← Book details Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 84

Sashe 59

Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

tana sakkowa kasa ta isko gaba daya mutanen gidan azaune apalo ana jajanta abunda yafaru jiya harda grany acikinsu

tana sakkowa suka hau daure fuska suna tabe baki

Ko kallonsu batayi ba tahau kwalama masu aiki kira dagudu suka karaso wurinta suna mika gaisuwa

kallonsu tayi dayan bayan daya sannan tace
Bakomai yasa nakiraku ba sedan insanardaku cewa daga yau aikinku ya kare anan gidan mungode da zaman mutuncin da mukayi da Ku abaya amma ayanzu bama bukatar yan aiki anan gidan

Dafe kirji dattijiwar cikinsu tayi tana langwabar dakai kamar zatayi kuka tace madam meyafaru idan wani laifi mukayi amana hakuri zamu gyara amma wannan aikin dashi muka dogara dan allah ataimaka

Murmushi tayi tana dafa kafadarta tace ba kuyi komai ba baba kawai dai lokaci ne dayakamata ace kuma kun huta

Check taciro acikin Jakarta ta bisu daya bayan daya ta mikamusu tana fadin ga wannan ya isheku Ku kama kowace irin Sana'a kukeso se kuje kuyi allah yabada sa'a sannan idan kuna bukatar wani taimako awurina to zaku iya zuwa kusameni akowane lokaci

washe baki suka hau yi cike dafarin ciki suna mata godiya

Mikewa mutanen gidan sukayi cike da mamki suna kallonta cikin daga murya inna ladidi tace to yanzu da kika kuresu uban wa zaiyi aikin gidan

Karasowa tayi dap da ita tana murmushi cikin sassanyar murya tace nanfa gidana ne ni nakeda ikon sawa ayi ko abari acikinsa ina ganin girmanki dan haka kija bakinki kiyi shiru

Juyowa tayi takalli aunty sadiya sannan tamaida kallonta kan inna ladidi tana fadin bakuyi tsofan dayakama ace kun daina aikin komai ba saboda haka kuzaku kula da tsabatce gidannan ciki da wajansa

Dariya akasa gaba daya palon ana kallonta dan su kallon mai tabin hankali suke mata

Itama murmushi tayi tana kallonsu sannan takarasa wurin aysha da sarah tana kallonsu tace munada tika tikan yan mata kamarku bama bukatar masu girki saboda haka daga yanzu kuzaku rika yin girkin safe da yamma saboda yanda kuke dayawa bazan iya cidaku so uku arana ba

Kallon juna sukayi sannan suka kalleta suna kwashewa da dariya

Banza tayi dasu tana kallon grany tace ke kuma grany.....

Bata karasaba inna ameena takatseta da fadin ita kuma me rashin imanin naki har yakai ki kalli girmanta kice zaki sakata aiki

Murmushi tayi tana kallonta tace to ai bakijira kinji mezan ceba ....

kallon grany tayi taci gaba dafadin dake da inna ameena zaku kula da bangarenku idan taga zata iya setayi gaba daya ke kuma ki huta amma yakamata ace kinadan aiki saboda motsa jiki yanada kyew

Wani dogon tsaki uncle jamilu yaja yana gyara zamansa kan kujera

Juyowa tayi tana kallonsa tace ohh uncle ashe kana nan nibanma ganka ba ai se yanzu

Kallon bashir tayi sannan tamaida kallonta kan jamilu tace uncle kaida bashir kuna wasa da aikinku sosai yanzu karfe Tara amma banga kunada niyyar zuwa office ba

Kallon agogon hannunta tayi sannan takallesu tace yanzu zan wuce office idan har narigaku zuwa to wallahi kunji narantse zan sallameku a aiki

Zaro ido sukayi suna kallonta amma basuga alaman wasa a tattare da ita ba

Juyawa tayi zata fita sukayi saurin mikewa atare suka wuceta har zasu fita tace yawwa bashir zonan dawowa yayi ya tsaya agabanta yakosa tafadi abunda zata fada ya taxi dan uncle jamilu tuni yafita

Makullin motarsa takarba tana fadin a wuri daya kuke aiki banga dalilin dazaisa Ku dauki motoci biyu kufita dasuba

Zaiyi magana tadaure fuska tana fadin nakune ?

