Sashe 14
Sakacina Ko Halin Maza Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri ta matsa za ta bi ta bayansa ta shige cikin gidan da ya bake ƙofar,amma sai ya daka mata tsawa tare da jan hijabinta."Ina zaki ƴar iska maza dawo,iskancin naki ya kai har a kawo ki gida a mota.Kawai sai ya saka salati da ƙarfin sa ya ci gaba da cewa."Inna lillahi gara da ka mutu Yaya Ahmed in da ka na raye Juwairiya ita za ta ƙashe ka.Karuwa kika zama fa ke ko kunya duniya ba za ki jiba tunna baki ji na Allah ba."
"Ashsha!Subuhanallahi haba Malam ya za ka dinga jifan ta da waÉ—annan muggan kalamai?Iya sani na Juwairiya yarinyar kirki ne ta É—aÉ—e ta na tare damu ta na mana aiki.Yanzu haka mun daidaita ne nake son ka bani auren ta,ma'ana na yaba da hankalinta ina sonta."
Wayyo Allah faɗin haka da ya yi wato ya na son Juwairiya ji Baba Sani ya yi kamar ya watsa mishi fetur ya kyasta ashana domin baƙin cikin sa biyu ne a kan maganar.Na farko ta ya ya za 'ai mutum me hannu da shuni yace ya na sonta,sannan kuma baƙin kishinta ya taso ya lulluɓe mishi zuciyarsa kawai sai ya ƙara kuka ya na faɗin ma abokin da suke hira cewar."Kaji ko wai na ba shi aurenta bayan ya gama iskanci da ita ni nasan ya na naɗe tabarmar kunya ne.Amma ta ya ya zai auri mazinaciya!Ba Juwairiya dake tsaye ta na kuka ba har ta Daddyn Abnaj sai da yaji wani irin abu ya soke shi ya rintse idanunsa ya na jin kamar ya shaƙo wuyar Baba Sani,take ya fahimci wani abu wato na zaman ƙunci da suke yi iya zaman su da ita bata taɓa basu labari ba,duk da ya san cewa ba lai-lai bane ta gaya musu kasancewar ta na da zurfin ciki.
Ya kalli Juwairiya da ta ƙara sautin kukan ta ganin mutane sun fara taruwa Baba Sani yaci gaba da magana da ƙarfi ya na nanatawa,sai ta ruga da gudu dai-dai lokacin da Baba Sani ya kai mata bugu a bayanta.
Ba ta san ya suka ƙare ba ya dai shigo gida ya na ta faɗa tare da ja mata jifa'i kala-kala, Juwairiya ta so ta tanka saboda abin da ya yi mata a gaban mutumim da yake girmama lamarin ta,amma Mama ta hana duk san da ya gaya mata baƙa ta buɗe baki za ta yi magana Mama za ta hana ta,har ya gaji da rashin mutuncinsa ya fice.
A ranar Juwairiya ta ci kuka sosai ta ji ta ƙara mugun tsanar shi a ranta.
Washegari ganin taƙi shiryawa taje aiki Mama ta shigo ɗakin ta tsaya ta na kallonta tace."Juwairiya ba zaki je aiki bane naga rana ta yi."
"Na haƙura da aikin Mama gara na zauna a gida dama kin san mun yanke shawarar na daina zuwa,sai ga abin da Baba Sani ya yi min a gaban shi Allah kunya nake ji matuƙa.Karuwa ya kira ni."Sai kawai ta saka kuka ta na jin zafin kalmar da ya danganta ta da ita."
Mama a ranta har tafi Juwairiya damuwa amma sai ta ɗan gyara murya tace."Ki yi haƙuri komai lokaci ne watarana sai ya yi dana sani,amma da kin daure kije kila ma ya shafa miki lafiya don na tabbata ba zai ƙara miki maganar soyayya ba,ganin yadda ya tozar taki."
"To Mama shikenan a haka rayuwata za ta ƙare duk wanda ya fito neman aurena sai Baba Sani ya ɓata lamarin gaskiya na gaji."Tace cikin hawaye yayin da ta tuna katoɓarar da ta yi na faɗin hakan,kamar ta nuna ta na son auren kenan sai ta zari hijabinta da sauri ta fice zuwa aiki.
Ko da ta isa bata sami Anty Naja ba duk da ta san dama abu ne me wuya ta same ta,abin mamaki ta yi sallama ta shiga fuskarta babu walwala,sai ta same shi zaune akan one siter ya zuba tagumi ya na kallon hanya,ganin ta ya saka shi sakin ajiyar zuciya mai ƙarfin gaske.
