Sashe 18
Sakacina Ko Halin Maza Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
" Ya dai aboki a kwai matsala ko yanayin ka ya nuna a kwai abin da ke damun ka."
Ya kauda kansa gefe ya na faɗin."Kai ma ka san matsalar a kan Zainab ce ta na ba ni ciwon kai lamarin ta a kwai gyara.Na rasa yadda zan ɓullo mata ga kafiya da taurin kai."
A.k ya watsa hannun shi in akan wannan ne be wani dame shi ba yadda ka san auren dole a ka yi musu kullum cikin faɗa."In dai akan wannan ne ba ni da matsala daku kai ba haƙuri ita kuma kafiya ni lamarin ki ya na bani mamaki.Kun fi kusa kun san yadda zaku sasanta kan ku."
Ya faɗa ba tare da wata damuwa ba don ba yau ya saba kawo mishi ƙarar ta ba,kuma ko yaje ba saurarsa take ba gashi shi baya iya haƙuri da fushin ta haka kawai su yi ta sa maka ɓacin rai.
"Ko zamu keɓe ina da wata magana da zan ɗan tautauna a tsakanin mu kuma sirri ce."A.m yace da muryar raɗa ya na kallon gefen matarsa don ya yadda da aminin na sa ba zai gaya mata ba.
"Ki kawo mana abincin falona."Yace sannan suka shge cikin ƙaton falonsa da ya sha gyara ya na ta ƙamshi.Bayan sun ci abinci sun natsa har sai da suka yi salar azahar sannan suka natsa tare da taɓa hirar kasuwancin su.
A.m ya gyara zama ya na kallonsa cikin fuskar tausayi ya fara magana duk da wani gefe na zuciyarsa ta na masa gargaÉ—in karya faÉ—a masa amma ya fara magana da cewa.
" A kwai wani sirri da na ɓoye a raina na san zaka fahimce ni kuma ka ba ni shawara me kyai kamar yadda ka saba,ina ganin kamar na yi wa iyayena rashin adalci da na ɓoye musu cewar ni ne ba na haihuwa bayan ba haka lamarin yake ba.
"Na yi wa Zainab alƙawarin ba zan yi mata kishiya ba kuma ba zan taɓa gaya ma iyayena cewar ba ta haihuwa ba,amma na yi tunanin za ta canza halayenta mu yi zaman lafiya amma kullum ƙara bijiro da abin da zai saka mu samu saɓani,jiya duk ruwan da ake ta na waje wai sun je fati kamar ba matar aure ba,gabaki ɗaya ba ta damuwa da halin da zan shiga in ta ɓata min."
Ya yi shiru ko zai ce wani abu amma be tsinka shi ba sai kallon shi da yake yi ganin haka sai ya É—ora da cewa." Jiya ta kai fagen da na mareta wanda daga baya na yi dana sani.Ka ba ni shawara kar Zainab ta haukani."
A yanayin yadda ya yi maganar sai ya ba shi tausayi,sai dai ya na mamakin wai Zainab ɗin ce bata haihuwa kuma ya yi mata alƙawarin va ze gaya ma iyayen shi ba,sannan ba ya yi mata alƙawarin ba ze ƙara aure ba to wane irin shawara yake son ya ba shi don ya san be wuce yace ya ƙara aure ya samu matar da za ta ba shi yaro ba.
"Gaskiya ka yi wauta kana tunanin in kai ne ba ka haihuwa za ta yadda ta zauna da kai?Kuma ka cuci iyayenka kullum muka haɗu da Daddy sai ya yi min ƙorafin rashin haihuwar ka ya na tausaya maka,ga kuma masoyinka da yake ɓatar da kuɗin shi gurin yi maka sadaka da neman maka magani."
Ya numfasa ya na kallon shi a tsanake yaci gaba da cewa."Wace shawara kake son na ba ka bayan ka yi mata alƙawarin ba zaka ƙara aure ba kasan dai zuriya ta hanyar aure ake samun su,don haka Baban soyayya kaje kuci gaba da soyewa kawai shine shawarar da zan baka."
Abin da A.k yace mishi kenan ya miƙe don ransa ya gama ɓaci.A.m shima miƙewa ya yi don ba shi da abin da ze ce kan shi ya ɗau zafi,shi dai ya san koma mene ne ba zai karya alƙawarin da ya yi mata ba.
Bayan sun fito ya kalli matar A.k da take tattara gurin da yara suka ci abinci ya na dariya."To ni madan zan wuce."Dariya ita ma ta yi "Wato an gama gulmar mu ko ba komai nima ina nan zuwa gidana musha namu."
