← Book details Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 65 OF 84

Sashe 65

Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

daidai wani katafaren shagon aski asma'u tayi parking zaro ido khadeeja tayi tana kallon wurin tace ammah menake gani haka....badai aski za'amun ba

Dariya asma'u tayi batace komai ba tafito daga moyar sannan tazagaya tafito da khadeeja suka shiga cikin shagon
Wurin wani dan matashi suka nufa dayake ma wani mutun gyaran fuska yana ganinsu ya hau washe baki yana fadin a'ah hajiya yaukece dakanki to bismillah mushiga ciki .....yafada yana nufar wani dan karamin office dake cikin shagon suna binsa abaya cikin rada khadeeja tace ammah wannan ba yaron nan bane dayake muku aiki

"eh shine kinsan na sallamesu daga gida to yanzu anan yake aiki

Bayan sun zauna yakamusu ruwa sannan asma'u tanuna mai khadeeja tana fadin nura nasan ka kware sosai aharkar aski dan allah wannan yarinyar nakeso kadan canza mata kamanni zuwa namiji ....zaka iya

Shiru yayi yana kape khadeeja da ido yace eh....to zan gwada dai amma canza wannan kyekkyewar zuwa gardin namiji its not easy gaskiya

Dariya asma'u tayi tamike tana ijiye mashi kudi masu yawa tace nasan zaka iya ....gawannan kasayi duk abunda zaku bukata ...and please kayi sauri zanje indawo yanzu

Ba'adau lokaciba asma'u tadawo tana sanye da bakar abaya tasha nikaf idonta ne kawai awaje sedai dataga khadeeja seda bakaramin mamaki tayiba ganin yanda tacanza guda tadawo wani dan karamin handsome guy irin masu karamin jiki dinnan

Shiga ce irin tahadaddun samari akamata Jan takalmine iron namaza akafanta se bakin riga da bakin wando tasha stoking se jacket maidan kauri da aka doro mata akai itama kalar ja dabaki saboda aboye gashin kan akadoro mata irin hularnan hana sallah fuskan kuma tasha fake saje da gashin baki sedan gyaran fuska da akamata wanda shiyakara canzata zuwa sak namiji

Sosai asma'u tayaba da aikin nura har saida takara mishi wasu kudin akai cike dafarin ciki ya karba yana mata godiya se tsokanar khadeeja yake ita kwa tadake kamar dagaske har wani canza taku take adole dan saurayi

Suna fitowa khadeeja ta tsaya cak tana kallon wasu yan mata dake tsaye daga gefe da alama wani suke jira

Murmushi tayi tana kallonsu tace ammah kinga wasu kyewawan yan mata kuwa

Dariya asma'u tayi tace allah yaga abunda yagani yayiki mace da munshiga uku

Inda suke tanufa tana fadin dan jirani bari muyi gwaji muga dagaske nacanza

tafiya take cikin takunta sak iron namaza tundaga nesa suka kureta da ido dayar tace wow kinga wani hadadden guy kuwa ....da alama wurin mu zaizo

dayar zatayi magana kenan khadeeja ta iso wurinsu cikin sassanyar murya tace sannunku kyewawa

Fari da ido sukayi cike dafarinciki dayar tace sannunka kaima

Murmushi tayi tana kafesu da ido tace am...dan allah kozaki ban aron kawarki na minti biyu inaso zan danyi magana da ita
Ok ...tafada tana shigewa shagon dake kusa dasu

Kauda kai yarinyar tayi tana hura hanci ita adole zataja ajinta

dariya ce takusa kwacema khadeeja tayi saurin danneta tana fadin agaskiya tunda uwata ta haifeni zan iya cewa bantaba ganin kyekkyewa irinki ba ....shiyasa tunda nadora idona akanki naji bazan iya sake wannan damar ta kubucemun ba

Murmushi tayi cike dafarin ciki tace allah koh ?