Girgiza kai yayi yana fadin a'a nakine

baijira mezata ceba yafita aguje ya isko uncle jamilu har zai tada mota yabude gidan gaba yashiga

Juyowa yayi yana kallonsa fuska ahade cikin kakkausar murya yace kai miye haka

janyo sit belt yayi yadaura yana fadin kai dai uncle muje kawai zamma bayani ahanya

tsaki yayi yatada motar suka fita aguje kamar masu shirin barin garin

wayar Asma'u ce tayi ringing tana dagawa tace kazo ....to kashigo kawai

Dariya aysha tayi suka tafa da sarah tana fadin yau ni ke kallon film ganin idona

Dariya sarah tayi tace jifa wai mune zamuyi aiki base taganmu bama bare mu mata girki

Murmushin mugunta asma'u tayi tana kallon kofa tace gali shigo mana

😳😳😳😳😳

zaro ido sukayi atare suna kallon Wanda yashigo palon cikin shiga ta rashin mutunci kana ganinsa kaga dan kwaya ga idonnan yakade yayi ja fuska ahade ba alamar far'a ko wasa atare dashi

Cike da isa ya karaso palon kanshi Asama yana bin ko ina da kallo

Murmushi asma'u tayi tana kallon su sarah tace wannan shine zai rika kula da aikinku idan bakuyiba dan allah to zakuyi dan wuya

juyowa tayi tana kallon gali tace gali katabbatar komai yatafi daidai duk wacce tama rashin kunya acikinsu kanada damar hukunta ta wacce taga bazata iya ba kuma zata iya tafiya ba dole

dariyar mugunta yayi yana binsu da kallo yace angama hajiya nayi na banza ma bare inda za'a biyani ai karki damu kije kawai

Murmushi tayi tafita daga palon dagudu gudu tashiga motarta tafigeta aguje tafita daga gidan

ahanya bashir se ihu yakema uncle jamilu kan baya gudu tukin ma ashe bai iya ba

Sunzo daidai traffic light uncle jamilu ya juyo cike da takaici Kai kafa isheni fa dan ubanka wayace kabata makullin motarka idan kaga bazaka iya ba kafitarmun amota inyaso ni innaje inga inta isa takoreni aikin banza kai

Kauda kai bashir yayi yana zunbura baki bai kara magana ba har suka isa

suna fitowa daga motarsu motar asma'u tashigo companyn kusan tasu tayi parking tana fitowa takallesu tana murmushin gefe tace allah yaaa taimakeku

Tagefensu tawuce tana maida glasses dinta tasa kai cikin company

Da kallo bashir yabita har tayi nisa sannan ya jinginu da mota yana sauke ajiyar zuciya yace ohhh thank God

Wani banzan kallo uncle jamilu ya watsamai sannan ya wuce ciki yana Jan tsaki

[20/07, 18:48] Hassan Atk: Da daddare asma'u nadaki kan kujerar dake gefen gadonsu tana aiki a computer

AK yashigo dakin yana satar kallonta ya nufi kan gado ya kwanta

Har yarufa ya hango coffee dinsa dake kan bedside drawer
Kallon asma'u yayi aransa yana fadin grany batada lafiya kenan ita tayi wanann coffee din

tashi zaune yayi yajanyo flax din ya zuba a mug sannan ya gyara zamansa yana Satan kallonta yaga ko dagowa ma batayi barema tagansa

Kurban coffee din yayi ya furzar yana yamutsa fuska yace
Wannan wane kalan coffee ne...... koma waye ya hada bai iyaba .....kuma kar yakara hadamun dan ba kowane kalan kazanta nakesha ba

dagowa tayi takallesa sannan sadda kanta tace kaga idan kana son kanka to karkayi wasa da coffee dinnan

ada sau uku kake sha arana yanzu kuma ni nake saya da kudina dan haka nayi niyyar baka so daya arana idan kazubar da wannan to kaida wani kuma se gobe warahaka now it's up to u

wani malalacin murmushi yayi yace haba ai wannan fada kawai kike dan bakinki yasha iska amma ai kema kinsan baki isa ki hanani shan coffee agidannan ba

