← Book details Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 84

Sashe 24

Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kin manta kintaba gayamun cewa inada hali mai kyew zaki tayani da addu'a Allah yabani miji nagari ba kya tunanin addu'ar ce Allah yakarba

Da kyar asma'u ta lallashi khadeeja tayi shiru sannan ta roketa akan kar tagayama kowa halin datake ciki ahmad tabari dakanta zata mai bayani

bayanin datama khadeeja shitama ahmad amma da kyar ta shayo kansa ya hakura da zacan da cewa yayi se yaje yasanar da grany halin da ake ciki

Bayan angama taro kowa ya watse tun aranar yane uwansu suka koma

Ahmad ne yamaida Momy dasu khadeeja gida

Gidan yayi shuru har antattare angyara yakoma yanda yake da
Kowa na bangarensa

asma'u har ta kuanta taji anturo kofa afirgice ta tashi zaune ta kure kofar da ido 😳
[18/07, 15:04] Hubbey Frd Ameena Kn: AK ne yashigo yana cire coat dinsa

Ganin yanufo gadon yasa tayi saurin driwowa kasa tana zare ido

Ko kallonta bai yiba ya ijiye coat din akan gado sannan yakalleta yana fadin kewai kallon namiye
Ko kina tunanin zan kuana wuri daya dake ne idan kina bukata ta kibiyoni inda nake

Kauda kai tayi tana fadin ba'abunda zanyi dakai so zaka iya tafiya

Nasan kina so natafi dan kisamu daman zuwa wurin ahmad
Sannan yamatso kusa da ita yace

kina son ahmad ko?

Eh... Tafada atakaice

Girgiza kai yayi yace karya kike bazaki iya son kowa ba saboda kudi kawai kike so

Matsawa tayi daga gurin tana fadin kai kuma bawanda zai soka saboda kanada bad altitude

Dressing room dinsa yanufa yana fadin u will suffer nan gidan dakike kwadayin shiga seya zame maki prison saboda ba inda zakije

Dakallo tabishi tana fadin idan dai har zakayi nesa dani badamuwa

Juyowa yayi yana kallonta yace bakinki zai mutu ranarda nayi ball dake daga gidan nan ahmad ya auri sarah ni kuma na auri aysha

Sannan yadawo kusa da ita yace kina mamaki kinji nace aysha ko to itace budurwata

Tayarda na aureki ne dan tasan ko giyar wake nasha bazan fada sonki ba

Dariya tayi tace ta amince ne saboda batasan me ake cewa so ba datana sonka dabata yarda ka auri wata ba

Shiru yayi nadan lokaci kamar mai tunani can kuma yace tasan cewa kudi ne agabanki

Kauda kai tayi ahankali tafurta ni bansan meyasa mutane suke haukan kana birgesu ba bayan ni kuma inaji kadameni

Ahasale yace
be quite kar ki manta agidana kike kuma adakina sannan yajuya yanafadin so yakamata ki girmama ni

Itama ahasale tace kai kuma karka manta kana magana da matarka ne

Juyowa yayi da mamki yana kallonta sannan ahankali ya furta mata?? Mata fa kikace?? To idan ma bacci kike kifarka wannan matsayin yafi karfinki kuma bazaki taba samunshi ba
Nagaya miki this is just the beginning of ur suffering!!

Kauda kai tayi tana fadin I am already regretting it

Dariya yayi yace to ai baki maga komai ba tunda auren kawai kika gani senasa kin tsani kanki

Karasowa tayi gabanshi tana fadin wai ma meyasa katsaya kana magana dani kamata yayi ace kana wurin budurwanka yanzu ni kahanani bacci katafi kawai gobe kaacigaba da cimun fuska

nayarda nan din prison ne awurina all tnx to u

Fita yayi daga dakin yana fadin u are welcome

Dakallo tabishi sefa yafita sannan tadauke coat dinshi da ya ijiye akan gado tanufi dressing room tana mitar ta tsani taga kaya akn gado

Cikin sanda AK ya sawko dwonstairs yanufi hanyar fita yana Satan kallon bangaren grany
Har yakai kofa kamar daga sama yaji tace