"Shigo mana Juwairiya hankalina ya tashi matuƙa na yi zaton wannan mara kirkin Baban nan naki ya hanaki zuwa "Yace da ita ganin ta dogare a bakin ƙofa,ta ɗan tsaya ta na kallon shi sai kuma ta ƙara haɗe fuska haushin sa take ji don shi ya yi shishshigi a lamarinta,har ya saka Bab Sani ya yi mata wannan tozarcin.
"Gaskiya ban ji daɗin abin da ya faru ba!Haba sai kace ba ƙanin mahaifinki ba.Lamarinsa ya tsoratani baƙin cikina yadda yaƙi yadda da maganata akan ina sonki da aure.Kawai ki gaya min dangin ku naje can na nemi aurenki."
Yace da ita ya na kare mata kallo don ya fahimci a wani hali take,takaici ya kamata jin abin da ya faɗa sai ta miƙe hanyar kicin ba tare da tace mishi komai ba.
Gabanta ya sha tare da riƙe mata hijabi yace."Na fa fara ƙosawa da halin ko in kula da kike min haba waike dutse ne a ƙirjin ki ba zuciya ba!Ki ji tausayina ko don halin da kike ciki ki zaɓe ni a matsayin mijin ki hatta mahaifiyarki ba za ta zauna a wannan gida ba.
Takai hannu da nufin ta ƙwace hijabinta sai ya riƙe hannun cikin kalar tausayi ya na jin kamar ya yi mata kuka,ganin sam ba ta da rangwame akan soyayya.Baki ta buɗe da nufin ta yi magana sai suka ji sallamar Anty Naja ta shigo da sauri da alamun gajiya tare da ita.
Da sauri ya saki hannunta ya matsa gefe ya na zare ido,ita ma cikin tashin hankali ta tsaya ta kasa haÉ—a ido da ita ta na jiran tashi n hankalin da za ta fuskanta.
Amma sai dukansu ta basu mamaki ta faɗa kan kujera ta na lumshe ido "Wash Allah! Na gaji matuƙa Juwairiya bani ruwa don Allah."Tace cikin sakin fuska ba tare da ta fahimci komai ba."
Da sauri Juwairiya ta shige kicin ta na mamakin sokanci irin nata haba ta ya ya za'ai tace bata fahimci komai ba.Bayan ta kawo mata ruwan ta haɗo har da abin motsa baki,ta shige kicin ta ci gaba da aiyukan ta can sai ga shi ya shigo yace."Ina jiranki in kin gama zaki tafi ina hanyar da nake tsayawa sai mu ƙarashe tautaunawar.
Ganin ba zai saduda ba Mama tace ta haƙura da aikin in ta bata kuɗin aikin ta na wata haka kuwa aka yi,bayan ta yi mata albashi ta ƙara mata harda zannuwa masu kyau biyu nata sai ɗaya Mama ta ɗinka,kasancewar suna da biki a family ɗin su kuma tare da Juwairiya za su tafi garin Kano.
Hankalin Anty Naja ya tashi matuƙa ganin ba ta zo aiki ba,ta shiga ruɗani ta din ga tunanin ko ta yi mata wani abu amma bata gano ba.Shi ma hankalinsa ya tashi sosai duk da yaso sai sun gama daidaitawa a tsakanin su sai tabar aikin,amma ta yi sauri gashi ya na son yaje gidan ya na tsoron tijararren ƙanin mahaifinta
Sai ya azalzala ma Anty Naja ta shirya ya kaita har ya na mata barazana da ya na nan akan bakan sa in dai ba Juwairiya ba sai dai ta bar aikin,ai kuwa ba shiri ta shirya suka taho ya ijeta a kofar gidan ta shiga ciki ya zauna da yaransa ya na jiran ta fito,burin sa ya ga Juwairiya.
Juwairiya na tsakar ta na girki Mama ta na zaune ta na jan carbi ta yi sallama ta shigo,da sauri Juwairiya ta saka hannu ta rufe fuskarta ta na dariya.
Anty Naja ta harareta ta na kallon Mama tace."Da ma Mama haka Juwairiya take bata da kirki? Kawai ta guje mu ba tare da mun yi mata wani abu ba,hankalina ya tashi ƙwarai Mama gaskiya ba ta kyauta ba."
