← Book details Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 84

Sashe 30

Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kallon asma'u AK yayi yaga yanda fuskanta yacanza kamar zatayi kuka suna hada ido tasunkuy dakanta kasa tana wasa da yatsunta

Murmushi yayi yace wa yagayamuku hardaku zatayi girkin dani da grany kawai zatama kuma bandamu darashin kwalliyarta ba ina sonta ahaka

Dagowa tayi damamki tana kallonsa yayi saurin kauda kai yacigaba dacin abincinsa

Shuru sukayi bawanda yace kala aysha kwa tuni ta tashi tabar wurin tana jan tsaki

Dariya grany tayi tace gaskiyanka abidi kwalliya bashi kadai ne mace ba girki shine kan gaba
Washegari dasafe asma'u na bangaren grany suna shirye shiryen bikin sarah tana gayamata abubuwan da zasu bukata da gyaran gida da sauransu

Sarah tashigo tana hade fuska tace grany inaso naje shopping amma kowa yaki rakani gashi banaso naje nikadai

Dariya grany tayi tace to ba ga asma'u nan tarakaki ba ...

Murmushin mugunta tayi tace to shikenan

Da mamaki asma'u ke kallonta tasan dole akwai abunda tashirya

Kallon grany tayi tace a'a grany ni bazani ba inada aiki agabana

Grany tace a'a asma'u kuje mana daga nan sekiyo ma sauran mutanen gidan sayayya tunda kinga gobe za'afara bikin nan

Badan taso ba hakanan ta amince suka tafi

Suna isa shop owner din yataresu yana murmushi yace hajiya sarah barka dazuwa

Daure fuska tayi tana amsa gaisuwarsa

Ina kawarki yau bakuzo tare ba kika zo da mai aikinku

kallon asma'u tayi takwashe da dariya

Shima dariyar yayi yace Koda yake naji ance yallabai yayi aure nasan ita ya aura ko

Nuna mishi asma'u tayi tace to ai ga matar sa nan

Dariya yayi yajuya yana fadin aaaa haba kinma rainamun hankali

Daure fuska asma'u tayi tana kallon sarah tace
idan kin gama cimun fuska se muyi abunda ya kawomu

Wucewa sarah tayi tana fadin kije dai kiyi abunda yakawoki ni daban inda zanje

Tsaki tayi tanufi wurin atanfofi tafara zaba

Mutumin dazu ne yakara zuwa wurinta yana fadin malama lafiya kike tattaba mun kaya kibari uwar gidanki tazaba mana

Hararansa tayi tanunasa dayatsa tace

Kaga malam kafita ahanyata kajiko inace dai kudi zanbiya ina ruwanka da abunda zan dauka

Bayan sun gama sayayya akayi lissafi sarah tace ma asma'u tafita da kayan tajirata awaje
Iya nata tadauka tafita tabar na sarah awurin

Murmushin mugunta sarah tayi tana kallon shop owner din tace ina so Karage kashi 50 cikin kudin kayanta

Da mamaki yace haba hajiya kamar ya kashi hamsin yau kece da Neman ragi haka

Damen kudi ta ijiyemai kan table tace kasan Nafi karfin haka ga kufinka kawai kayi abunda nace

Dawkan kudin yayi yana dariya yace angama hajiya nan take yamika mata recite na abunda aka kashe amma yarage kudin kayan da asma'u tasaya atanfan dubu ashirin yasata adubu goma

Bayan sun iso gida sarah tacema asma'u takawo jakanta tashiga da kayan ita setashigo da sauran

Suna shiga ciki ta mika ma kowa nashi sun yaba kyan kayan sunata jin dadi

Sarah tace asma'u banga recite dinba muga jakanki naduba koyana ciki

Daukan jakan tayi taciro recite din tana dubawa

Kallon asma'u tayi cikin daga murya tace wannan wane kalan rainin wayaw ne
Damamaki kowa ke kallonta grany tace meyafaru

Tsaki tayi Tamika ma grany recite din tana fadin tarage kashi hamsin cikin kudin dakika bata tasiyo kaya masu arha

Damamaki kowa ke kallon asma'u har AK dake kwance kan 3siter yana kallo

Nan take aysha ,ladidi da sadiya suka dawo dakayansu wai sunfi karfin kayan dubu goma

