Sashe 27
Halimatu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Babu abin da yake tashi a cikin gidan sai koke koke,da gudu su rahinatu suka ƙaraso ita da Hanne sakamakon mugun labarin da suka ji.wani irin kuka mai tsuma zuciya da ruhi suka saki lokacin da suka ga halin da su inna laure suke ciki,kuka suke yi babu mai rarrashin wani,musamman ma rahine da abin ya haɗe mata biyu mahaifiyar ta da kuma mijin ta.
INNA LAURE suman ta uku,da an yayyafa mata ruwa ta farfaɗo zafin ciwo sai ya sake sumar da ita,shi kuwa baban kamilu suman shi ɗaya, tun da ya farfaɗo bai ƙara sume wa ba,sai dai kuma numfarfashin da yake na wahala sabo da zafin ciwo.ɗago da kansa yayi ya dubi rahane da ta tsura masa idanu babu ko ƙiftawa,suna haɗa idanu ya fashe da wani kuka mai ban tausayi,kana jin kukan kasan daga cikin zuciyar shi yake fitowa.
Sai da yayi mai isar sa sannan ya buɗe baki cikin azabar ciwo da raɗaɗi yace "rahane kinga abin da ya same ni ko?? Ashe dama tsau-tsayi ne yake kira na!! banji ba ban gani ba an cutar da ni! Wallahi da nason haka ce zata faru da duk abin da za'ayi bazan zo kawo kuɗin nan ba,yanzu ga shi nan gurin taimako sun nakasa min rayuwa ta.ya ƙarasa maganar yana mai fashewa da sabon kuka.
Kuka take yi sosai harda sheshsheƙa ba ƙaramin tausayi ya bata ba,musamman yadda taga ƙafar tashi har ta fara kumbura,cikin kuka tace"kayi haƙuri baban kamilu,ƙaddara ta riga fata,dama Allah ya ƙaddara hakan zai faru daku" ta ƙarasa maganar tare share hawayen da ya zubo akan kuncin ta.
Sallamar HARUNA mijin altine ce ta katse su daga zancen da suke yi, shigowa yayi tare da wani tsohon mutum hannun sa ɗauke da wata jakar fata, tsuguna wa tsohon yayi a gaban babban kamilu ya ajiye jakar da take ruƙe a hannun shi.duban baban kamilu yayi sannan yace masa "sannu! bari na ɗan duba maka ƙafar taka!!". Yana gama faɗin haka bai jirawo cewar baban kamilu ba ya damƙi ƙafar da hannayen shi guda biyu ya tattaɓa tare da lallatsawa.
Wani irin ihu mai firgitarwa haɗe da wani gawur taccen gurnani baban kamilu ya saki,babu shiri baba lado ya sakar masa ƙafar sa,duban sa ya kai gun mijin altine yace masa "a gaskiya Haruna sai an samu waɗan da zasu iya ruƙe min baban kamilu,idan ba haka ba kuwa ba zai taɓa bari a gyara ƙafar nan ba,kuma kaga karayar guda uku ce! Sannan ga yanka!! Idan kuma aka ƙyale shi ƙafar zata iya samun gagarumar matsala!!".
Jin furucin da baba lado yayi ne yasa baban kamilu ƙara fashewa da wani sabon kuka mai tsuma zuciya,babu abinda yake yi sai surutai.miƙewa HARUNA mijin altine yayi tare da kallon jerin mutanan da suke gurin yace "dan Allah ku taimaka mana a samu waɗan da zasu taya ni ruƙe bawan Allah n nan!!"ya faɗa yana duban baban kamilu.
Mutum biyu ne suka fito majiya ƙarfi suka haɗu su uku harda HARUNA suka yiwa baban kamilu ruƙo bana wasa ba.ba tare da ɓata lokaci ba baba lado ya damƙi ƙafar baban kamilu ya fara gyarawa,wani uban ihu ya saki wanda yafi na farko tare da zazzare idanu kamar zasu fito waje Sabo da azabar zafi.