Ta ƙarashe maganar ta na kallon Juwairiya sannan ta ɗora da cewa "Ko mun yi miki wani abu ne?Ai gaya mana ya kamata ki yi ba ki ɗauke kafafunki ba.Ni da yara da Daddyn su Abnaj duk hankalin mu ya tashi."
Mama ita ba tace komai ba tace komai ba sai dariyar yaƙe take mata,bayan sun shiga ɗaki suka yi gaisuwa a tsakanin su sanann shiru ya biyo baya.Sannan Anty Naja ta katse shirun tace."Me ya faru Mama kwana biyu bata zo aiki ba na yi tunanin ko wani ba lafiya,amma da nazo naga kowa lafiya.Ko na yi laifi ne Mama."
Matuƙar kunya sai ya lulluɓe Mam ta ji kamar ta nitse ta rasa yadda za ta fara mata bayani,har Juwairiya ta yi sallama ta shigo,ganin Mama ta kasa mata bayani ta kalli Juwairiya tace."To ko auren ne ya zo,in kuma wannan ne Mama ai ni ce me haɗo kayan ɗaki ko?"Ta ƙarashe maganar ta na me tsigar tambaya.
I ta dai Juwairiya ba tace komai ba ta na ta wasa da yatsunta,Mama ta daure tace."Ba shi bane ban san dai yadda zaki ɗauki zancen bane shi yasa na kasa sanar miki,amma ranar wanka ba'a ɓoyan ciji."
Gaban Anty Naja ya faɗi daram!Sai ta ji zuciyar ta ta raya mata lai-lai a kwai abin da suke ɓoye mata,duk da bata san ko menene ba amma taji ta firgita Allah ya sa ba wani lamari me girma ya faru ba.
Ganin ta yi shiru ba tace komai ba jikinta ya yi sanyi Mama dai ta daure tace."Dama mijinki ya bijiro da wata magana ya na son auren Juwairiya har ya shigo da maganar gida,mu kuma muka ga rashin dacewar haka saboda irin halaccin da kika yi mana shi yasa nace ta dakata da aikin kawai ki nemi wani."Tace ta na karantar fuskarta.
Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi na Tara.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_.
Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakaƙuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce.
Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani.
*FOLLOW, READ, COMMENT, SHARE*
*SAKACINA KO HALIN MAZA?*
*RUBUTAWA:-*
*JAMILA LAWAL ZANGO*
*SADAUKARWA GA:-*
*SUMMY M NA'IGE*
_(Aminiya)_
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO....*
*SHAFI NA TARA*
"Ashsha!Subuhanallahi haba Malam ya za ka dinga jifan ta da waÉ—annan muggan kalamai?Iya sani na Juwairiya yarinyar kirki ne ta É—aÉ—e ta na tare damu ta na mana aiki.Yanzu haka mun daidaita ne nake son ka bani auren ta,ma'ana na yaba da hankalinta ina sonta."
Wayyo Allah faɗin haka da ya yi wato ya na son Juwairiya ji Baba Sani ya yi kamar ya watsa mishi fetur ya kyasta ashana domin baƙin cikin sa biyu ne a kan maganar.Na farko ta ya ya za 'ai mutum me hannu da shuni yace ya na sonta,sannan kuma baƙin kishinta ya taso ya lulluɓe mishi zuciyarsa kawai sai ya ƙara kuka ya na faɗin ma abokin da suke hira cewar."Kaji ko wai na ba shi aurenta bayan ya gama iskanci da ita ni nasan ya na naɗe tabarmar kunya ne.Amma ta ya ya zai auri mazinaciya!Ba Juwairiya dake tsaye ta na kuka ba har ta Daddyn Abnaj sai da yaji wani irin abu ya soke shi ya rintse idanunsa ya na jin kamar ya shaƙo wuyar Baba Sani,take ya fahimci wani abu wato na zaman ƙunci da suke yi iya zaman su da ita bata taɓa basu labari ba,duk da ya san cewa ba lai-lai bane ta gaya musu kasancewar ta na da zurfin ciki.
Ya kalli Juwairiya da ta ƙara sautin kukan ta ganin mutane sun fara taruwa Baba Sani yaci gaba da magana da ƙarfi ya na nanatawa,sai ta ruga da gudu dai-dai lokacin da Baba Sani ya kai mata bugu a bayanta.
Ba ta san ya suka ƙare ba ya dai shigo gida ya na ta faɗa tare da ja mata jifa'i kala-kala, Juwairiya ta so ta tanka saboda abin da ya yi mata a gaban mutumim da yake girmama lamarin ta,amma Mama ta hana duk san da ya gaya mata baƙa ta buɗe baki za ta yi magana Mama za ta hana ta,har ya gaji da rashin mutuncinsa ya fice.