Abidi ina zuwa cikin wannan Daren

Runtse ido yayi hade da cije lebe bai jiyowa ba kuma nai yi magana seda tace bada kai nakeba sannan ya juyo yana sadda kai irin na mara gaskiya
Ganin ba wasa afuskar grany yasa ya kalalo murmushi yana Sosa kai yace grany zan dan fita ne ahmad yan jirana

Daure fuska tayi tace ba inda zakaje wannan lokacin kamata yayi ace kana tare da matarka

Buga kafa yayi da kasa kaman zai fashe da kuka yace haba mana grany bafa dadewa zanyi ba

Amma bata saurareshiba ta tasa keyarshi seda taga yashiga bangarensa sannan ta juya tana masifa

Asma'u har tayi shirin kuanciya cikin doguwar rigan baccinta har kasa mai kyew

Taji anturo kofa
Atsorace ta juyo ganin AK atsaye yasa tayi saurin daukan gyelenta ta yafa tana fadin

Mekuma yadawo dakai...

Tsaki yayi ya kauda kai yana yace daban ysaya fada dake ba dayanzu nafita amma gashi kinja zan bata lokacina anan

Karasowa cikin daki Yayi yafara cire shirt dinsa

afirgice takauda kanta tana fadin wai mekake shirin yi

Kallon kin raina mun hankali yayi mata sannan yace kima daina acting kamar wata mutuniyar arziki bayan kinfi kowa sanin abunda nake shirin yi

Sake kauda kanta tayi tana facing mirror tace abunda kake baka kyewtawa

Karasowa yayi tabayanta yatsaya yana cire belt dinsa yace nan daki nane kuma ahaka nasaba kuanciya idan kinga bazaki iyaba zaki iya zuwa waje ki kuana

ai bai gama rufe baki ba tayi waje aguje sedai tana fita ta tsinkayo grany tafito daga dakin sarah

Saurin shan kuana tayi tadawo dakin tana rufe da idonta
AK yana daga kwance kan gado ya lullube da bargo yarufe ido kamar mai bacci Sam baiji shigowarta ba

Lalube tafara kan gadon tana Neman pilo by mistake ta taboshi
Afirgice ya tashi yana bige hannunta

Atsorace ta bude idonta tana Sosa inda ya bigeta

Tsaki yayi yace to ke koda kinada bukata haka akezuwa ba notice

Daure fuska tayi tadauki pilo tana fadin not interested

Kwace pilon hannunta yayi yace wannan pilo nane kinema wani

Dayan pilon tadauka hade da blanket takoma Palo kan 3sitter ta kuanta ta rufa da blanket din tana jin kewar Umma da khadeeja

har bacci yafara daukanta taji AK na atishshawa

Banza tayi dashi ta gyara kuanciyarta tana fadin alhakina kadai ma ya isheka

Jin abun yayi yawa yasa tamike tanufi dakin
Ahankali ta tura kofar tashiga

Tana shiga taji AK nafadin to wai meke damuna ne ..?

Remote din AC tadauka takashe sannan tanufi wurin kettle tadaura ruwa

Damamaki yake kallonta yana fadin malama lafiya zaki kashemun AC wayasaki

Banza tayi dashi seda ruwan yayi dumi sannan tazubo a cup ta kawomasa

Damamaki yace what are u doing

Kauda kai tayi tace kaina nakeyiwa saboda bazan iya yin bacci dawanan atishawar taka ba

Karban ruwan yayi yana fadin ai daga yau kindaina bacci mai dadi sannan yakai ruwan bakinsa

Da kyar yasha rabin Kofi ya mikamata sauran yana yamutsa fuska kin karba tayi tace idan bakasha dayawa ba bazaka warkeba

Ijiye kofin yayi akasa yana fadin bazaki kasheni da ruwan zafi ba

Daukan copin tayi tamaida tanufi hanyar tana fadin kuma kanemi kaya kasa kafin ka kunna AC

Da kallo yabita seda tafita sannan yaje yakarasa hanye ruwan dumin dayarage yasaka riga ya koma cikin bargo

Washegari dasafe......