"Sosaima ....khadeeja tafada tana tura hannayenta aljihu

daga cikin mota asma'u tadanno mata horn juyawa tayi takalleta sannan takalli yarinyar tana mikamata waya tace kinga inatare da friend dina ne kar inbata masa lokaci ga wannan kisamun numbanki

Karban wayar tayi tana wani fari da ido khadeeja kwa banda murmushi ba abunda take tana karban wayar ta tura aljihu tana fadin bari inje se munyi waya

Hartajuya yarinyar tace baka fadamun sunanka ba murmushi tayi batare datajuyo ba tace kamal ....

dakallo yarinyar tabita har tashige motar sannan tajuya cike dafarin ciki tashige shagon dakawarta tashiga dazu

khadeeja nashiga mota tace ammah yazaki katsemun jin dadina

Dariya asma'u tayi batace komai ba tatada motar suka tafi

Suna isowa hotel din khadeeja takira sarah tace tana hanya zatazo yanzu sunfito daga mota kenan sukaga motar ahmad awurin cike da mamaki khadeeja tace wannan ba motar Tarzan bace mekuma yake anan

cikin hotel din asma'u tanufa tana fadin ba ahmad kadai yakeda irin wannan motar ba ai

Bin bayanta khadeeja tayi tana kara gyara zaman wandonta tace ammah nifa gaskiya belt dinnan ta isheni duk tadauremun kwankwaso

ahawa nasama restaurant din yake danhaka se sunhau lifter suna shiga asma'u zata danna Kenan su AK suka shigo zaro ido sukayi suna kallonsu sannan khadeeja takalli asma'u tana langabe kai kamar zatayi kuka alama asma'u tamata akan tanatsu karsugane su

kallon ahmad AK yayi yana fadin friend inaji ajikina kamar lady boss nakusa dani

zaro ido asma'u tayi tana kauda kai gefe

Dariya ahmad ahmad yayi yace har wani yanayi ma kakeji idan tana kusa dakai kenan

Jinginar dakansa yayi yana lumshe ido yace whenever she is around..... My heart start beating faster ......my hands start shaking ....I feel like I have everting in the world.... Rungume hannayensa yayi akirji yaci gaba dafadin se inji tamkar inrungumeta ajikina har tsawon rayuwata

Dariya ce takwacema khadeeja tayi saurin gintseta tana kauda kai hade da daure fuska tamkar ba ita tayita ba

Kallonta sukayi da mamaki AK yace kai wakakema dariya

Juyowa tayi tana kallonsa tace da Wanda ya tsargu ....ko dokane ba'a dariya a lifter

Dariya ahmad yayi yace kai dabakinka wazai hanaka dariya ...

Kokarin leko fuskan asma'u AK yake danshi dagaske yake yanaji ajikinsa tana kusa dashi
saurin shiga gabansa khadeeja tayi tana kare asma'u tace ahh ....malam lafiya ya kake Abu kamar ba nagartaccen namiji ba tunda muka shigo ka kure baiwar allah da ido .. haka ake

daur fuska AK yayi yace kaikuma awa? zaka hayayyako mun ....

mijinta ne ni.......

Dariya AK yayi yana kallon ahmad yace kaji fa....wai mijinta ne ....wannan shi ake kira hadin gambiza mijin wizi matar ustaziyya ....

daure fuska khadeeja tayi tana kallon ahmad dayakafeta da ido tace kaikuma lafiya saurin kauda kai yayi yana fadin kalau....

Kureta da ido AK yayi yana fadin ni senaga ma kamar nataba ganinka kuma Kanamun kama da......

Katsesa tayi dafadin.....anzo wurin yanzu zakace nayi kama da matarka

dariya AK yayi yana tafa hannu yace yawwa ....se yanzu natuna dakanwata kake kama exactly..... ahmad bakaga tayi kama da khadeeja ba daza'a cire wannan gashin bakin Sak deeja zatafito anan wajan

daure fuska tayi tana kauda kai tace Ahab ai kuma sekayi .....

shiru yayi baice komai ba har suka fito kowa yayi hanyarsa har lokacin AK nakokarin ganin fuskar asma'u amma khadeeja tahanasa

Suna zaunawa su AK sukazo a table din kusa dasu suka zauna

Daure fuska khadeeja tayi tana kallon asma'u tace ammah miye abunyi
Tashi asma'u tayi tabar wurin tana fadin zo muje waje bin bayanta khadeeja tayi tana maka musu harara