Nan take ya saki kashi da fitsari a lokaci guda, runtse ido baba lado yayi ya murza ƙafar da kyau ji kake ƙaƙaƙas sakamakon komar da ƙashin yayi mazaunin sa,hakanne ya sa baban kamilu ya ƙara kurma wata razananniyar ƙara da tayi sanadiyar farfaɗowar Inna laure daga suman da tayi shi kuma ya sume,har aka gama gyaran bai san inda kansa yake ba.
Umarni baba lado ya bawa rahine akan tazo ta gyarawa baban kamilu jiki,"to"tace! Tare da miƙewa ta yafa mayafinta ta fita domin zuwa ɗakkowa baban kamilu wasu kayan idan ta gyara masa jikin shi ta canja mashi su.
Tashi baba lado ya yi ya ƙara so gurin da inna laure take kwan ce magashiyyan,altine da hanne ne suka ƙara so wajen tare da marka maƙociyar su.duban ƙafar baba lado yayi yaga ta kubura sosai,ɗagowa yayi yace su ruƙe masa Inna laure da kyau sabo da baya so a samu matsala.
Share hawayen da suka sakko akan kuncin ta tayi tare da cewa "to". bismillah malam lado yayi tare da sa hannu ya cafki ƙafar inna laure,nan take tayi wata iriyar zabura ta ƙwace kanta daga ruƙon da suka yi mata abin ka da mai jiki gaba ɗaya ta watsar dasu gefe tana wata iriyar girgiza,gaba ɗaya ilahirin jikin ta rawa yake yi sakamakon azabar da ƙafar take mata.
Ganin haka ne baba lado ya umarci HARUNA mijin altine da mazan nan da suka ruƙe baban kamilu da suzo su ruƙe masa Inna laure,ba tare da ɓata lokaci ba suka ruƙeta tare da danne ta baba lado ya ci-gaba da aikin sa.wani irin firgitaccen ihu inna laure ta kurma tare da saka hannu ta fizge ɗankwalin da yake ɗaure a kanta ta fara fizgar gashin kanta sabo da azaba.
Babu Abin da kake ji yana tashi a cikin gidan sai ihun inna laure da koke koken su Hanne.gaba ɗaya inna laure ta gama jigata,hawaye da majina duk sun ɓata fuskar nan tata,fitsari kuwa tayi shi ya kai sau biyar sabo da a zaba,a haka malam lado ya gama gyaran ƙafar tata.shi kanshi ba ƙaramar wahala ya sha ba, Sabo da karaya uku ta samu da tsagewar ƙashi,shi yasa ya wahala wajen dai dai ta ƙasusuwan nata.
Bayan an gama ne altine ta gyarawa inna laure jikin ta,ita kuma HANNE ta gyara gurin da aka kwantar da ita, HARUNA mijin altine ya umarci altinen da HANNE su zauna a wajen inna laure domin su kula da ita,idan yaso yaran sai su zauna a wajen mahaifiyarsa.shi kuma baban kamilu tuni rahine ta gyara masa jikin sa,yayin da ƙannen sa guda uku suka zo suka cicciɓe shi suka tafi dashi gida,dole rahine tabi bayan su domin kula da mijin ta .
"HALIMATU"
A ɓangaren su HALIMATU kuwa, tun da ta kwanta bata farka daga bacci ba sai a suba,gabatar da sallah tayi tare da yin azkar sannan ta ɗauki ƙur'ani ta fara karatu cikin daddaɗar muryar ta.bayan ta gama karatun ne ta ajiye ƙur'anin tare da nunke hijab ɗin da tayi sallar da sallaya ta ajiye akan side drawer.zama tayi a ƙasa tare da jawo Ledodin da MUKHTAR ya kawo mata, buɗewa ta fara yi domin ta ƙagu ta ga abin da yake cikin su.
Ledar farko wasu irin manya manyan biscuits ne masu tsadar gaske kala kala shaƙe da ledar,mayar dasu tayi gefe tare da jawo ɗayar ledar ta buɗe, chocolate ne manya manya masu tsada kala kala shaƙe a cikin ledar,sai kuma ledar ƙarshe wadda tafi kowacce girma, ƙunshe take da tarkacen alawoyi,chewngum,kalolin yoghurt da kuma lemuka.