A ranar Juwairiya ta ci kuka sosai ta ji ta ƙara mugun tsanar shi a ranta.
Washegari ganin taƙi shiryawa taje aiki Mama ta shigo ɗakin ta tsaya ta na kallonta tace."Juwairiya ba zaki je aiki bane naga rana ta yi."
"Na haƙura da aikin Mama gara na zauna a gida dama kin san mun yanke shawarar na daina zuwa,sai ga abin da Baba Sani ya yi min a gaban shi Allah kunya nake ji matuƙa.Karuwa ya kira ni."Sai kawai ta saka kuka ta na jin zafin kalmar da ya danganta ta da ita."
Mama a ranta har tafi Juwairiya damuwa amma sai ta ɗan gyara murya tace."Ki yi haƙuri komai lokaci ne watarana sai ya yi dana sani,amma da kin daure kije kila ma ya shafa miki lafiya don na tabbata ba zai ƙara miki maganar soyayya ba,ganin yadda ya tozar taki."
"To Mama shikenan a haka rayuwata za ta ƙare duk wanda ya fito neman aurena sai Baba Sani ya ɓata lamarin gaskiya na gaji."Tace cikin hawaye yayin da ta tuna katoɓarar da ta yi na faɗin hakan,kamar ta nuna ta na son auren kenan sai ta zari hijabinta da sauri ta fice zuwa aiki.
Ko da ta isa bata sami Anty Naja ba duk da ta san dama abu ne me wuya ta same ta,abin mamaki ta yi sallama ta shiga fuskarta babu walwala,sai ta same shi zaune akan one siter ya zuba tagumi ya na kallon hanya,ganin ta ya saka shi sakin ajiyar zuciya mai ƙarfin gaske.
"Shigo mana Juwairiya hankalina ya tashi matuƙa na yi zaton wannan mara kirkin Baban nan naki ya hanaki zuwa "Yace da ita ganin ta dogare a bakin ƙofa,ta ɗan tsaya ta na kallon shi sai kuma ta ƙara haɗe fuska haushin sa take ji don shi ya yi shishshigi a lamarinta,har ya saka Bab Sani ya yi mata wannan tozarcin.
"Gaskiya ban ji daɗin abin da ya faru ba!Haba sai kace ba ƙanin mahaifinki ba.Lamarinsa ya tsoratani baƙin cikina yadda yaƙi yadda da maganata akan ina sonki da aure.Kawai ki gaya min dangin ku naje can na nemi aurenki."
Yace da ita ya na kare mata kallo don ya fahimci a wani hali take,takaici ya kamata jin abin da ya faɗa sai ta miƙe hanyar kicin ba tare da tace mishi komai ba.
Gabanta ya sha tare da riƙe mata hijabi yace."Na fa fara ƙosawa da halin ko in kula da kike min haba waike dutse ne a ƙirjin ki ba zuciya ba!Ki ji tausayina ko don halin da kike ciki ki zaɓe ni a matsayin mijin ki hatta mahaifiyarki ba za ta zauna a wannan gida ba.
Takai hannu da nufin ta ƙwace hijabinta sai ya riƙe hannun cikin kalar tausayi ya na jin kamar ya yi mata kuka,ganin sam ba ta da rangwame akan soyayya.Baki ta buɗe da nufin ta yi magana sai suka ji sallamar Anty Naja ta shigo da sauri da alamun gajiya tare da ita.
Da sauri ya saki hannunta ya matsa gefe ya na zare ido,ita ma cikin tashin hankali ta tsaya ta kasa haÉ—a ido da ita ta na jiran tashi n hankalin da za ta fuskanta.
Amma sai dukansu ta basu mamaki ta faɗa kan kujera ta na lumshe ido "Wash Allah! Na gaji matuƙa Juwairiya bani ruwa don Allah."Tace cikin sakin fuska ba tare da ta fahimci komai ba."
Da sauri Juwairiya ta shige kicin ta na mamakin sokanci irin nata haba ta ya ya za'ai tace bata fahimci komai ba.Bayan ta kawo mata ruwan ta haɗo har da abin motsa baki,ta shige kicin ta ci gaba da aiyukan ta can sai ga shi ya shigo yace."Ina jiranki in kin gama zaki tafi ina hanyar da nake tsayawa sai mu ƙarashe tautaunawar.