Ci gaba da aikinta tayi tana fadin muzuba mugani inace kap makullan ahannuna suke ko..... to sedai kaje kasha awaje amma banawa ba ....ko kasiyo grany tahadamaka .....wannan duk bai dameni ba

Ni yanzu kaina kawai nasani duk abunda zan karu dashi shizanyi kowa kuma yaji da matsalarsa

"To meyasa dazu kika shiga damuwa da kika ga grany akuance

"Saboda nasan kudi zan kashe wurin sayan maganinta shiyasa amma ba wai ainahin rashin lafiyarta bane yadameni ko kai dakaga nadamu akanka ba tausayi kabani ba kawai dai rigakafi namaka dan naga alama kaima kana shirin jamun wani kashin kudinne....shi yasa nabaka ruwan sanyi dan kar jininka ya hau

Shiru yayi yana kallonta dan yanda tayi maganar ko kadan ba alamar wasa atare da ita

bayan kuana biyu......

Grany taji sauki amma har yanzu bata sakamar ma AK fuska kullun idan asma'u tadawo daga boye zataje ta dubata har Sudan yi fira

sosai aysha kesamun kulawa daga bangaren AK dan gaba daya hankalinsa yakoma kanta da abunda ke cikinta
yar dubu dari dinsa tuni aysha tagama cinyeta yadawo ba ko sisi hakan yasa yafara zuwa aiki tare da asma'u akan zata biyashi a kowace rana yayi aiki

Haka ta amince ta daukesa dan tasan saboda aysha yake Neman kudi kuma tanajin dadin aiki dashi sosai saboda yafita experience kuma yana bata shawarwari idan tabukaci hakan

a company kuma komai yana tafiya daidai aiki suke ba wasa asma'u takawo canji sosai a harkokinsu shi kanshi AK tana birgesa yanda yaga tana aikinta cikin natsuwa sodayawa yakan shagala wajan kallonta idan suna meeting kowani abun wani lokacin se antaboshi yake dawowa hayyacinsa

Kullun ahmad yana ba khadeeja labarin abunda yake faruwa harda cikin aysha seda yagayamata tana son zuwa wurin asma'u amma Umma tahanata sedai tayita rokon ahmad akan yakular mata da yayarta

abangaren asma'u kuwa Sam takasa yarda cewa cikin jikin aysha na AK ne dan haka tasamata ido sosai akan duk wani motsi nata

har wannan lokacin su Umma basusan abunda ke faruwa ba Sam asma'u bata zuwa gidan suma basa zuwa sedai kowane lokaci da tunaninsu aranta

uncle jamilu yasake yanata harkokinsa Sam yamanta da zancan kudin dazaibiya yana ganin ai tunda amma yarsa ciki komai ya wuce

ganin take takensa yasa asma'u ta kirasa awaya tana son ganinsa yazo office dinta

zaune yake akan kujera kansa akasa yana faman daure fuska

"Jamilu najika shiru ne inafata dai baka manta ba kuana biyu kawai yarage maka cikin lokacinda nabaka

Saurin dagowa yayi yana kallonta yace kamar ya ni bakiga abunda mijinki ya mun bane .....ko nine bansan ciwon kaina ba

Murmushin gefe tayi tana kallonsa tace wannan tsakaninku ne.... ni bai shafeni ba idan kaga dama kayi karansa ko kayi masa abunda yadace ba ruwana.... nidai kudina kawai nasani

Bakaramin tashin hankali yashiga ba ganin da gaske asma'u keyi tabbas zata yi karansa idan bai biya kudinnan ba shi kuma ko za'akasheshi baida ko kwandala kadararsa kuma koyasaida bazata wuce 1M ba ko kashi uku cikin kudinta basu kaiba
Chapter 59 · 0% Book details