Samun kanta tayi cikin matsanan cin farin ciki da annashuwa,ajiye kayan tayi tare da sakkowa down stairs.bata iske kowa a parlon ba, direct kitchen ta nufa domin ɗora break fast. tsaya wa tayi tana tunani abinda ya kamata ta ta ɗora,ƙwai ta ɗebo guda ashirin ta wanke tare da zubawa a tukunya, fridge ta buɗe ta ɗakko ɗanyar hanta ta yanka ta ƙana tare da wanke ta tas ,tukunya ta ɗakko ta zuba hantar da ƙwan sannan ta yanka albasa da tafarnuwa da citta da seasoning,ta kunna gas ta ɗora akai.wake ta ɗebo ta gyara ta wanke shi tsaf, sannan ta sanya shi a cikin blender taɗan bubburga shi kaɗan yanda zai surfu,sannan ta juyeshi ta wanke shi tsaf ta ajiye a gefe.
Fridge ta buɗe ta ɗebo tattasai da attaruhu ta gyara,sannan ta ɗebo albasa a store itama ta gyara ta haɗe su waje ɗaya,blender ta ɗakko babba ta zuba waken da ta gyara tare da attaruhu da tattasai da albasa,tafarnuwa da citta da black papper ta ɗan zuba akai,sannan ta ɗakko seasoning da mix spices ta zuba akai tare da zuba mai da ɗan manja.
Bayan ta gama haɗa komai tayi blending ɗin su gaba ɗaya,sai da ta tabbatar sun yi laushi sannan ta juye a cikin wani babban bowl,ƙwan ta tsame ta zuba a cikin ruwan sanyi ta ɓare su,ita kuma hantar ta juye ta a cikin ƙullun alalar,leda ta ɗakko ta fara zuba ƙullin alalar ta a ciki,duk ledar da ta zuba ƙullin sai ta jefa ƙwai guda ɗaya a ciki,haka tayi tayi har ta gama ƙullawa gaba ɗaya.
Steammer ta ɗakko ta zuba ruwa a ƙasan ta, sannan ta rufe tare da jera alalar a ciki ta rufe ta ɗora akan wuta tare da rage wutan a medium low flame.markaɗaɗɗiyar gyaɗa ta ɗakko a cikin bucket ta ɗiba a cikin bowl,ruwa ta zuba ta dama gyaɗar sosai sannan ta tace ta zuba a cikin tukunya.kus kus ta ɗebo ɗan kaɗan ta watsa a ciki sannan ta ɗebo kamu a cikin fridge ta zuba ruwa kaɗan ta dama a cikin cup ta ajiye a gefe sannan ta ɗebo suger kaɗan ta zuba a ciki.
Tafasa kunun ya fara yi,sai da ta ga gafin gyaɗar ya ɗan rage sannan ta sauke a ƙasa,ƙullin ta ɗakko taɗan zuba kaɗan ta saka abin juyawa ta juya sosai,sai da taga kaurin yayi mata yan da take so sannan ta ɗakko ruwan lemin juice ta zuba kaɗan a ciki tare da juya wa.madarar gari ta ɗakko ta ɗibi three cup ta dama da ruwan sanyi sannan ta zuba a cikin kunun ta motsa shi sosai,sannan ta ƙara ɗakko condence milk itama ta zuba three cup a ciki ta sake motsawa.
Kyakkyawan flacks babba ta ɗakko ta zuba a ciki,sannan ta zubawa su inna laure da su baba mai gadi nasu.zuwa tayi ta buɗe alalar ta taga ta nuna tayi kyau sosai Sai tashin ƙamshi take yi,ba tare da ɓata lokaci ba ta sauke tare da ɗakko haɗaɗɗun food wamers ta zuba a ciki.cikin sauri ta haɗa haɗaɗɗiyar source ɗin ƙoda mai ɗan karan daɗi,gaba ɗaya gidan ya bure da ƙamshin girkin HALIMATU.