Suna fita ahmad yabi bayansu dasauri kafin su shiga mota yasha gabansu

Dafe kai khadeeja tayi tace ohhh ni kamal....wai kukan memuka tsaremaku ne
daure fuska yayi yafizge gashin bakinta yana fadin dallah yimun shiru kina tunanin bazan ganeki bane .....deeja mekuke shirin aikatawa ne dama duk abunda asma'u ta aikata da had in bakinki tayi ....kinbani mamaki
Shiga tsakaninsu asma'u tayi tana fadin a'ah ahamad karkace haka zanma bayanin komai ..................nan tabashi labarin duk abunda yafaru tun zuwanta company har zuwa yau dazasu saye Zane ahannun sarah

Cike damamki yace dama sarah ce tasaci zanen to amma meyasa baki gayamun ba bakya bukatar taimako nane konima baki yarda dani bane

"bahaka bane itama khady seyau tasan dazancan mun riga mungama tsara komai gashi zaku bata mana shirinmu idan sarah tazo taga AK awurin bazata sayar dazanen ba

Murmushi yayi cike dafarin ciki yace karkidamu wannan ba matsala bane bari zansan yanda zanyi injanyeshi daganan dama ni nace muzo

Kallon khadeeja yayi yana dariya yace kamal ....
Kauda kai tayi tana daure fuska ita adole fushi take anfizge mata gashin baki

barin wurin yayi yana fadin bari inje karta iskomu juyowa khadeeja tayi tana fadin malam sekamaidamun gashin bakina

Dawowa yayi yamaidamata gashin bakin yana dariya Yace dan allah kidaina kallona haka wallahi senaji wani banbarakwai .....bige hannunsa tayi tana kallon kanta a glass din motar tadaidaita gashin bakinta shikuma yawuce ciki suna binsa abaya

Yana zuwa AK yahaushi damasifa wai yabarshi shikadai azaune kallon wurin yana yamutsa fuska yace friend bakajin wani wari yana tashi anan wajan

shinshina wurin AK yafarayi har kan table din su asma'u yana fadin nidai banji wani wariba gaskiya

"Nikuma gaskiya inajin wari katashi kawai mubar wurin nan

gyara zama AK yayi yace ba inda zanje inace kai kamatsa muzo nan shine kuma yanzu zakace mutafi bayan munyi odan abinci ....idan kai kanada kudi ni bandashi ehhe....

langabe kai ahmad yayi yana kallon khadeeja yamata alama tayi wani abu akai AK yaki tafiya

Lemu tadauka takoma kujerar dake kusan ta AK tafara shan lemun seta wurga bawan table dinsu AK

Cike datakaici AK yace kai wai lafiya kaga nan yamaka kama da dustbin ne ko akan bola kaganmu zaune

daure fuska tayi tace ...kuma ba dakinka baneba ba ....kudi nabiya dan haka inada damar yin abunda naga dama ....tunda bakai zaka share ba sekayi shuru ....idan kaga kaga bazaka iyaba se kabar nan

Kallonsa ahmad yayi yana kunshe dariyarsa yace friend kaga irinta ai katashi mutafi this place was so disgusting

bude abincinsa yayi yana fadin ba inda zanje ....yakara wurgomun wani abun yagani ....dawani karamin jikinsa awurin

zaikai lomar farko khadeeja tajanyo tissue ta fara fyace majina runtse ido yayi yana yamutsa fuska yace ohhh gosh wai wannan wane irin mutum ne

tashi ahmad yayi yana dariya yaja hannunsa suka bar wajan khadeeja tabisu da dariyar keta

[24/07, 05:50] Hassan Atk: 📚📚📚📚📚📚
👨‍👧 _DOMUN KANWATA_ 👩‍👧

1⃣9⃣0⃣

Suna fita sarah tashigo restaurant din khadeeja naganinta tagyara zama tana fadin now the game will begin ...

Tana isowa wurinsu khadeeja tamike tsaye tana murmushi tace barka dazuwa hajiya sarah gaskiya kin jamana aji dayawa tundazu muke jiranki anan

Murmushi tayi tana kallon asma'u dake zaune cikin nikaf tace ...kayi hakuri yanayin hanyar ne da cinkoso ....amma tare kuke ne

"Oh sorry bamugabar miki dakanmu ba ....nidai sunana kamal Ahmad wannan kuma abokiyar aikina ce sunanta .....sunanta salamatu Nuhu

Murmushi sarah tayi tana sake kallon asma'u tace ok....sannu salamatu

Yawwa sannu .....asma'u tafada ciki ciki dan kar sarah tagane muryanta
Chapter 65 · 0% Book details