Cikin rawar murya asma'u tace grany wallahi karya takemun ban rage komai aciki ba

Karban jakanta sarah tayi taciro bandir din kudi tana fadin su kuma wannan daga ina kika samesu tsiyar talaka kenan daga ansakemaku sekuyi abunda kukaga dama

Kusan asma'u grany tamatso tana fadin asma'u dagaske kin rage kudin danabaki
Shuru tayi tasadda kanta kasa tana boye hawayen fuskarta

Murmushi grany tayi tace se yanzu nayarda nayima abidi zaben daya dace
Da mamaki kowa yadago yana kallonta

Daure fuska tayi tana kallon su sadiya tace kafin kuji kudin kayanku duk kuyabasu kuma kunce sunyi kyew amma da kukaji kudin daga kuka dawo dasu
Yakamata kukoyi tattali adano daga wurin asma'u
Dakuna haka dayanzu kundaina family meeting din da kuke kuna tatsar abidi

Daure fuska sarah tayi dan ita bahaka taso ba

Tashi AK yayi yanufi bangarensa yana waya

Dariya aysha tayi tace shikenan komai ya wuce jibi dai sarah zata auri ahmad karyan mutum takusa karewa

Sarah tace wallahi kwa gobe ma zamu hada party anan gidan mu ba marada kunya

Tsaki asma'u tayi tanufi bangaren grany da sauran kayan da tasiyo

Washegari da safe ...

AK yana bayi asma'u tashigo bata saniba

tana daga labule tagansa atsaye yana balle maballan rigarsa

Atsorace tasaki labulan tana rufe fuskarta

Murmushi yayi yace kinzo yimun wanka kuma miye na tsorata

Bude fuskarta tayi tana fadin malan dan Allah kafita wanka zanyi

Cire rigarsa yayi yace Nima ai wankan zanyi kuma nan wuri nane kije ga shower can kiyi

Allah yakayewta nayi wanka wuri daya dakai kuma bazan fita ba senayi wankan grany tana jirana

Banza yayi da ita yashiga bathtub din da 3quater dinsa yana fadin to kizo muyi wankan tare
Juyawa tayi dasuri zata bar wurin santsi ya kwasheta se cikin ruwan tafada saman AK

Yar kara yasaki yana dafe bayansa yace Hajiya ai se kishigo ahankali ko

Atsorace ta tashi zata fita yakara janyota tafado kansa
Kallon cikin idon junansu sukayi nadan lokaci kana ta tureshi ta tashi da gudu tabar wurin

Kallonta yake yana dariya har tafita

Bayan dan lokaci yafito sanye da kananun kaya yayi kyew sosai
Tana zaune ta rufa da bargo tana atishawa

Dariya yayi yace tashi kishiga nafito

Hararansa tayi bata ce komai se atishawa take jerawa

Ruwan dumi ya mikomata batare dayayi magana ba

Da mamaki tace don't tell me that
u care about me

Kauda yayi yace karma kiyi tunanin haka I am doing it for my self
Banaso kiyi effecting dina

Karban ruwan tayi tasha tana fadin thank u

Bai kulata ba yafita daga dakin

Murmushi tayi tatashi tashiga bayi

Su sarah da aysha anci ado anyi kyew kowa yataru apalo ana party

Grany takalli asma'u tace kin gayyato ummanku kuwa

Girgiza kai tayi tace a'a grany tace bazasu samu daman zuwa ba se Gobe zasu zo camu amma zata turo khadeeja

Dariya grany tayi tace to Allah yakawosu nima yau kanwata zata zo

atsorace AK yace badai ameena ba

Daure fuska grany tayi tace ita ko kanada matsala ne

Dariya asma'u tayi tace meyasa bayaso tazo

Daure fuska yayi yace idan tazo zaki sani

Gida yacika da yan uwa kowa yazo har ahmad da Momy ga fa'iz da nusaiba sunzo

Sedai ahmad Sam baya cikin walwala se waige waige yake kozai ga khadeeja dama saboda ita yazo wurin

Kusa dashi sarah tazo tazauna tana murmushi tace honey ya kazauna kai kadai muje mudan taka mana