Tana gamawa ta gyara kitchen ɗin tsaf tamkar ba'ayi girki a cikinsa ba,sannan ta kwaso kayan ta jere su a kan dining table. up stairs ta haye zuwa ɗakin ta domin ta yi wanka ta shirya, sabo da yau zata fara zuwa makarantar islamiyya ƙarfe takwas.
INNA LAURE suman ta uku,da an yayyafa mata ruwa ta farfaɗo zafin ciwo sai ya sake sumar da ita,shi kuwa baban kamilu suman shi ɗaya, tun da ya farfaɗo bai ƙara sume wa ba,sai dai kuma numfarfashin da yake na wahala sabo da zafin ciwo.ɗago da kansa yayi ya dubi rahane da ta tsura masa idanu babu ko ƙiftawa,suna haɗa idanu ya fashe da wani kuka mai ban tausayi,kana jin kukan kasan daga cikin zuciyar shi yake fitowa.
Sai da yayi mai isar sa sannan ya buɗe baki cikin azabar ciwo da raɗaɗi yace "rahane kinga abin da ya same ni ko?? Ashe dama tsau-tsayi ne yake kira na!! banji ba ban gani ba an cutar da ni! Wallahi da nason haka ce zata faru da duk abin da za'ayi bazan zo kawo kuɗin nan ba,yanzu ga shi nan gurin taimako sun nakasa min rayuwa ta.ya ƙarasa maganar yana mai fashewa da sabon kuka.
Kuka take yi sosai harda sheshsheƙa ba ƙaramin tausayi ya bata ba,musamman yadda taga ƙafar tashi har ta fara kumbura,cikin kuka tace"kayi haƙuri baban kamilu,ƙaddara ta riga fata,dama Allah ya ƙaddara hakan zai faru daku" ta ƙarasa maganar tare share hawayen da ya zubo akan kuncin ta.
Sallamar HARUNA mijin altine ce ta katse su daga zancen da suke yi, shigowa yayi tare da wani tsohon mutum hannun sa ɗauke da wata jakar fata, tsuguna wa tsohon yayi a gaban babban kamilu ya ajiye jakar da take ruƙe a hannun shi.duban baban kamilu yayi sannan yace masa "sannu! bari na ɗan duba maka ƙafar taka!!". Yana gama faɗin haka bai jirawo cewar baban kamilu ba ya damƙi ƙafar da hannayen shi guda biyu ya tattaɓa tare da lallatsawa.
Wani irin ihu mai firgitarwa haɗe da wani gawur taccen gurnani baban kamilu ya saki,babu shiri baba lado ya sakar masa ƙafar sa,duban sa ya kai gun mijin altine yace masa "a gaskiya Haruna sai an samu waɗan da zasu iya ruƙe min baban kamilu,idan ba haka ba kuwa ba zai taɓa bari a gyara ƙafar nan ba,kuma kaga karayar guda uku ce! Sannan ga yanka!! Idan kuma aka ƙyale shi ƙafar zata iya samun gagarumar matsala!!".
Jin furucin da baba lado yayi ne yasa baban kamilu ƙara fashewa da wani sabon kuka mai tsuma zuciya,babu abinda yake yi sai surutai.miƙewa HARUNA mijin altine yayi tare da kallon jerin mutanan da suke gurin yace "dan Allah ku taimaka mana a samu waɗan da zasu taya ni ruƙe bawan Allah n nan!!"ya faɗa yana duban baban kamilu.
Mutum biyu ne suka fito majiya ƙarfi suka haɗu su uku harda HARUNA suka yiwa baban kamilu ruƙo bana wasa ba.ba tare da ɓata lokaci ba baba lado ya damƙi ƙafar baban kamilu ya fara gyarawa,wani uban ihu ya saki wanda yafi na farko tare da zazzare idanu kamar zasu fito waje Sabo da azabar zafi.
Nan take ya saki kashi da fitsari a lokaci guda, runtse ido baba lado yayi ya murza ƙafar da kyau ji kake ƙaƙaƙas sakamakon komar da ƙashin yayi mazaunin sa,hakanne ya sa baban kamilu ya ƙara kurma wata razananniyar ƙara da tayi sanadiyar farfaɗowar Inna laure daga suman da tayi shi kuma ya sume,har aka gama gyaran bai san inda kansa yake ba.