Ganin ba zai saduda ba Mama tace ta haƙura da aikin in ta bata kuɗin aikin ta na wata haka kuwa aka yi,bayan ta yi mata albashi ta ƙara mata harda zannuwa masu kyau biyu nata sai ɗaya Mama ta ɗinka,kasancewar suna da biki a family ɗin su kuma tare da Juwairiya za su tafi garin Kano.
Hankalin Anty Naja ya tashi matuƙa ganin ba ta zo aiki ba,ta shiga ruɗani ta din ga tunanin ko ta yi mata wani abu amma bata gano ba.Shi ma hankalinsa ya tashi sosai duk da yaso sai sun gama daidaitawa a tsakanin su sai tabar aikin,amma ta yi sauri gashi ya na son yaje gidan ya na tsoron tijararren ƙanin mahaifinta
Sai ya azalzala ma Anty Naja ta shirya ya kaita har ya na mata barazana da ya na nan akan bakan sa in dai ba Juwairiya ba sai dai ta bar aikin,ai kuwa ba shiri ta shirya suka taho ya ijeta a kofar gidan ta shiga ciki ya zauna da yaransa ya na jiran ta fito,burin sa ya ga Juwairiya.
Juwairiya na tsakar ta na girki Mama ta na zaune ta na jan carbi ta yi sallama ta shigo,da sauri Juwairiya ta saka hannu ta rufe fuskarta ta na dariya.
Anty Naja ta harareta ta na kallon Mama tace."Da ma Mama haka Juwairiya take bata da kirki? Kawai ta guje mu ba tare da mun yi mata wani abu ba,hankalina ya tashi ƙwarai Mama gaskiya ba ta kyauta ba."
Ta ƙarashe maganar ta na kallon Juwairiya sannan ta ɗora da cewa "Ko mun yi miki wani abu ne?Ai gaya mana ya kamata ki yi ba ki ɗauke kafafunki ba.Ni da yara da Daddyn su Abnaj duk hankalin mu ya tashi."
Mama ita ba tace komai ba tace komai ba sai dariyar yaƙe take mata,bayan sun shiga ɗaki suka yi gaisuwa a tsakanin su sanann shiru ya biyo baya.Sannan Anty Naja ta katse shirun tace."Me ya faru Mama kwana biyu bata zo aiki ba na yi tunanin ko wani ba lafiya,amma da nazo naga kowa lafiya.Ko na yi laifi ne Mama."
Matuƙar kunya sai ya lulluɓe Mam ta ji kamar ta nitse ta rasa yadda za ta fara mata bayani,har Juwairiya ta yi sallama ta shigo,ganin Mama ta kasa mata bayani ta kalli Juwairiya tace."To ko auren ne ya zo,in kuma wannan ne Mama ai ni ce me haɗo kayan ɗaki ko?"Ta ƙarashe maganar ta na me tsigar tambaya.
I ta dai Juwairiya ba tace komai ba ta na ta wasa da yatsunta,Mama ta daure tace."Ba shi bane ban san dai yadda zaki ɗauki zancen bane shi yasa na kasa sanar miki,amma ranar wanka ba'a ɓoyan ciji."
Gaban Anty Naja ya faɗi daram!Sai ta ji zuciyar ta ta raya mata lai-lai a kwai abin da suke ɓoye mata,duk da bata san ko menene ba amma taji ta firgita Allah ya sa ba wani lamari me girma ya faru ba.
Ganin ta yi shiru ba tace komai ba jikinta ya yi sanyi Mama dai ta daure tace."Dama mijinki ya bijiro da wata magana ya na son auren Juwairiya har ya shigo da maganar gida,mu kuma muka ga rashin dacewar haka saboda irin halaccin da kika yi mana shi yasa nace ta dakata da aikin kawai ki nemi wani."Tace ta na karantar fuskarta.
Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haɗu a shafi na Tara.Ga masu buƙatar shiga cikin group ɗina na whatsapp ga numba 08144072423_.
Kuma ƙofa a buɗe take na ƙorafi gyara ko ƙarin bayani ga zakaƙuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce.
Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaƙauran marubuciya,kuma ƙawata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ƙara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani.
*FOLLOW, READ, COMMENT, SHARE*
*SAKACINA KO HALIN MAZA?*
*RUBUTAWA:-*
*JAMILA LAWAL ZANGO*
*SADAUKARWA GA:-*
*SUMMY M NA'IGE*
_(Aminiya)_
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO....*
*SHAFI NA TARA*