A.m ya ƙara dariya yana cewa."Baku da dama ne shi yasa musamman mutuniyar ki.A.k ya ja hannun shi ya na faɗin.Muje ka ji in ka biye mata sai ta ɓata maka lokaci da surutun ta suka fice.
******
Juwairiya ta ƙara samun aiki a gidan wata mata mai suna Hajiya Binta,matar ta na da kirki matuƙar gaske yaranta bakwai.Kusan dukkan aikin gidan Juwairiya take yi,saboda yawan yaranta take wahala a gidan sai dai amma babu laifi suna ƙaruwa da ita.Matsalar ta ɗaya mafaɗaciya ce sam ba ta da haƙuri kamar zawo take,duk yadda take taka tsan-tsan amma sai ta rori abin da za ta yi mata faɗa.
Saboda ba ta saba da irin aikin ba sai yake ba ta wahala ƙwarai,in ta dawo aiki ba ta iya taɓuka wani aikin watarana ma sai tasha maganin ciwon jiki.
Ganin irin wahalar da take sha Mama ta ba ta shawarar ta haƙura da aikin,amma ta nace sai ta yi musamman da ta ga kuɗin aikin na ta da tsoka.
Yaran matar kwata-kwata basu da mutunci ga rashin kunya abu kaÉ—an za su hauta da zagi suna ci mata mutunci,mahaifiyarsu kuma ba ta son ganin laifin É—anta hakan ya sa ba ta kula su.
Abin da ya ƙara tsorata ta ganin sun girme mata ƙaramar cikin su ita ce take tunanin za su zo tsara da juna.
Hatta wankin su ita take yi musu don tsabar rashin mutunci harda pant da breziya suke ba ta wanki,amma ta yi haƙuri ta jure burinta ta samu abin da za su dinga ci.
Sai dai rashin mutuncin da suke mata da ta fahimci ba me ƙarewa bane ta yi tsalle ta fara nuna musu sam ba za ta ɗauka ba.
Hakan ya saka suka ƙara saka mata ƙahon zuƙa,domin zuciyar su tsabar hassada ce suna ƙyashin kyan da Allah ya yi mata musamman da suka ga sun ɓata jikinsu da mayukan bilicin.
Abin da Hajiya Binta ta tsira ya sa Juwairiya ta ji aikin ya fita a ranta,saboda kullum ta zo sai ta tuhumeta da cewar ta yi mata sata.Hakan ya tinzira ta ta saka a ranta duk ranar da ta ƙara za ta bar mata aikin ta.
Haka kuwa aka yi taƙi zuwa aikin bayan kwana biyu da barin aikin sai ga motar ƴan sanda da Hajiya Binta akan Juwairiya ta sace mata sarƙar gwal ɗin ta.
Juwairiya ta shiga cikin tsananin tashin hankali ganin yadda ɗan sandan yake ƙoƙarin tasa ta zuwa ofis ɗinsu,hankalinta ya tashi matuƙa ya dinga kuka tana rantsuwar ba ta ɗauka ba.Tsananin tashin hankalin da Mama ta shiga ba'a magana duk da ta san halinta,amma sai ta shiga ruɗu ta din ga tamabayarta da in ta san inda yake ta fito mata da shi,hakan ya saka Juwairiya cikin tashin hankali ta dinga wani irin kuka gani take kamar Mama ba ta yadda da ita ba.
Baba Sani ya sami abin da yake so don haka ya ƙara zuga Hajiya Binta kan ta tafi da ita ofishin ɗan sanda,burinsa ya cika dama tintuni yake addu'ar Allah ya sa haka ya faru.
Mama na gani aka tafi da Juwairiya ta na wani irin kuka gani take kamar dukan ta zasu ta yi har sai ta amsa laifin da ba ta aikata ba.Ganin an tafi da ita Mama ta nufi hanyar shiga cikin gida ranta na wani irin suya,hango halin da Juwairiya take ciki da yadda take kuka ta na kiran sunan ta,sai kawai gani akai ta yanke jiki ta faɗi ƙasa.
Hankalin Mariya ya tashi matuƙa wacce take zaune a ƙasa ta na kuka sosai,gani take kamar ita ta saka ta a cikin wannan hali saboda hanyar aikin da ta yi mata.
Ita da mahaifiyar ta suka kama Mama suka shigar da ita gida,sai dai daga baya kan dole suka kwasheta zuwa asibiti ganin numfashinta na É—aukewa gashi ta na aman jini!