Umarni baba lado ya bawa rahine akan tazo ta gyarawa baban kamilu jiki,"to"tace! Tare da miƙewa ta yafa mayafinta ta fita domin zuwa ɗakkowa baban kamilu wasu kayan idan ta gyara masa jikin shi ta canja mashi su.
Tashi baba lado ya yi ya ƙara so gurin da inna laure take kwan ce magashiyyan,altine da hanne ne suka ƙara so wajen tare da marka maƙociyar su.duban ƙafar baba lado yayi yaga ta kubura sosai,ɗagowa yayi yace su ruƙe masa Inna laure da kyau sabo da baya so a samu matsala.
Share hawayen da suka sakko akan kuncin ta tayi tare da cewa "to". bismillah malam lado yayi tare da sa hannu ya cafki ƙafar inna laure,nan take tayi wata iriyar zabura ta ƙwace kanta daga ruƙon da suka yi mata abin ka da mai jiki gaba ɗaya ta watsar dasu gefe tana wata iriyar girgiza,gaba ɗaya ilahirin jikin ta rawa yake yi sakamakon azabar da ƙafar take mata.
Ganin haka ne baba lado ya umarci HARUNA mijin altine da mazan nan da suka ruƙe baban kamilu da suzo su ruƙe masa Inna laure,ba tare da ɓata lokaci ba suka ruƙeta tare da danne ta baba lado ya ci-gaba da aikin sa.wani irin firgitaccen ihu inna laure ta kurma tare da saka hannu ta fizge ɗankwalin da yake ɗaure a kanta ta fara fizgar gashin kanta sabo da azaba.
Babu Abin da kake ji yana tashi a cikin gidan sai ihun inna laure da koke koken su Hanne.gaba ɗaya inna laure ta gama jigata,hawaye da majina duk sun ɓata fuskar nan tata,fitsari kuwa tayi shi ya kai sau biyar sabo da a zaba,a haka malam lado ya gama gyaran ƙafar tata.shi kanshi ba ƙaramar wahala ya sha ba, Sabo da karaya uku ta samu da tsagewar ƙashi,shi yasa ya wahala wajen dai dai ta ƙasusuwan nata.
Bayan an gama ne altine ta gyarawa inna laure jikin ta,ita kuma HANNE ta gyara gurin da aka kwantar da ita, HARUNA mijin altine ya umarci altinen da HANNE su zauna a wajen inna laure domin su kula da ita,idan yaso yaran sai su zauna a wajen mahaifiyarsa.shi kuma baban kamilu tuni rahine ta gyara masa jikin sa,yayin da ƙannen sa guda uku suka zo suka cicciɓe shi suka tafi dashi gida,dole rahine tabi bayan su domin kula da mijin ta .
"HALIMATU"
A ɓangaren su HALIMATU kuwa, tun da ta kwanta bata farka daga bacci ba sai a suba,gabatar da sallah tayi tare da yin azkar sannan ta ɗauki ƙur'ani ta fara karatu cikin daddaɗar muryar ta.bayan ta gama karatun ne ta ajiye ƙur'anin tare da nunke hijab ɗin da tayi sallar da sallaya ta ajiye akan side drawer.zama tayi a ƙasa tare da jawo Ledodin da MUKHTAR ya kawo mata, buɗewa ta fara yi domin ta ƙagu ta ga abin da yake cikin su.
Ledar farko wasu irin manya manyan biscuits ne masu tsadar gaske kala kala shaƙe da ledar,mayar dasu tayi gefe tare da jawo ɗayar ledar ta buɗe, chocolate ne manya manya masu tsada kala kala shaƙe a cikin ledar,sai kuma ledar ƙarshe wadda tafi kowacce girma, ƙunshe take da tarkacen alawoyi,chewngum,kalolin yoghurt da kuma lemuka.
