ko kallon inda yake kuwa Yoohan da Aymah basuyiba.
Wani bala'in waro idanu Blessing tayi tare da daka tsalle gefe hannayenta duka a saman kai tace, “Heeyyy!!! Ahhhhhh!! Emiiii!!!”.
Dariya ta bama Aymah sosai. Hakan ya sakata darawar kuwa. Yoohan kuwa daya zaunar da ita a kujera ko kallon Blessing ɗin baiyiba. Sai durƙusawa yay a gabanta ya kama ƙafafunta ya zare takalman da take sanye da su masu taushi, amma saboda tsabar hawa da ƙafar tayi sun manne mata har sunyi mata sayi. Matsa mata ƙafar ya farayi a sannu-sannu ransa fal tausayinta duk da yasan bawai wata matsala bane. Yanayine kawai da wasu masu cikin kan shiga.
Ihun Blessing ne ya fito da Joy da Miracle daga ɗaki suma a guje. Sai ga Victoria dasu Favour da har yanzu su suna abuja basu koma ƙauye ba. Makaranta ma Yoohan yace zai duba musu anan, sai kuma aka samu akasi wancan matsalar ta faru Yoohan yabar ƙasar babu shiri.
Da gudun bala'i su Destiny sukayo kan Nu'aymah da itama take kallonsu fuskanta washe da dariyar Blessing data gama kwasa...
A wani zabure Yoohan ya miƙe yana dakatar dasu, amma ina sukam idonsu ya rufe yau saboda farin cikin ganin auntynsu da kullum suke nacin son dawowarta. Gata kuma da ciki zata haifa musu baby a gida.
Goshi kawai Yoohan ya dafe yana faɗin, “Oh GOD!”.
Itako Aymah da dama ba hankalinne ya gama isartaba oho. Tuni ta tarbi ƴan yaranta da suka nuna mata ƙauna zalla a gidan babu algus. Sai da Yoohan yaga lamarin nasu bana ƙare bane yasa hannu ya fara ɗagasu ɗai-ɗai daga kan Nu'aymahr.
Ihun su Destiny ne ya farkar da mama debora a barcin da takeyi. Ta fito jikinta na rawa dan ta ɗauka wani abunne ya faru da yaran. Kaɗan ya rage bata bangaje su Joy da Miracle tai suman gigitaba ta tarota. Kota kansu batabiba ta fara sauka a benen da gudu zane a hannu.
Wani bala'in waro ido tayi akan Nu'aymah tana faɗin, “Jesus John matarka ne da ciki? Cikin jikana ɗanka. Kaima zaka haifi yaronka John ?”. Sai kuma ta nufeta cike da Sassarfa. A take annurin fuskar Aymah ya ɓace ɓat, hakama Yoohan kallon kakar tasa yake yaga mizatayi. A mamakin kowa sai mama debora ta fashe da kuka tana rungume Nu'aymah. Sai kuma ta durƙusa ƙasa ta ɗaura hannunta akan cikin Aymah tana sambatun zance da yare wanda sam Aymah ba ji takeba. Sai dai yanda taga Yoohan ya langaɓe kai yana kallon kakar tasu fuskarsa da murmushi ya sata fahimtar ba mummunan abu mama debora ke faɗi akan gudan jinin nasu ba. Tabbas duk wanda ya kalli mama debora a wannan lokacin yasan farin cikine na gaske tattare da ita. Ba komai yay silarsaba kuma sai cikin jikin Nu'aymah ɗin. Dan kanta batasan yaya akai ƙaunar cikin ta saukar mata ba lokaci ɗaya tare da Nu'aymahn kanta. (Nace Ƙarfin addu'a ce mama debora).
Tana faman sharar ƙwalla ta kamo hannun Yoohan ta zaunar a kusa da Nu'aymah. Ta haɗa hannayensu cikin na juna sannan tai Kneeling a gabansu tare da rufe idanunta duka ta ɗaga hannaye sama ta fara raira waƙar addu'a da yare tana hawaye, ganin hakan yasa su Victoria ma durƙusawa tare da Blessing suka fara tayata suma duk idanu a rufe.
Cike da zaro idanu Nu'aymah ta kalli Yoohan kamar zatai kuka. Dariya taso kufce masa. Amma sai ya gimtse yay murmushi kawai. A cikin kunnenta yace, “Karki damu addu'ar kariya sukema baby dakema ALLAH ya saukeki lafiya cikin ƙoshin lafiya”.