Baba Sani ya yi matuƙar jin daɗin faruwar lamarin duk da ba shi da shiri akan hakan sai dai ya na ganin yanzu ne burinsa zai cika akanta,don ya tabbata basu da wanda zai yi belin ta hakan zai ba shi damar ɗora mata sharaɗin zai yi belinta amma sai ta amince za ta yadda da buƙatarsa,don haka ma yaƙi zuwa ogishin da nufin sai sun yi mata dukan kawo wuƙa ta galabaita saboda ya san ta a kwai kafiya.
Juwairiya na zaune a cikin cell ɗin ta ƙudundune kanta a cikin jikinta tun da suka kawota take kuka,tunanin halin da Mama take ciki yake damunta wani irin sauro da yake damunta da ihu da cizo,yasa take ta zubar jawaye ga yunwa dake ƙwaƙularta."Rabbi inni lima anzalta ilayya min khairin faƙir."Abin da bakinta yake faɗi kenan cikin tsananin tashin hankali.
Tun da Hajiya Binta ta kawota ba ta ƙara zuwa ba sai washegari da safe lokacin ta matuƙar galabaita,bayan sun tuhumeta amma taƙi amsa laifinta dukan tsiya suka yi mata sannan aka maida ta.
Da rana sai ga Baba Sani ya shigo ofishin ya na zare ido,gurinta yazo ya na kallonta." Kin ga abin da kika jawo ma kanki kosaboda shegen taurin ranki.'Yace ya na kallonta duk da ita ba shi take kallo ba saboda taƙi ta kalleshi wani irin tsanar sa take ji matuƙa.
" Har yanzu kina da dama zan iya fitar dake amma sai kin amince za ki yadda da buƙatata."Yace da ita ya na kashe murya.
Wani irin kallo ta watsa mishi " Allah ya yi min tsari da mugun nufin ka,da na amince gara na tabbata a gurin nan ko ya zamo shine ajalina."
"Ok haka kika ce ko?To ai shikenan kuɗina ya huta tunna kin zaɓi rayuwar zuwa gidan mutane kina sata."Yace tare da watsa mata harara ya fice daga ofishin,kuka ta saka tare da cigaba da addu'ar ta ta na roƙon Allah ya kawo mata mafita.
Ya kauda kansa gefe ya na faɗin."Kai ma ka san matsalar a kan Zainab ce ta na ba ni ciwon kai lamarin ta a kwai gyara.Na rasa yadda zan ɓullo mata ga kafiya da taurin kai."
A.k ya watsa hannun shi in akan wannan ne be wani dame shi ba yadda ka san auren dole a ka yi musu kullum cikin faɗa."In dai akan wannan ne ba ni da matsala daku kai ba haƙuri ita kuma kafiya ni lamarin ki ya na bani mamaki.Kun fi kusa kun san yadda zaku sasanta kan ku."
Ya faɗa ba tare da wata damuwa ba don ba yau ya saba kawo mishi ƙarar ta ba,kuma ko yaje ba saurarsa take ba gashi shi baya iya haƙuri da fushin ta haka kawai su yi ta sa maka ɓacin rai.
"Ko zamu keɓe ina da wata magana da zan ɗan tautauna a tsakanin mu kuma sirri ce."A.m yace da muryar raɗa ya na kallon gefen matarsa don ya yadda da aminin na sa ba zai gaya mata ba.
"Ki kawo mana abincin falona."Yace sannan suka shge cikin ƙaton falonsa da ya sha gyara ya na ta ƙamshi.Bayan sun ci abinci sun natsa har sai da suka yi salar azahar sannan suka natsa tare da taɓa hirar kasuwancin su.
A.m ya gyara zama ya na kallonsa cikin fuskar tausayi ya fara magana duk da wani gefe na zuciyarsa ta na masa gargaÉ—in karya faÉ—a masa amma ya fara magana da cewa.
" A kwai wani sirri da na ɓoye a raina na san zaka fahimce ni kuma ka ba ni shawara me kyai kamar yadda ka saba,ina ganin kamar na yi wa iyayena rashin adalci da na ɓoye musu cewar ni ne ba na haihuwa bayan ba haka lamarin yake ba.