Samun kanta tayi cikin matsanan cin farin ciki da annashuwa,ajiye kayan tayi tare da sakkowa down stairs.bata iske kowa a parlon ba, direct kitchen ta nufa domin ɗora break fast. tsaya wa tayi tana tunani abinda ya kamata ta ta ɗora,ƙwai ta ɗebo guda ashirin ta wanke tare da zubawa a tukunya, fridge ta buɗe ta ɗakko ɗanyar hanta ta yanka ta ƙana tare da wanke ta tas ,tukunya ta ɗakko ta zuba hantar da ƙwan sannan ta yanka albasa da tafarnuwa da citta da seasoning,ta kunna gas ta ɗora akai.wake ta ɗebo ta gyara ta wanke shi tsaf, sannan ta sanya shi a cikin blender taɗan bubburga shi kaɗan yanda zai surfu,sannan ta juyeshi ta wanke shi tsaf ta ajiye a gefe.
Fridge ta buɗe ta ɗebo tattasai da attaruhu ta gyara,sannan ta ɗebo albasa a store itama ta gyara ta haɗe su waje ɗaya,blender ta ɗakko babba ta zuba waken da ta gyara tare da attaruhu da tattasai da albasa,tafarnuwa da citta da black papper ta ɗan zuba akai,sannan ta ɗakko seasoning da mix spices ta zuba akai tare da zuba mai da ɗan manja.
Bayan ta gama haɗa komai tayi blending ɗin su gaba ɗaya,sai da ta tabbatar sun yi laushi sannan ta juye a cikin wani babban bowl,ƙwan ta tsame ta zuba a cikin ruwan sanyi ta ɓare su,ita kuma hantar ta juye ta a cikin ƙullun alalar,leda ta ɗakko ta fara zuba ƙullin alalar ta a ciki,duk ledar da ta zuba ƙullin sai ta jefa ƙwai guda ɗaya a ciki,haka tayi tayi har ta gama ƙullawa gaba ɗaya.
Steammer ta ɗakko ta zuba ruwa a ƙasan ta, sannan ta rufe tare da jera alalar a ciki ta rufe ta ɗora akan wuta tare da rage wutan a medium low flame.markaɗaɗɗiyar gyaɗa ta ɗakko a cikin bucket ta ɗiba a cikin bowl,ruwa ta zuba ta dama gyaɗar sosai sannan ta tace ta zuba a cikin tukunya.kus kus ta ɗebo ɗan kaɗan ta watsa a ciki sannan ta ɗebo kamu a cikin fridge ta zuba ruwa kaɗan ta dama a cikin cup ta ajiye a gefe sannan ta ɗebo suger kaɗan ta zuba a ciki.
Tafasa kunun ya fara yi,sai da ta ga gafin gyaɗar ya ɗan rage sannan ta sauke a ƙasa,ƙullin ta ɗakko taɗan zuba kaɗan ta saka abin juyawa ta juya sosai,sai da taga kaurin yayi mata yan da take so sannan ta ɗakko ruwan lemin juice ta zuba kaɗan a ciki tare da juya wa.madarar gari ta ɗakko ta ɗibi three cup ta dama da ruwan sanyi sannan ta zuba a cikin kunun ta motsa shi sosai,sannan ta ƙara ɗakko condence milk itama ta zuba three cup a ciki ta sake motsawa.
Kyakkyawan flacks babba ta ɗakko ta zuba a ciki,sannan ta zubawa su inna laure da su baba mai gadi nasu.zuwa tayi ta buɗe alalar ta taga ta nuna tayi kyau sosai Sai tashin ƙamshi take yi,ba tare da ɓata lokaci ba ta sauke tare da ɗakko haɗaɗɗun food wamers ta zuba a ciki.cikin sauri ta haɗa haɗaɗɗiyar source ɗin ƙoda mai ɗan karan daɗi,gaba ɗaya gidan ya bure da ƙamshin girkin HALIMATU.
Tana gamawa ta gyara kitchen ɗin tsaf tamkar ba'ayi girki a cikinsa ba,sannan ta kwaso kayan ta jere su a kan dining table. up stairs ta haye zuwa ɗakin ta domin ta yi wanka ta shirya, sabo da yau zata fara zuwa makarantar islamiyya ƙarfe takwas.