Duk da tasan su ba musulmai bane ta ɗanji sanyi a ranta tunda ba wani tsafi baneba dai. sai kawai ta ɗora kanta a gefen hannunsa tana mai addu'a a ranta itama ALLAH yasa sunada rabon musulinci. Dan tabbas yau taji gaba ɗaya haushin mama debora da takeji ya kwaranye. Dama ance mai ɗa wawa.
Bayan sun gama addu'arsu sun zauna, mama debora nata wani ji da Nu'aymah. Ita dai abin har dariya yake bata. Hakam Yoohan dariya kakar tasa ke basa da gaske. Ta dungure masa kai tana faɗin, “Mara mutunci. kasan matarka nada ciki baka taɓa faɗama kowaba. Yarinyata watansa nawa?”. Ta maida maganar kan Nu'aymah bayan ta zubama Yoohan dake kumbura mata fuska saboda mangarar masa ƙeya da tayi harara.
Haka kawai sai Aymah taji nauyin faɗa. Sai Yoohan ɗinne ya bata amsa. Sai kawai ta tashi ta kama rawa tana waƙar yarensu irinta tsoffi.
A wannan yanayin papa da Madam Chioma da basa gidan suka shigo suka samesu. Gaban Nu'aymah yay mummunan faɗuwa. Da sauri ta shiga karanto addu'a a cikin ranta. Sannan ta yunƙura ta miƙe kamar yanda taga Yoohan ya miƙe fuskarsa a tsuke saboda ganin Momy.
Da wani irin kallo papa kebin Nu'aymah da cikinta. madam Chioma kam Yoohan take kallo kamar wata tsohuwar mayya. Dan sam hankalinta bai kai kan Aymah ba tukkunna.
Cike da farin ciki Mama debora ta nufi papa tana rera waƙarta da ke nuna tana a tsantsar farin ciki na haƙiƙa, hannunsa ta kamo ta nufi inda Nu'aymah take. Da sauri Madam Chioma takai dubanta inda mama debora ta nufa da Papa. Aiki idanunta sukai mata mummunan gani. Da tsanin gigita ta furta, “What??! Impossible!. Na rantse da ALLAH impossible!!!”.
A kusan tare kowa dake a falon ya kalleta, sai kawai ganinta sukai a ƙasa ta sulale sumammiya.
A guje su Destiny sukayi kanta da papa. Yoohan kam fuska ya kauda gefe cike da ƙunar zuciya. Nu'aymah da tasan ba sonta madam Chioma keyiba dama can sai bata ɗauki hakan komaiba face ƙiyayyar da take nuna mata dama can.
Mama debora kam wani irin taɓe baki tayi da faɗin, “Aiko Chioma zaki mutune a haifamin jikana duniya. Kujimin yarinya da baƙin halin baƙin ciki. Ke sanda kika haifi John nayi miki hassada ne? Bandama inada zuciya me ƙyau ai saina saka ayar tambaya a kanki dan Yoohana baya kama dake, nayi shirune kawai dan yana kama da yarona, amma kekam ai kamarma ba ɗanki ba. Sai shi yanzu zaki baƙin ciki matarsa zata haifa masa ɗa. Kema sai kinji abinda naji na rabani da ɗana da kikayi......”
A guje Blessing ta kawo ruwa aka yayyafama Madam Chioma. Tako fasa wata razananniyar ƙara da miƙewa zaune tana nuna Nu'aymah. “Wannan ba cikin yarona bane, kufitarmin da ashawo ɗinnan a gida, na rantse da ALLAH john wannan ba cikinka baneba. Dan hakan bazata taɓa kaswncewaba. Idan baku fitarmin da ita a gidaba zan kasheta. Ku kaita can ta nemo uban cikinta dan bana John bane. Darling narsantse damfararmu yarinyar nan zatayi cikin nan bana John bane. Sun tsafemin yaro sun rabani da shi. Yanzu zasu manna masa cikin kuma da ba nasab.......”
Yanda take surutan zaka ɗauka bata da hankalima sam. Yoohan da takaici ya kume yaja hannun Nu'aymah suka haye sama abinsu batare da yayi ko tariba. Mama debora ma wani dariya da ihu ta sanya tana tafa hannaye. “Chioma kishi da matar ɗanki yasa kin haukace gaskiya. Tunda ni kakar John na yarda cikinsa ne koke da goshpower kukaƙi yarda nasan kishi ne. Yanda nasha baƙin cikin rabani da ɗana da kikayi kema sai kinsha fiye da wannan baƙin cikin na rabuwa da John. Wuuuuuuu!!! She she Shem!!! Wuuuuuu!!!! Hhhhhhhh!!!! Anji kunya uwa mai kishi da matar yaronta!!!!”.