"Na yi wa Zainab alƙawarin ba zan yi mata kishiya ba kuma ba zan taɓa gaya ma iyayena cewar ba ta haihuwa ba,amma na yi tunanin za ta canza halayenta mu yi zaman lafiya amma kullum ƙara bijiro da abin da zai saka mu samu saɓani,jiya duk ruwan da ake ta na waje wai sun je fati kamar ba matar aure ba,gabaki ɗaya ba ta damuwa da halin da zan shiga in ta ɓata min."
Ya yi shiru ko zai ce wani abu amma be tsinka shi ba sai kallon shi da yake yi ganin haka sai ya É—ora da cewa." Jiya ta kai fagen da na mareta wanda daga baya na yi dana sani.Ka ba ni shawara kar Zainab ta haukani."
A yanayin yadda ya yi maganar sai ya ba shi tausayi,sai dai ya na mamakin wai Zainab ɗin ce bata haihuwa kuma ya yi mata alƙawarin va ze gaya ma iyayen shi ba,sannan ba ya yi mata alƙawarin ba ze ƙara aure ba to wane irin shawara yake son ya ba shi don ya san be wuce yace ya ƙara aure ya samu matar da za ta ba shi yaro ba.
"Gaskiya ka yi wauta kana tunanin in kai ne ba ka haihuwa za ta yadda ta zauna da kai?Kuma ka cuci iyayenka kullum muka haɗu da Daddy sai ya yi min ƙorafin rashin haihuwar ka ya na tausaya maka,ga kuma masoyinka da yake ɓatar da kuɗin shi gurin yi maka sadaka da neman maka magani."
Ya numfasa ya na kallon shi a tsanake yaci gaba da cewa."Wace shawara kake son na ba ka bayan ka yi mata alƙawarin ba zaka ƙara aure ba kasan dai zuriya ta hanyar aure ake samun su,don haka Baban soyayya kaje kuci gaba da soyewa kawai shine shawarar da zan baka."
Abin da A.k yace mishi kenan ya miƙe don ransa ya gama ɓaci.A.m shima miƙewa ya yi don ba shi da abin da ze ce kan shi ya ɗau zafi,shi dai ya san koma mene ne ba zai karya alƙawarin da ya yi mata ba.
Bayan sun fito ya kalli matar A.k da take tattara gurin da yara suka ci abinci ya na dariya."To ni madan zan wuce."Dariya ita ma ta yi "Wato an gama gulmar mu ko ba komai nima ina nan zuwa gidana musha namu."
A.m ya ƙara dariya yana cewa."Baku da dama ne shi yasa musamman mutuniyar ki.A.k ya ja hannun shi ya na faɗin.Muje ka ji in ka biye mata sai ta ɓata maka lokaci da surutun ta suka fice.
******
Juwairiya ta ƙara samun aiki a gidan wata mata mai suna Hajiya Binta,matar ta na da kirki matuƙar gaske yaranta bakwai.Kusan dukkan aikin gidan Juwairiya take yi,saboda yawan yaranta take wahala a gidan sai dai amma babu laifi suna ƙaruwa da ita.Matsalar ta ɗaya mafaɗaciya ce sam ba ta da haƙuri kamar zawo take,duk yadda take taka tsan-tsan amma sai ta rori abin da za ta yi mata faɗa.
Saboda ba ta saba da irin aikin ba sai yake ba ta wahala ƙwarai,in ta dawo aiki ba ta iya taɓuka wani aikin watarana ma sai tasha maganin ciwon jiki.
Ganin irin wahalar da take sha Mama ta ba ta shawarar ta haƙura da aikin,amma ta nace sai ta yi musamman da ta ga kuɗin aikin na ta da tsoka.
Yaran matar kwata-kwata basu da mutunci ga rashin kunya abu kaÉ—an za su hauta da zagi suna ci mata mutunci,mahaifiyarsu kuma ba ta son ganin laifin É—anta hakan ya sa ba ta kula su.
Abin da ya ƙara tsorata ta ganin sun girme mata ƙaramar cikin su ita ce take tunanin za su zo tsara da juna.
Hatta wankin su ita take yi musu don tsabar rashin mutunci harda pant da breziya suke ba ta wanki,amma ta yi haƙuri ta jure burinta ta samu abin da za su dinga ci.
Sai dai rashin mutuncin da suke mata da ta fahimci ba me ƙarewa bane ta yi tsalle ta fara nuna musu sam ba za ta ɗauka ba.
Hakan ya saka suka ƙara saka mata ƙahon zuƙa,domin zuciyar su tsabar hassada ce suna ƙyashin kyan da Allah ya yi mata musamman da suka ga sun ɓata jikinsu da mayukan bilicin.