Wayanshine keta ringing yana kwance yana bacci

Jiyayi andafashi yariko hannun yana fadin baby I am not feeling well wannan yarinyar taban ruwan dumi naji dadinsu amma...

Bai karasaba asma'u tamaka mai pilon dake hannunta
Afirgice yatashi yana kallonta da mamaki yace mekike anan

Dariya tayi tace mummunan mafarki kake ne

Daure fuska yayi yana fadin kece mummunan mafarkina

Wayarsa Tamika mai tana fadin dan Allah kadauki wayanka tadameni da kara

Fizge wayan yayi ahannunta yana duba mai kiran
Murmushi yakai wayan kunne yana fadin hi baby

Tashi asma'u tayi tanufi dressing room

Tadayan bangaren aysha cikin mryan shagwaba tace honey ina fata ba abunda yashiga tsakaninku

Dariya yayi yace haba wa kema kinsan nafi karfin haka so kawai ki kuantar da hankalinki I only belongs to u
Dariya tayi suka ci gaba da firarsu

Sarah ce da AK zaune abangaren grany suna breakfast

Can sarah tadago tace Yaya idan nasamu lokaci inaso zanyi tafiya

Dagowa yayi yakalleta yace ina kuma zakije awannan lokacin

Yaman ...nakeso naje akwai abunda zai kaini

Sanin acan tayi karatunta shiyasa bai yiwata gardama ya amince

Cike da farin ciki tace thank u Yaya amma kamun alkawarin bazaka kula wannan yarinyar ba

Lomar abinci yakai bakinsa yana fadin kar kidamu ba abunda zanyi da wannan mai fuskan yara ..

AK ne zaune ababban palon kasa yana kiran Nura dagudu Nura yakaraso yadurkusa yana fadin gani yallabai

Kaje wurin grany ka karbomun coffee

Washe baki nura yayi yace ai yanzu nafito daga can nabaro madam tana hada wa tace idan tagama zata kawo

Wace madam din ...
AK yafada cike da mamaki

Sadda kai nura yayi yana fadin madam dai amarya

Gyada kai AK yayi yana fadin takawo to ina jiranta

Asma'u na bangaren grany tafaketa tana koyamata yanda akema AK coffee dan tace yanzu yayi aure bazata iya wahalar hadamai kofee so uku arana ba

Kayan kanshi tadibo tazuba

Damamaki asma'u tace kayan kanshi a coffee kuma grany

Eh haka yake sonshi se kisa ido sosai ki kula

Bayan grany tagama hadawa tabata takaimasa

Yana zaune ta iso da coffee din a cup tadoreshi kan dan karamen faranti da teaspoon agefe se kanshi yake

Grany nadaga nesa tana kallonsu amma baiganta ba

Karban cup din yayi ya kurpa

Saurin furzarwa yayi yana fadin wannan coffee ne kome
Anya ma kintaba hada coffee kuwa
Dawannan bagara naje nasaya natiti basha ba mema yasa grany bata hadamun ba se ke

Karasowa grany tayi tana fadin Abidi dagaske baiyi dadi ba amma ai haka kake sonshi shiyasa nayishi haka kuma baka taba cewa baiyi dadi ba se yau

Da mamaki yake kallonta dan Sam baisan tana wurin ba baki yawashe yana fadin haba ai ina dandana shi nasan ke kikayi yayi dadi sosai

Daure fuska tayi tace to meyasa kakema asma'u magana haka badadin ji

Dariya yayi yace grany mufa ma'aurata ne zamu iya tsokanar junanmu yana kara dankon kauna

To shine kuma seka fara mata tunda sassafe

Satan kallon asma'u yayi yana fadin saboda inaso itama ta iya Wanda yafi naki dadi shiyasa nakushe Wanda takawo

Amma kiyi hakuri grany bazan karaba

Murmushi tayi tace ba komai kudai kuhada kanku kuzauna lafiya kar kuji jiya yanda ake yabon Ku wallahi har cikin raina naji dadi
Abidi dan Allah karike yar mutane amana kaji

Tashi yayi yanufi sama yana fadin idan ma dan wannan ne saranki a inuwa grany
Chapter 24 · 0% Book details