Daure fuska yayi yace I am not in the mood

Hannunta takai ta tabashi yayi saurin tashi yabar wurin

AK dake gefe yana kallonsu baiji dadi ba amma ya zaiyi

Lhadeeja ce tashigo gidan da wata mace mai kama da Umma se kuma wani kyekkyewan saurayi tare dasu suna shigo palon kallo yakoma Kansu

Sukuma sebin gidan suke da kallo dagudu asma'u tazo tarungume matar suka gaisa sannan takalli saurayin tana murmushi tace Ali ya kake

Murmushi yayi suka gaisa sannan takaisu wurin grany suka gaisa tagayamata matar kanwar Umma ce sawrayin kuma danta ne sannan tanufi kitchen dan kawomusu wani abu

Hannu Ali yaba AK suka gaisa yana musu fatan alkhairi a aurensu

Ahmad nahango khadeeja ya saki murmushi yana kallonta

Kamar ance ta kalla sukayi ido biyu kauda kai tayi kaman bata gansa ba tana daure fuska

Aysha da Sarah na tsaye daga gefe suna kallonsu tsaki aysha tayi tace ni wallahi nagaji daganin yarinyar nan kuma ni banga abunda AK yake mata ba banda kowane lokaci suna tare

Dafata sarah tayi tace kuantar da hankalinki aysha yanayi ne saboda kar grany ta fuskanci wani Abu amma nafiki tsanar yarinyar nan

Suna cikin magana Sega kanwar grany ta iso cike da farin ciki suka gaisa da kowa tun kafin tazauna tafara tambayar ina amaryar AK

Murmushi grany tayi tace bari akiramaki sarah kiganta

a'a nidai Nafi so naga amaryar AK sarah ai nasanta

Daure fuska sarah tayi tana gaisheta

Sama sama ta amsa gaisuwar tana waigen waigen mutanan wurin

Tunda asma'u tanufo wurin takafeta da ido tana washe baki

Tana zuwa suka gaisa tace gaskiya AK kayi dacen mata zuuuuuki

Dariya akasa gaba daya banda sarah data bar wurin tana jan tsaki

Bayan anyi shagali kowa ya watse aysha ta matsama AK akan seyafita da ita

Hakanan suka shirya suka fita yana driving tana mishi shagwabar yadaina kulata tunda yayi aure kamar yadaina sonta

Daure fuska yayi yace haba aysha ya isa haka mana yanzu bagashi nafito dakeba

Inda bana sonki kema kinsan ko kallo baki isheni ba

Ganin ya hasala yasa tafara bashi hakuri banza yayi da ita yana bin wakar da yake sawrare amotar

Sunkuyowa tayi gefen fuskarsa wai zata mai kiss

Birki yafara kokarin takawa yana fadin aysha miye haka kimatsa bana ganin gabana can't u see I am driving bai karasa ba yaji ya kade wani mutum saurin taka birki yayi yana salati

Ganin mutane sun nufi mutumin yasa yayi kokarin Barin motar amma aysha tarikosa tana kuka tace dan Allah sutafi kar agansu mutuncin shi zai zube idan aka ganshi da ita cikin Daren nan

Bashiri yataka motar suka tafi amma yanaji abunda yayi baidace ba

Suna isa gida yawuce bangarensa yana tunanin wane hali mutuminnan yake ciki

Baiga asma'u apalo ba kuma bata daki kayan baccinsa yasa yauna bakin gado yana danna laptop

Can anjima tashigo rike da mug ahannunta kan bedside drawer tadora tana fadin nagayamaka idan zaka fita da aysha kasan lokacinda yadace kufita yanzu da grany taga lokacinda kuka shigo mezaka cemata

Banza yayi da ita yana duba laptop dinsa da damuwa afuskansa

Kusa dashi ta tsaya tana fadin meyake damunka

Dagowa yayi yakalleta yace inada damuwan da tawuce kine

Murmushi tayi taleka laptop din da mamaki tace

Hukuncin tukin ganganci kuma kayi accident ne

Banyiba ....yafada atakaice

To meyasa kake Neman hukuncinsa ...
Chapter 30 · 0% Book details