Abin da Hajiya Binta ta tsira ya sa Juwairiya ta ji aikin ya fita a ranta,saboda kullum ta zo sai ta tuhumeta da cewar ta yi mata sata.Hakan ya tinzira ta ta saka a ranta duk ranar da ta ƙara za ta bar mata aikin ta.
Haka kuwa aka yi taƙi zuwa aikin bayan kwana biyu da barin aikin sai ga motar ƴan sanda da Hajiya Binta akan Juwairiya ta sace mata sarƙar gwal ɗin ta.
Juwairiya ta shiga cikin tsananin tashin hankali ganin yadda ɗan sandan yake ƙoƙarin tasa ta zuwa ofis ɗinsu,hankalinta ya tashi matuƙa ya dinga kuka tana rantsuwar ba ta ɗauka ba.Tsananin tashin hankalin da Mama ta shiga ba'a magana duk da ta san halinta,amma sai ta shiga ruɗu ta din ga tamabayarta da in ta san inda yake ta fito mata da shi,hakan ya saka Juwairiya cikin tashin hankali ta dinga wani irin kuka gani take kamar Mama ba ta yadda da ita ba.
Baba Sani ya sami abin da yake so don haka ya ƙara zuga Hajiya Binta kan ta tafi da ita ofishin ɗan sanda,burinsa ya cika dama tintuni yake addu'ar Allah ya sa haka ya faru.
Mama na gani aka tafi da Juwairiya ta na wani irin kuka gani take kamar dukan ta zasu ta yi har sai ta amsa laifin da ba ta aikata ba.Ganin an tafi da ita Mama ta nufi hanyar shiga cikin gida ranta na wani irin suya,hango halin da Juwairiya take ciki da yadda take kuka ta na kiran sunan ta,sai kawai gani akai ta yanke jiki ta faɗi ƙasa.
Hankalin Mariya ya tashi matuƙa wacce take zaune a ƙasa ta na kuka sosai,gani take kamar ita ta saka ta a cikin wannan hali saboda hanyar aikin da ta yi mata.
Ita da mahaifiyar ta suka kama Mama suka shigar da ita gida,sai dai daga baya kan dole suka kwasheta zuwa asibiti ganin numfashinta na É—aukewa gashi ta na aman jini!
Baba Sani ya yi matuƙar jin daɗin faruwar lamarin duk da ba shi da shiri akan hakan sai dai ya na ganin yanzu ne burinsa zai cika akanta,don ya tabbata basu da wanda zai yi belin ta hakan zai ba shi damar ɗora mata sharaɗin zai yi belinta amma sai ta amince za ta yadda da buƙatarsa,don haka ma yaƙi zuwa ogishin da nufin sai sun yi mata dukan kawo wuƙa ta galabaita saboda ya san ta a kwai kafiya.
Juwairiya na zaune a cikin cell ɗin ta ƙudundune kanta a cikin jikinta tun da suka kawota take kuka,tunanin halin da Mama take ciki yake damunta wani irin sauro da yake damunta da ihu da cizo,yasa take ta zubar jawaye ga yunwa dake ƙwaƙularta."Rabbi inni lima anzalta ilayya min khairin faƙir."Abin da bakinta yake faɗi kenan cikin tsananin tashin hankali.
Tun da Hajiya Binta ta kawota ba ta ƙara zuwa ba sai washegari da safe lokacin ta matuƙar galabaita,bayan sun tuhumeta amma taƙi amsa laifinta dukan tsiya suka yi mata sannan aka maida ta.
Da rana sai ga Baba Sani ya shigo ofishin ya na zare ido,gurinta yazo ya na kallonta." Kin ga abin da kika jawo ma kanki kosaboda shegen taurin ranki.'Yace ya na kallonta duk da ita ba shi take kallo ba saboda taƙi ta kalleshi wani irin tsanar sa take ji matuƙa.
" Har yanzu kina da dama zan iya fitar dake amma sai kin amince za ki yadda da buƙatata."Yace da ita ya na kashe murya.
Wani irin kallo ta watsa mishi " Allah ya yi min tsari da mugun nufin ka,da na amince gara na tabbata a gurin nan ko ya zamo shine ajalina."
"Ok haka kika ce ko?To ai shikenan kuɗina ya huta tunna kin zaɓi rayuwar zuwa gidan mutane kina sata."Yace tare da watsa mata harara ya fice daga ofishin,kuka ta saka tare da cigaba da addu'ar ta ta na roƙon Allah ya kawo mata mafita.